< Revelation 5 >
1 And in the right hand of the One sitting upon the throne, I saw a book, written inside and out, sealed with seven seals.
Sa'annan na ga a cikin hannun daman wanda ke zaune a kan kursiyin, na ga littafi wanda ke da rubutu ciki da waje, an kuma hatimce shi da hatimai bakwai.
2 And I saw a strong Angel, proclaiming with a great voice, “Who is worthy to open the book and to break its seals?”
Na kuma ga wani kakkarfan mala'ika na shela da murya mai karfi, “Wa ya isa ya bude littafin ya kuma bambare hatimin?”
3 And no one was able, neither in heaven, nor on earth, nor under the earth, to open the book, nor to gaze upon it.
Ba wani a sama ko a kasa ko karkashin kasa da ya iya ya bude littafin ko ya karanta abin da ke cikinsa.
4 And I wept greatly because no one was found worthy to open the book, nor to see it.
Na yi kuka mai zafi saboda ba wani da ya cancanta da zai bude littafin ko ya karanta abin da ke cikinsa.
5 And one of the elders said to me: “Weep not. Behold, the lion from the tribe of Judah, the root of David, has prevailed to open the book and to break its seven seals.”
Amma daya daga cikin dattawan nan ya ce mani, “Kada ka yi kuka. Duba! Zaki na kabilar Yahuza, Tushen Dauda, ya yi nasara. Ya cancanci bude littafin da kuma hatimansa bakwai.”
6 And I saw, and behold, in the midst of the throne and the four living creatures, and in the midst of the elders, a Lamb was standing, as if it were slain, having seven horns and seven eyes, which are the seven spirits of God, sent forth to all the earth.
Na ga Dan Rago yana tsaye tsakanin kursiyin da rayayyun halittun nan guda hudu a cikin dattawa. Yana kama da wanda aka kashe. Yana da kafonni bakwai da idanuwa bakwai; wadannan sune ruhohin Allah bakwai da aka aiko zuwa dukan duniya.
7 And he approached and received the book from the right hand of the One sitting upon the throne.
Ya tafi ya karbi littafin daga hannun daman wanda ke zaune bisa kursiyin.
8 And when he had opened the book, the four living creatures and the twenty-four elders fell down before the Lamb, each having stringed instruments, as well as golden bowls full of fragrances, which are the prayers of the saints.
Lokacin da Dan Ragon ya dauki littafin, rayayyun halittun nan hudu da dattawan nan ashirin da hudu suka fadi har kasa a gaban Dan ragon. Kowannen su na dauke da molo da tasar zinariya cike da kayan kamshi, wadanda kuwa sune addu'o'in masu ba da gaskiya.
9 And they were singing a new canticle, saying: “O Lord, you are worthy to receive the book and to open its seals, because you were slain and have redeemed us for God, by your blood, from every tribe and language and people and nation.
Suka raira sabuwar waka: “Ka cancanta ka dauki littafinka kuma bude hatimansa. Domin an yanka ka, da jininka ka saya wa Allah mutane daga kowacce kabila, harshe, jama'a da al'umma.
10 And you have made us into a kingdom and into priests for our God, and we shall reign over the earth.”
Ka maishe su mulki da firistoci su bauta wa Allanmu, kuma za su yi mulki a duniya.”
11 And I saw, and I heard the voice of many Angels surrounding the throne and the living creatures and the elders, (and their number was thousands of thousands)
Da na duba sai na ji karar mala'iku masu yawa kewaye da kursiyin da rayayyun halitu da kuma dattawa. Jimillarsu ya kai dubbai goma, sau dubbai goma, da dubun dubbai.
12 saying with a great voice: “The Lamb who was slain is worthy to receive power, and divinity, and wisdom, and strength, and honor, and glory, and blessing.”
Suka tada murya da karfi suka ce, “Macancanci ne Dan Ragon da aka yanka ya karbi iko, wadata, hikima, karfi, girma, daukaka da yabo.”
13 And every creature that is in heaven, and on earth, and under the earth, and all that is within the sea: I heard them all saying: “To the One sitting upon the throne and to the Lamb be blessing, and honor, and glory, and authority, forever and ever.” (aiōn )
Na ji kowanne halittaccen abu da ke cikin sama da kasa da karkashin kasa da cikin teku - dukan abubuwan da ke cikinsu - na cewa, “Ga shi wanda ke zaune a kan kursiyin da kuma Dan Ragon, yabo, girma, daraja, da kuma ikon yin mulki, har abada abadin. (aiōn )
14 And the four living creatures were saying, “Amen.” And the twenty-four elders fell down on their faces, and they adored the One who lives forever and ever.
Sai rayayyun halittun nan hudu suka ce, “Amin!” dattawan nan kuma suka fadi da fuskokinsu suka yi sujada.