< Romans 11 >

1 Therefore, I say: Has God driven away his people? Let it not be so! For I, too, am an Israelite of the offspring of Abraham, from the tribe of Benjamin.
Sai na ce, Allah ya ki mutanensa ne? Ba zai taba yiwuwa ba. Domin ni ma ba-Isra'ile ne, na zuriyar Ibrahim, a kabilar Bilyaminu.
2 God has not driven away his people, whom he foreknew. And do you not know what Scripture says in Elijah, how he calls upon God against Israel?
Allah bai ki mutanen sa da ya ke da rigyasaninsu ba. Ko kun san abin da nassi ya ce game da Iliya, yadda ya kai karar Isra'ila a gaban Allah?
3 “Lord, they have slain your Prophets. They have overturned your altars. And I alone remain, and they are seeking my life.”
Ya ce, ''Ubangiji, sun kashe annabawanka, sun rushe alfarwanka kuma, Ni kadai ne na rage, ga shi suna neman su kashe ni.''
4 But what is the Divine response to him? “I have retained for myself seven thousand men, who have not bent their knees before Baal.”
Amma wacce amsa ce Allah ya ba shi? Ya ce, ''Ina da mutane dubu bakwai da na kebe don kaina, da ba su taba rusuna wa Ba'al ba.''
5 Therefore, in the same way, again in this time, there is a remnant that has been saved in accord with the choice of grace.
Ban da haka ma, ban da haka ma a wannan lokacin akwai sauran zabe na alheri.
6 And if it is by grace, then it is not now by works; otherwise grace is no longer free.
Amma tun da ta wurin alheri ne, ba ga ayyuka ba. In ba haka ba, alheri ba zai zama alheri ba kenan.
7 What is next? What Israel was seeking, he has not obtained. But the elect have obtained it. And truly, these others have been blinded,
Sai kuma me? Abin da Isra'ila ke nema, ba su samu ba, amma zababbun sun same shi, saura kuma sun taurare.
8 just as it was written: “God has given them a spirit of reluctance: eyes that do not perceive, and ears that do not hear, even until this very day.”
Kamar yadda yake a rubuce, ''Allah ya ba su ruhun rashin fahimta, ga idanu amma ba za su gani ba, ga kunnuwa amma ba za su ji ba, har zuwa wannan rana.''
9 And David says: “Let their table become like a snare, and a deception, and a scandal, and a retribution for them.
Dauda kuma ya ce, ''bari teburinsu ya zama taru, da tarko, ya zama dutsen tuntube da abin ramako a gare su.
10 Let their eyes be obscured, so that they may not see, and so that they may bow down their backs always.”
Bari idanunsu ya duhunta domin kada su gani; bayansu kuma a duke kullum.''
11 Therefore, I say: Have they stumbled in such a way that they should fall? Let it not be so! Instead, by their offense, salvation is with the Gentiles, so that they may be a rival to them.
Na ce, ''sun yi tuntube domin su fadi ne?'' Kada abu kamar haka ya faru. A maimakon haka, juyawa baya da suka yi ya sa, ceto ya zo ga Al'ummai, domin ya sa su kishi.
12 Now if their offense is the riches of the world, and if their diminution is the riches of the Gentiles, how much more is their fullness?
Idan yanzu juyawa baya da sun yi ya zama arziki ga duniya, rashin su kuma arziki ga Al'ummai, yaya kwatancin girmansa zai kasance in sun zo ga kammala?
13 For I say to you Gentiles: Certainly, as long as I am an Apostle to the Gentiles, I will honor my ministry,
Yanzu ina magana da ku ku da ke Al'ummai. Tunda yake ni ne manzo ga Al'ummai, ina kuma fahariya cikin hidimata.
14 in such a way that I might provoke to rivalry those who are my own flesh, and so that I may save some of them.
Yana yiwuwa in sa ''yan'uwa na kishi, domin mu ceci wadansu su.
15 For if their loss is for the reconciliation of the world, what could their return be for, except life out of death?
Idan kinsu ya kawo sulhuntawa ga duniya, Karbarsu kuma zata zama yaya? Zata zama rai ne daga mutuwa.
16 For if the first-fruit has been sanctified, so also has the whole. And if the root is holy, so also are the branches.
'ya'yan farko sunan haka ma kakkabensu yake, Idan saiwar itace na nan, haka ma rassan za su zama.
17 And if some of the branches are broken, and if you, being a wild olive branch, are grafted on to them, and you become a partaker of the root and of the fatness of the olive tree,
Amma idan an karye wasu daga cikin rassan, idan ku rassan zaitun na ainihi ne, da aka samu daga cinkinsu, kuma idan kuna da gado tare da su, acikin saiwar itacen zaitun din.
18 do not glorify yourself above the branches. For though you glory, you do not support the root, but the root supports you.
Kada ku yi fahariya a kan rassan. Amma idan kuka yi fahariya to ba ku bane masu karfafa saiwar amma saiwar ce ke karfafa ku.
19 Therefore, you would say: The branches were broken off, so that I might be grafted on.
Kana iya cewa, ''An karye rassan domin a same ni a ciki.''
20 Well enough. They were broken off because of unbelief. But you stand on faith. So do not choose to savor what is exalted, but instead be afraid.
Wannan gaskiya ne! Saboda rashin bangaskiyarsu ne ya sa aka karye su daga rassan, amma ku tsaya da karfi acikin bangaskiyarku. Kada ku dauki kanku fiye da yadda ya kamata, amma ku ji tsoro.
21 For if God has not spared the natural branches, perhaps also he might not spare you.
Domin idan Allah bai bar ainihin rassan ba, to ba zai bar ku ba.
22 So then, notice the goodness and the severity of God. Certainly, toward those who have fallen, there is severity; but toward you, there is the goodness of God, if you remain in goodness. Otherwise, you also will be cut off.
Ku duba yadda irin ayyuka masu tsananni na Allah. Ta daya hannun kuma, tsanannin kan zoa kan Yahudawa wadanda suka fadi. Har 'ila yau jinkai Allah ya zo maku, idan kun cigaba cikin alherinsa baza a sare ku ba. Amma in kun ki za a sare ku.
23 Moreover, if they do not remain in unbelief, they will be grafted on. For God is able to graft them on again.
Hakanan, idan ba su ci gaba cikin rashin bangaskiyarsu ba, za a maida su cikin itacen. Domin Allah zai iya sake maida su.
24 So if you have been cut off from the wild olive tree, which is natural to you, and, contrary to nature, you are grafted on to the good olive tree, how much more shall those who are the natural branches be grafted on to their own olive tree?
Idan an yanke ka daga itacen zaitun da ke na jeji, har ya yiwu an hada ka cikin itacen zaitun na ainihi, yaya kuma wadannan Yahudawa wadanda sune ainihin rassan, da za'a maido cikin zaitun da ke na ainihi?
25 For I do not want you to be ignorant, brothers, of this mystery (lest you seem wise only to yourselves) that a certain blindness has occurred in Israel, until the fullness of the Gentiles has arrived.
Yan'uwa, ba na so ku kasance cikin duhu a game da wannan asirin, domin kada ku zama da hikima cikin tunaninku. Wannan asirin shine cewa wannan taurarewa ta faru a Isra'ila, har sai da Al'ummai suka shigo ciki.
26 And in this way, all of Israel may be saved, just as it was written: “From Zion shall arrive he who delivers, and he shall turn impiety away from Jacob.
Ta haka dukan Isra'ila za su tsira, kamar yadda yake a rubuce: ''Daga cikin Sihiyona mai Kubutarwa zai fito; Zai kawar da kazanta daga cikin Yakubu.
27 And this will be my covenant for them, when I will take away their sins.”
Wannan zai zama alkawarina da su, sa'adda na kawar da zunubansu.''
28 Certainly, according to the Gospel, they are enemies for your sake. But according to the election, they are most beloved for the sake of the fathers.
A wani bangaren kuma game da bishara, su makiya ne amamadinku, ta wani fannin kuma bisa ga zabin Allah su kaunattatu ne saboda ubanni.
29 For the gifts and the call of God are without regret.
Domin baye-baye da kiran Allah basa canzawa.
30 And just as you also, in times past, did not believe in God, but now you have obtained mercy because of their unbelief,
Domin ku ma da ba ku yin biyayya ga Allah, amma yanzu kun sami jinkai saboda rashin biyayyarsu.
31 so also have these now not believed, for your mercy, so that they might obtain mercy also.
Ta wannan hanyar dai, wadannan Yahudawan sun zama marasa biyayya. Sakamakon haka shine ta wurin jinkan da aka nuna maku, suma su samu jikai yanzu.
32 For God has enclosed everyone in unbelief, so that he may have mercy on everyone. (eleēsē g1653)
Domin Allah ya rufe kowa ga rashin biyayya, domin ya nuna jinkai ga kowa. (eleēsē g1653)
33 Oh, the depths of the richness of the wisdom and knowledge of God! How incomprehensible are his judgments, and how unsearchable are his ways!
Ina misalin zurfin wadata da kuma hikima da sani na Allah! Hukunce-hukuncensa sun fi gaban a bincika, hanyoyinsa kuma sun fi gaban ganewa!
34 For who has known the mind of the Lord? Or who has been his counselor?
Don wanene ya san tunanin Ubangiji? Wanene kuma ya zama mai bashi shawara?
35 Or who first gave to him, so that repayment would be owed?
Ko kuma, wanene ya fara ba Allah wani abu, domin a biya shi?''
36 For from him, and through him, and in him are all things. To him is glory, for all eternity. Amen. (aiōn g165)
Daga wurinsa ne, ta wurinsa ne kuma, a gare shi ne kuma dukan abu suka fito. A gare shi daukaka ta tabbata har abada. Amin. (aiōn g165)

< Romans 11 >