< Psalms 96 >
1 A Canticle of David himself, when the house was built after the captivity. Sing to the Lord a new song. Sing to the Lord, all the earth.
Ku rera sabuwar waƙa ga Ubangiji; ku rera ga Ubangiji, ku duniya duka.
2 Sing to the Lord and bless his name. Announce his salvation from day to day.
Ku rera ga Ubangiji, ku yabe sunansa; ku yi shelar cetonsa kowace rana.
3 Announce his glory among the Gentiles, his miracles among all peoples.
Ku furta ɗaukakarsa a cikin al’ummai, manyan ayyukansa a cikin dukan mutane.
4 For the Lord is great and greatly to be praised. He is terrible, beyond all gods.
Gama da girma Ubangiji yake, ya kuma cancanci yabo; tilas a ji tsoronsa fiye da dukan alloli.
5 For all the gods of the Gentiles are demons, but the Lord made the heavens.
Gama dukan allolin al’ummai gumaka ne, amma Ubangiji ne ya yi sammai.
6 Confession and beauty are in his sight. Sanctity and magnificence are in his sanctuary.
Daraja da ɗaukaka suna a gabansa; ƙarfi da ɗaukaka suna a cikin tsarkakar wurinsa.
7 Bring to the Lord, you natives of the nations, bring to the Lord glory and honor.
Ku ba wa Ubangiji, ya iyalan al’ummai ku ba wa Ubangiji ɗaukaka da kuma ƙarfi.
8 Bring to the Lord glory for his name. Lift up sacrifices, and enter into his courts.
Ku ba wa Ubangiji ɗaukakar da ta dace da sunansa; ku kawo sadaka ku kuma zo cikin filayen gidansa.
9 Adore the Lord in his holy court. Let the entire earth be shaken before his face.
Ku bauta wa Ubangiji da darajar tsarkinsa; ku yi rawar jiki a gabansa, dukan duniya.
10 Say among the Gentiles: The Lord has reigned. For he has even corrected the whole world, which will not be shaken. He will judge the peoples with fairness.
Ku faɗa cikin al’ummai, “Ubangiji yana mulki.” Duniya ta kahu daram, ba za a iya matsar da ita ba; zai yi wa mutane hukunci da gaskiya.
11 Let the heavens rejoice, and let the earth exult; let the sea and all its fullness be moved.
Bari sammai su yi farin ciki, bari duniya tă yi murna; bari teku tă yi ruri, da kuma dukan abin da yake cikinsa;
12 The fields and all the things that are in them will be glad. Then all the trees of the forest will rejoice
bari gonaki su yi tsalle da murna, da kuma kome da yake cikinsu. Ta haka dukan itatuwan kurmi za su rera don farin ciki;
13 before the face of the Lord: for he arrives. For he arrives to judge the earth. He will judge the whole world with fairness and the peoples with his truth.
za su rera a gaban Ubangiji, gama yana zuwa, yana zuwa don yă hukunta duniya. Zai hukunta duniya cikin adalci mutane kuma cikin amincinsa.