< Romans 7 >
1 Or do you not know, brothers, (now I am speaking to those who know the law) that the law has dominion over a man only so long as he lives?
'Yan'uwa, ko baku sani ba (domin ina magana da wadanda suka san shari'a), cewar shari'a na mulkin mutum muddin ransa?
2 For example, a woman who is subject to a husband is obligated by the law while her husband lives. But when her husband has died, she is released from the law of her husband.
Domin ta wurin shari'a matar aure a daure take muddin mijinta nada rai, amma idan mijinta ya mutu, ta kubuta daga shari'ar aure.
3 Therefore, while her husband lives, if she has been with another man, she should be called an adulteress. But when her husband has died, she is freed from the law of her husband, such that, if she has been with another man, she is not an adulteress.
To don haka idan, mijinta na da rai, sai ta tafi ta zauna da wani mutumin, za'a kirata mazinaciya. Amma idan mijin ya mutu, ''yantarciya ce daga shari'a, domin kada ta kasance mazinaciya idan ta auri wani mutum.
4 And so, my brothers, you also have become dead to the law, through the body of Christ, so that you may be another one who has risen from the dead, in order that we may bear fruit for God.
Domin wannan, 'yan'uwana, ku ma an sa kun mutu ga shari'a ta wurin jikin Almasihu, saboda a hada ku aure da wani, wato, ga wanda aka tashe shi daga matattu, domin mu haifawa Allah 'ya'ya.
5 For when we were in the flesh, the passions of sins, which were under the law, operated within our bodies, so as to bear fruit unto death.
Domin sa'adda muke cikin jiki, ana motsa dabi'armu ta zunubi dake cikin jikunan mu ta wurin shari'a domin mu haifi 'ya'ya zuwa mutuwa.
6 But now we have been released from the law of death, by which we were being held, so that now we may serve with a renewed spirit, and not in the old way, by the letter.
Amma yanzu an kubutar damu daga shari'a, mun mutu daga abin da ya daure mu, domin mu yi bauta cikin sabuntuwar Ruhu, ba cikin tsohon rubutun shari'a ba.
7 What should we say next? Is the law sin? Let it not be so! But I do not know sin, except through the law. For example, I would not have known about coveting, unless the law said: “You shall not covet.”
To me zamu ce kenan? ita shari'ar kanta zunubi ce? ba zai taba faruwa ba. Duk da haka. Idan ba ta wurin shari'a ba, ba zan taba sanin zunubi ba, in ba ta wurin shari'a ba. Ba zan taba kyashin abin wani ba, har sai da shari'a tace, “Kada kayi kyashi.”
8 But sin, receiving an opportunity through the commandment, wrought in me all manner of coveting. For apart from the law, sin was dead.
Amma zunubi, sai ya dauki zarafi ta wurin dokar, ya jawo dukkan sha'awa dake cikina. Domin in da babu shari'a, zunubi matacce ne.
9 Now I lived for some time apart from the law. But when the commandment had arrived, sin was revived,
Ada na rayu sau daya ba tare da shari'a ba, amma da dokar ta zo, sai zunubi ya farfado, ni kuma na mutu.
10 and I died. And the commandment, which was unto life, was itself found to be unto death for me.
Dokar wadda ta kamata ta kawo rai, sai na same ta matacciya.
11 For sin, receiving an opportunity through the commandment, seduced me, and, through the law, sin killed me.
Domin zunubin, ya dauki zarafi ta wurin dokar, ya rude ni, kuma ta wurin dokar ya kashe ni.
12 And so, the law itself is indeed holy, and the commandment is holy and just and good.
Domin haka, shari'ar na da tsarki, dokar na da tsarki, adalci da kuma kyau.
13 Then was what is good made into death for me? Let it not be so! But rather sin, in order that it might be known as sin by what is good, wrought death in me; so that sin, through the commandment, might become sinful beyond measure.
To abu mai kyau ya zamar mani mutuwa kenan? ba zai taba zama haka ba. Amma zunubi, domin ya nuna shi zunubi ne ta wurin abin da ke mai kyau, sai ya kawo mutuwa a cikina. Wannan ya kasance haka ne domin ta wurin dokar, zunubi ya zama cikakken zunubi.
14 For we know that the law is spiritual. But I am carnal, having been sold under sin.
Domin mun san shari'a mai Ruhaniya ce, amma ni ina cikin jiki. An sai da ni karkashin bautar zunubi.
15 For I do things that I do not understand. For I do not do the good that I want to do. But the evil that I hate is what I do.
Domin ni ma ban fahimci abin da nake aikatawa ba. Domin abin da nake so in aikata, ba shi nake aikatawa ba, kuma abin da bana so, shi nake aikatawa.
16 So, when I do what I do not want to do, I am in agreement with the law, that the law is good.
Amma idan na aikata abin da bana so, na amince da shari'a kenan, cewar shari'a nada kyau.
17 But I am then acting not according to the law, but according to the sin which lives within me.
Amma yanzu ba ni ke aikata abin ba, amma zunubi da ke zaune a cikina.
18 For I know that what is good does not live within me, that is, within my flesh. For the willingness to do good lies close to me, but the carrying out of that good, I cannot reach.
Domin na san a cikina, wato cikin jikina, babu wani abu mai kyau. Domin marmarin aikata abu mai kyau na tare da ni, amma ba ni iya aikatawa.
19 For I do not do the good that I want to do. But instead, I do the evil that I do not want to do.
Domin abu mai kyau da na ke so in aikata bana iyawa, amma muguntar da ba na so ita na ke aikatawa.
20 Now if I do what I am not willing to do, it is no longer I who am doing it, but the sin which lives within me.
To idan na yi abin da ba ni so in aikata, wato kenan ba ni bane ke aikatawa, amma zunubin da ke zaune a cikina.
21 And so, I discover the law, by wanting to do good within myself, though evil lies close beside me.
Don haka, sai na iske, akwai ka'ida a cikina dake son aikata abu mai kyau, amma kuma ainihin mugunta na tare dani.
22 For I am delighted with the law of God, according to the inner man.
Domin a cikina ina murna da shari'ar Allah.
23 But I perceive another law within my body, fighting against the law of my mind, and captivating me with the law of sin which is in my body.
Amma ina ganin wasu ka'idoji daban a gabobin jikina, su na yaki da wannan sabuwar ka'idar da ke cikin tunanina, suna kuma sanya ni bauta ta wurin ka'idar zunubi wadda ke cikin gabobin jikina.
24 Unhappy man that I am, who will free me from this body of death?
Ni wahalallen mutum ne! wa zai kubutar dani daga wannan jiki na mutuwa?
25 The grace of God, by Jesus Christ our Lord! Therefore, I serve the law of God with my own mind; but with the flesh, the law of sin.
Amma godiya ga Allah ta wurin Yesu Almasihu Ubangijinmu! Domin haka ni kaina a wannan hannu bisa ga tunani na ina bautawa shari'ar Allah. Duk da haka, ta wani gefen ina bautawa ka'idar zunubi da ke tare da jikina.