< Psalms 88 >
1 A Canticle Psalm to the sons of Korah. Unto the end. For Mahalath, to answer the understanding of Heman the Ezrahite. O Lord, God of my salvation: I have cried out, day and night, in your presence.
Waƙa ce, Zabura ta’ya’yan Kora maza. Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Bisa ga mahalat leyannotmaskil na Heman dangin Ezra. Ya Ubangiji, Allah wanda ya cece ni, dare da rana ina kuka a gabanka.
2 Let my prayer enter in your sight. Incline your ear to my petition.
Bari addu’ata ta zo a gabanka; ka kasa kunne ga kukata.
3 For my soul has been filled with evils, and my life has drawn near to Hell. (Sheol )
Gama raina yana cike da wahala rayuwata tana gab da kabari. (Sheol )
4 I am considered to be among those who will descend into the pit. I have become like a man without assistance,
An lissafta ni cikin waɗanda suka gangara zuwa cikin rami; ni kamar mutumin da ba shi da ƙarfi ne.
5 idle among the dead. I am like the wounded sleeping in sepulchers, whom you no longer remember, and who have been repelled by your hand.
An ware ni tare da matattu, kamar waɗanda aka kashe da suke kwance a kabari, waɗanda ba ka ƙara tunawa, waɗanda aka yanke daga taimakonka.
6 They have lain me in the lower pit: in dark places and in the shadow of death.
Ka sa ni a ramin da yake can ƙasa cikin zurfafa mafi duhu.
7 Your fury has been confirmed over me. And you have brought all your waves upon me.
Hasalarka tana da nauyi a kaina; ka turmushe ni da dukan raƙumanka. (Sela)
8 You have sent my acquaintances far from me. They have set me as an abomination to themselves. I was handed over, yet I did not depart.
Ka ɗauke abokaina na kurkusa daga gare ni ka sa na zama abin ƙyama a gare su. An kange ni, ba yadda zan kuɓuta
9 My eyes languished before destitution. All day long, I cried out to you, O Lord. I stretched out my hands to you.
idanuna ba sa gani sosai saboda baƙin ciki. Ina kira gare ka, ya Ubangiji, kowace rana; na tā da hannuwana zuwa gare ka.
10 Will you perform wonders for the dead? Or will physicians raise to life, and so confess to you?
Kakan nuna wa matattu ayyukanka na banmamaki ne? Waɗanda suka mutu sukan tashi su yabe ka ne? (Sela)
11 Could anyone declare your mercy in the sepulcher, or your truth from within perdition?
Ana furta ƙaunar a cikin kabari ne, ana zancen amincinka a cikin Hallaka ne?
12 Will your wonders be known in the darkness, or your justice in the land of oblivion?
An san ayyukanka masu banmamaki a wurin duhu ne, ko ayyukan adalcinka a lahira?
13 And I have cried out to you, O Lord, and in early morning, my prayer will come before you.
Amma ina kuka gare ka neman taimako, ya Ubangiji; da safe addu’ata kan zo gabanka.
14 Lord, why do you reject my prayer? Why do you turn your face away from me?
Don me, ya Ubangiji, ka ƙi ni ka kuma ɓoye fuskarka daga gare ni?
15 I am poor, and I have been amid hardships from my youth. And, though I have been exalted, I am humbled and disturbed.
Tun ina ƙarami na sha wahala na kuma yi kusa in mutu; na sha wahalar razanarka kuma na kuma fid da zuciya.
16 Your wrath has crossed into me, and your terrors have disturbed me.
Hasalarka ta sha kaina; razanarka ta hallaka ni.
17 They have surrounded me like water, all day long. They have surrounded me, all at once.
Dukan yini sun kewaye ni kamar rigyawa; sun mamaye ni ɗungum.
18 Friend and neighbor, and my acquaintances, you have sent far away from me, away from misery.
Ka ɗauke abokaina da ƙaunatattuna daga gare ni; duhu ne abokina na kurkusa.