< Revelation 9 >
1 And the fifth Angel sounded the trumpet. And I saw upon the earth, a star that had fallen from heaven, and the key to the well of the abyss was given to him. (Abyssos )
Mala’ika na biyar ya busa ƙahonsa, sai na ga tauraron da ya fāɗo duniya daga sararin sama. Aka ba wa tauraron mabuɗin ramin Abis. (Abyssos )
2 And he opened the well of the abyss. And the smoke of the well ascended, like the smoke of a great furnace. And the sun and the air were obscured by the smoke of the well. (Abyssos )
Da ya buɗe Abis ɗin, sai hayaƙi ya taso daga cikin kamar hayaƙin matoya mai girma. Hayaƙin nan daga Abis ya duhunta rana da sararin sama. (Abyssos )
3 And locusts went forth from the smoke of the well into the earth. And power was given to them, like the power that the scorpions of the earth have.
Daga cikin hayaƙin kuwa fāri suka fito zuwa cikin duniya aka kuma ba su iko irin na kunaman duniya.
4 And it was commanded of them that they must not harm the plants of the earth, nor anything green, nor any tree, but only those men who do not have the Seal of God upon their foreheads.
Aka faɗa musu kada su yi wa ciyawa na duniya lahani ko wani tsiro ko itace, sai dai su yi wa mutanen da ba su da hatimin Allah a goshinsu kaɗai lahani.
5 And it was given to them that they would not kill them, but that they would torture them for five months. And their torture was like the torture of a scorpion, when he strikes a man.
Ba a ba su iko su kashe su ba, sai dai su ba su azaba na watanni biyar. Azabar da suka sha kuwa ya yi kamar ta harbin kunama sa’ad da ta harbi mutum.
6 And in those days, men will seek death and they will not find it. And they will desire to die, and death will flee from them.
Cikin waɗannan kwanakin mutane za su nemi mutuwa, amma ba za su samu ba; za su yi marmarin mutuwa, amma mutuwa za tă ɓace musu.
7 And the likenesses of the locusts resembled horses prepared for battle. And upon their heads were something like crowns similar to gold. And their faces were like the faces of men.
Kamannin fārin nan kuwa yana kama da dawakan da aka shirya don yaƙi. A kawunansu kuwa da wani abu da ya yi kamar rawanin zinariya, fuskokinsu kuma sun yi kamar fuskokin mutane.
8 And they had hair like the hair of women. And their teeth were like the teeth of lions.
Gashin kansu ya yi kamar gashin kan mata, haƙoransu kuma sun yi kamar haƙoran zakoki.
9 And they had breastplates like iron breastplates. And the noise of their wings was like the noise of many running horses, rushing to battle.
Suna da sulkuna kamar sulkunan ƙarfe, ƙarar fikafikansu kuma ta yi kamar motsin dawakai da kekunan yaƙi masu yawa da suke rugawa zuwa yaƙi.
10 And they had tails similar to scorpions. And there were stingers in their tails, and these had the power to harm men for five months.
Suna da wutsiyoyi da ƙari kamar kunamai, kuma a wutsiyoyinsu suna da iko su ba wa mutane azaba na wata biyar.
11 And they had over them a king, the Angel of the abyss, whose name in Hebrew is Doom; in Greek, Destroyer; in Latin, Exterminator. (Abyssos )
Suna da sarkin da yake mulki a bisansu wanda yake mala’ikan Abis, wanda sunansa a harshen Yahudawa shi ne Abaddon, da harshen Hellenawa kuwa shi ne, Afolliyon. (Abyssos )
12 One woe has gone out, but behold, there are still two woes approaching afterward.
Bala’i na fari ya wuce, sauran bala’i biyu suna nan zuwa.
13 And the sixth Angel sounded the trumpet. And I heard a lone voice from the four horns of the golden altar, which is before the eyes of God,
Mala’ika na shida ya busa ƙahonsa, sai na ji murya tana fitowa daga ƙahonin bagaden zinariya da suke a gaban Allah.
14 saying to the sixth Angel who had the trumpet: “Release the four Angels who were bound at the great river Euphrates.”
Ta ce wa mala’ika na shida da yake da ƙahon, “Ka saki mala’iku huɗun nan da suke a daure a babban kogin Yuferites.”
15 And the four Angels were released, who had been prepared for that hour, and day, and month, and year, in order to kill one third part of men.
Mala’iku huɗun nan kuwa da aka shirya musamman don wannan sa’a da kuma don wannan rana da wata da kuma shekara aka sake su domin su kashe kashi ɗaya bisa uku na’yan Adam.
16 And the number of the army of horsemen was two hundred million. For I heard their number.
Yawan rundunan masu hawan dawakan nan mutum miliyon ɗari biyu ne. Na ji adadinsu.
17 And I also saw the horses in the vision. And those who were sitting upon them had breastplates of fire and hyacinth and sulphur. And the heads of the horses were like the heads of lions. And from their mouths proceeded fire and smoke and sulphur.
Dawakai da masu hawansu da na gani cikin wahayina sun yi kamar. Sulkunansu ja wur ne, baƙin shuɗi, da kuma rawaya kamar farar wuta. Kawunan dawakan sun yi kamar kawunan zakoki, daga bakunansu kuwa wuta, hayaƙi, da farar wuta suna fitowa.
18 And one third part of men were slain by these three afflictions: by the fire and by the smoke and by the sulphur, which proceeded from their mouths.
Aka kashe kashi ɗaya bisa uku na’yan Adam da annobai uku na wuta, hayaƙi da farar wuta da suka fito daga bakunansu.
19 For the power of these horses is in their mouths and in their tails. For their tails resemble serpents, having heads; and it is with these that they cause harm.
Ƙarfin dawakan nan kuwa yana a bakunansu da wutsiyoyinsu; gama wutsiyoyinsu suna kama da macizai masu kawuna, da wutsiyoyin ne kuma suke yi wa mutane rauni.
20 And the rest of men, who were not slain by these afflictions, did not repent from the works of their hands, so that they would not worship demons, or idols of gold and silver and brass and stone and wood, which can neither see, nor hear, nor walk.
Sauran’yan Adam da ba a kashe ta wajen waɗannan annobai ba kuwa har wa yau ba su tuba daga aikin hannuwansu ba; ba su daina bauta wa aljanu, da gumakan zinariya, azurfa, tagulla, dutse da na itace, gumakan da ba sa iya gani ko ji ko tafiya ba.
21 And they did not repent from their murders, nor from their drugs, nor from their fornication, nor from their thefts.
Ba su kuma tuba daga kisankansu, sihirinsu, fasikancinsu ko kuma daga sace-sacensu ba.