< Psalms 28 >
1 A Psalm of David himself. To you, Lord, I will cry out. My God, do not be silent toward me. For if you remain silent toward me, I will become like those who descend into the pit.
Ta Dawuda. A gare ka nake kira, ya Ubangiji Dutsena; kada ka yi mini kunnen ƙashi. Gama in ka yi shiru, zan zama kamar waɗanda suka gangara rami.
2 Hear, O Lord, the voice of my supplication, when I pray to you, when I lift up my hands toward your holy temple.
Ka ji kukata ta neman jinƙai yayinda nake kira ka don neman taimako, yayinda nake daga hannuwana wajen Wurinka Mafi Tsarki.
3 Do not draw me away together with sinners; and let me not perish with those who work iniquity, who speak peacefully to their neighbor, yet evils are in their hearts.
Kada ka ja ni tare da mugaye, tare da masu yin mugunta, masu magana kamar ta alheri ce da maƙwabtansu amma suna riƙe da su a zukatansu.
4 Give to them according to their works and according to the wickedness of their inventions. Assign to them according to the works of their hands. Repay them with their own retribution.
Ka sāka musu da ayyukansu da kuma don mugun aikinsu; ka sāka musu saboda abin da hannuwansu suka yi ka kuma mayar musu abin da ya dace da su.
5 Since they have not understood the works of the Lord and the works of his hands, you will destroy them, and you will not build them up.
Da yake ba su kula da ayyukan Ubangiji da abin da hannuwansa suka yi ba, zai rushe su ba kuwa zai ƙara gina su ba.
6 Blessed is the Lord, for he has heard the voice of my supplication.
Yabo ya tabbata ga Ubangiji, gama ya ji kukata na neman jinƙai.
7 The Lord is my helper and my protector. In him, my heart has hoped and I have been helped. And my flesh has flourished again. And from my will, I shall confess to him.
Ubangiji shi ne ƙarfina da garkuwata; zuciyata ta amince da shi, kuma na sami taimako. Zuciyata ta yi tsalle don farin ciki zan kuwa yi godiya gare shi cikin waƙa.
8 The Lord is the strength of his people and the protector of the salvation of his Christ.
Ubangiji shi ne ƙarfin mutanensa, kagarar ceto domin shafaffensa.
9 O Lord, save your people and bless your inheritance, and reign over them and exalt them, even unto eternity.
Ka cece mutanenka ka kuma albarkace gādonka; ka zama mai kiwonsu ka kuma riƙe su har abada.