< Psalms 140 >
1 Unto the end. A Psalm of David. Rescue me, O Lord, from the evil man. Rescue me from the iniquitous leader.
Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Zabura ta Dawuda. Ka cece ni, ya Ubangiji, daga mugaye; ka tsare ni daga mutane masu rikici,
2 Those who have devised iniquities in their hearts: all day long they constructed conflicts.
masu shirya maƙarƙashiya a zukatansu suna kuma kawo yaƙi kullum.
3 They have sharpened their tongues like a serpent. The venom of asps is under their lips.
Suna sa harsunansu su yi kaifi kamar na maciji; dafin gamsheƙa yana a leɓunansu. (Sela)
4 Preserve me, O Lord, from the hand of the sinner, and rescue me from men of iniquity. They have decided to supplant my steps.
Ka kiyaye ni, ya Ubangiji, daga hannuwan mugaye; ka tsare ni daga mutane masu rikici waɗanda suke shirin kwashe ni a ƙafafu.
5 The arrogant have hidden a snare for me. And they have stretched out cords for a snare. They have placed a stumbling block for me near the road.
Masu girman kai sun sa mini tarko; sun shimfiɗa igiyoyin ragarsu sun kuma shirya mini tarko a hanyata. (Sela)
6 I said to the Lord: You are my God. O Lord, heed the voice of my supplication.
Ya Ubangiji, na ce maka, “Kai ne Allahna.” Ka ji kukata ta neman jinƙai, ya Ubangiji.
7 Lord, O Lord, the strength of my salvation: you have overshadowed my head in the day of war.
Ya Ubangiji Mai Iko Duka, mai fansana mai ƙarfi, wanda yake garkuwoyin kaina a ranar yaƙi.
8 O Lord, do not hand me over to the sinner by my desire. They have plotted against me. Do not abandon me, lest they should triumph.
Kada ka biya wa mugaye bukatunsu, ya Ubangiji; kada ka bar shirinsu su yi nasara, in ba haka ba za su yi fariya. (Sela)
9 The head of those who encompass me, the labor of their lips, will overwhelm them.
Bari kawunan waɗanda suka kewaye ni su rufu da masifun da leɓunansu suka jawo.
10 Burning coals will fall upon them. You will cast them down into the fire, into miseries that they will not be able to withstand.
Bari garwashin wuta yă zubo a kansu; bari a jefar da su cikin wuta, cikin rami mai zurfi, kada su sāke tashi.
11 A talkative man will not be guided aright upon the earth. Evils will drag the unjust man unto utter ruin.
Kada masu ɓata suna su taɓa kahu a ƙasar; bari masifa ta farauci mutane masu rikici.
12 I know that the Lord will accomplish justice for the needy and vindication for the poor.
Na san cewa Ubangiji ya shirya wa matalauta adalci yana kuma yi wa mabukata adalci.
13 So then, truly, the just will confess your name, and the upright will dwell with your countenance.
Tabbatacce masu adalci za su yabi sunanka masu aikata gaskiya kuma za su zauna a gabanka.