< Psalms 109 >
1 Unto the end. A Psalm of David.
Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Ta Dawuda. Zabura ce. Ya Allah, wanda nake yabo, kada ka yi shiru,
2 O God, do not be silent toward my praise, for the mouth of the sinner and the mouth of the deceitful one have been opened against me.
gama mugaye da masu ruɗu sun buɗe bakunansu a kaina; sun yi magana a kaina da harsunan ƙarya.
3 They have spoken against me with deceitful tongues, and they have surrounded me with hateful words, and they fought against me over nothing.
Da kalmomin ƙiyayya sun kewaye ni; sun tasar mini ba dalili.
4 Instead of choosing to act on my behalf, they detracted me. But I gave myself to prayer.
A maimakon ƙauna sun sāka mini da zargi, amma ni mutum ne mai addu’a.
5 And they set evil against me, instead of good, and hatred, in return for my love.
Sun sāka mini alheri da mugunta, ƙauna kuma da ƙiyayya.
6 Establish the sinner over him, and let the devil stand at his right hand.
Ka naɗa mugun mutum yă yi hamayya da shi; bari mai zargi yă tsaya a hannun damansa.
7 When he is judged, may he go forth in condemnation, and may his prayer be counted as sin.
Sa’ad da aka yi masa shari’a, bari a same shi da laifi, bari kuma addu’o’insa su hukunta shi.
8 May his days be few, and let another take his episcopate.
Bari kwanakinsa su zama kaɗan; bari wani yă ɗauki wurinsa na shugabanci.
9 May his sons be orphans, and his wife a widow.
Bari’ya’yansa su zama marayu matarsa kuma gwauruwa.
10 May his sons be carried by those who walk unsteadily, and may they go begging. And may they be cast out of their dwelling places.
Bari’ya’yansa su zama masu yawo suna bara; bari a yi ta koransu daga gidajensu da suke kufai.
11 May the money lenders scrutinize all his belongings, and let foreigners plunder his labors.
Bari mai binsa bashi yă ƙwace dukan abin da yake da shi; bari baƙi su washe amfanin aikinsa.
12 May there be no one to assist him, nor anyone to be compassionate to his orphaned children.
Bari kada kowa yă yi masa alheri ko yă ji tausayin marayunsa.
13 May his posterity be in utter ruin. In one generation, may his name be wiped away.
Bari duk zuriyarsa su mutu, a shafe sunayensu daga tsara mai zuwa.
14 May the iniquity of his fathers return in memory before the sight of the Lord, and do not let the sin of his mother be wiped away.
Bari a tuna da laifin kakanninsa a gaban Ubangiji; bari kada a taɓa shafe zunubin mahaifiyarsa.
15 May these be opposite the Lord always, but let their memory perish from the earth.
Bari zunubansu su kasance a gaban Ubangiji kullum, don yă sa a manta da su daga duniya.
16 For certain things are not remembered about them, in order to be merciful.
Gama bai taɓa yin tunanin yin alheri ba, amma ya tsananta wa matalauta da mabukata da kuma masu fid da zuciya har suka mutu.
17 And so the destitute man was pursued, with the beggar and the remorseful in heart, so as to be put to death.
Yana jin daɗin la’antarwa, bari yă dawo a kansa; ba ya son sa albarka, bari kada kowa yă sa masa albarka.
18 And he loved a curse, and it came to him. And he was unwilling to have a blessing, and it went far from him. And he clothed himself with curses like a garment, and it entered his inner self like water, and it entered his bones like oil.
Ya sa la’antarwa kamar rigarsa; ta shiga cikin jikinsa kamar ruwa, cikin ƙasusuwansa kamar mai.
19 May it be to him like a garment that covers him, and like a belt that always cinches him.
Bari tă zama kamar mayafin da aka ɗaura kewaye da shi, kamar ɗamara da aka ɗaura kewaye da shi har abada.
20 This is the work of those who detract me with the Lord and who speak evils against my soul.
Bari wannan yă zama sakayyar Ubangiji ga masu zargina, ga waɗanda suke mugayen maganganu a kaina.
21 But as for you, Lord, O Lord: act on my behalf for your name’s sake. For your mercy is sweet.
Amma kai, ya Ubangiji Mai Iko Duka, ka yi da ni da kyau saboda sunanka; ta alherin ƙaunarka, ka cece ni.
22 Free me, for I am destitute and poor, and my heart has been disquieted within me.
Gama ni matalauci ne mai bukata kuma, zuciyata kuwa ta yi rauni a cikina.
23 I have been taken away like a shadow when it declines, and I have been shaken off like locusts.
Na ɓace kamar inuwar yamma; ana kakkaɓe ni kamar fāra.
24 My knees have been weakened by fasting, and my flesh has been replaced by oil.
Gwiwoyina suna mutuwa saboda azumi; jikina ya rame ba kuma ƙarfi.
25 And I have become a disgrace to them. They saw me, and they shook their heads.
Na zama abin dariya ga masu zargina; sa’ad da suka gan ni, suka kaɗa kawunansu.
26 Help me, O Lord, my God. Save me according to your mercy.
Ka taimake ni, ya Ubangiji Allahna; ka cece ni bisa ga ƙaunarka.
27 And let them know that this is your hand, and that you, O Lord, have done this.
Bari su san cewa hannunka ne, cewa kai ne, ya Ubangiji, ka yi shi.
28 They will curse, and you will bless. May those who rise up against me be confounded. But your servant will rejoice.
Za su iya la’anta, amma kai za ka sa albarka; sa’ad da suka tasar za su sha kunya, amma bawanka zai yi farin ciki.
29 May those who detract me be clothed with shame, and may they be covered with their confusion, as if with a double cloak.
Masu zargina za su sha kunya za a rufe su da kunya kamar mayafi.
30 I will confess exceedingly to the Lord with my mouth. And I will praise him in the midst of the multitude.
Da bakina zan ɗaukaka Ubangiji sosai; cikin babban taro zan yabe shi.
31 For he stands at the right hand of the poor, in order to save my soul from persecutors.
Gama yana tsaya a hannun damar mai bukata, don yă cece ransa daga waɗanda suke hukunta shi.