< Zechariah 4 >

1 And the angel who had been speaking with me returned, and he awakened me, like a man who is awakened from his sleep.
Sai mala’ikan da ya yi magana da ni ya komo ya farkar da ni, kamar yadda ake farkar da mutum daga barcinsa.
2 And he said to me, “What do you see?” And I said, “I looked, and behold, a candlestick entirely in gold, and its lamp was at its top, and seven oil lamps of it were upon it, and there were seven funnels for the oil lamps that were at its top.
Ya tambaye ni ya ce, “Me ka gani?” Na amsa, na ce, “Na ga wurin ajiye fitilan zinariya da kwano a kai, da kuma fitilu bakwai a kansa, da butocin kai wa fitilu mai guda bakwai.
3 And there were two olive trees upon it: one to the right of the lamp, and one to its left.”
Akwai kuma itatuwan zaitun guda biyu a gefensa, ɗaya a gefen dama na kwanon ɗaya kuma a gefen hagunsa.”
4 And I answered and spoke to the angel who was speaking with me, saying, “What are these, my lord?”
Na tambayi mala’ikan da ya yi magana da ni na ce, “Mene ne waɗannan, ranka yă daɗe?”
5 And the angel who was speaking with me answered, and he said to me, “Do you not know what these are?” And I said, “No, my lord.”
Sai ya amsa ya ce, “Ba ka san mene ne waɗannan ba?” Na amsa, na ce, “A’a, ranka yă daɗe.”
6 And he answered and spoke to me, saying: This is the word of the Lord to Zerubbabel, saying: Not by an army, nor by might, but in my spirit, says the Lord of hosts.
Sai ya ce mini, “Wannan ce maganar Ubangiji ga Zerubbabel. ‘Ba ta wurin ƙarfi ba, ko ta wurin iko, sai dai ta wurin Ruhuna,’ in ji Ubangiji Maɗaukaki.
7 What are you, great mountain, in the sight of Zerubbabel? You are among the plains. And he will lead out the primary stone, and he will give equal grace to its grace.
“Kai mene ne, ya babban dutse? A gaban Zerubbabel za a rushe ka ka zama fili. Sa’an nan Zerubbabel yă kawo dutsen da ya fi kyau, a kuma yi ta sowa ana cewa, ‘Allah yă yi masa albarka! Allah yă yi masa albarka!’”
8 And the word of the Lord came to me, saying:
Sai maganar Ubangiji ta zo mini,
9 The hand of Zerubbabel has founded this house, and his hands will complete it. And you will know that the Lord of hosts has sent me to you.
“Hannuwan Zerubbabel sun kafa harsashin haikalin nan; hannuwansa ne kuma za su gama ginin. Sa’an nan ne za ka san cewa Ubangiji Maɗaukaki ne ya aiko ni zuwa wurinka.
10 For who has despised the little days? And they will rejoice and will see the silver and lead stone in the hand of Zerubbabel. These are the seven eyes of the Lord, which roam quickly through all the earth.
“Wa ya rena ranar ƙananan abubuwa? Mutane za su yi murna sa’ad da suka ga igiyar gwaji a hannun Zerubbabel. “Waɗannan guda bakwai ɗin su ne idanun Ubangiji, masu jujjuyawa cikin dukan duniya.”
11 And I responded and said to him, “What are these two olive trees to the right of the candlestick, and to its left?”
Sai na tambaye shi na ce, “Mene ne waɗannan itatuwan zaitun guda biyu tsaye a hagu da kuma daman wurin ajiye fitilan fitilu?”
12 And I responded a second time and said to him, “What are the two olive branches, which are next to the two golden ridges, in which are the pouring spouts of gold?”
Na sāke tambaye shi na ce, “Mene ne waɗannan rassa biyun nan na zaitun a gefen bututu biyu na zinariya da suke zuba man zinariya?”
13 And he spoke to me, saying, “Do you not know what these are?” And I said, “No, my lord.”
Ya amsa ya ce, “Ba ka san mene ne waɗannan ba?” Na ce, “A’a, ranka yă daɗe.”
14 And he said, “These are the two sons of oil, who attend before the Sovereign of all the earth.”
Sai ya ce, “Waɗannan su ne biyun da aka shafe don su yi wa Ubangiji dukan duniya hidima.”

< Zechariah 4 >