< Numbers 2 >

1 And the Lord spoke to Moses and Aaron, saying:
Ubangiji ya ce wa Musa da Haruna,
2 “Each one shall make camp, by their troops, as well as by their insignia and standards, and by the houses of their kinships, all around the tabernacle of the covenant.”
“Duk sa’ad da Isra’ilawa suka yi sansani, kowane mutum zai sauka a inda tutar ƙungiyar kabilarsa take. Sansanin zai kasance a kewaye da Tentin Sujada.”
3 To the east, Judah shall fix his tents, by the companies of his army. And the leader of his sons shall be Nahshon the son of Amminadab.
Kabilar Yahuda za su yi sansani bisa ga ƙa’idarsu a gabas, wajen fitowar rana. Shugaban mutanen Yahuda kuwa shi ne Nashon ɗan Amminadab.
4 And the entire total of the fighting men from his stock was seventy-four thousand six hundred.
Yawan mutanen sashensa 74,600 ne.
5 Beside him, those of the tribe of Issachar were encamped, whose leader was Nathanael the son of Zuar.
Kabilar Issakar za su yi sansani biye da su. Shugabansu shi ne Netanel ɗan Zuwar.
6 And the entire number of his fighting men was fifty-four thousand four hundred.
Yawan mutanen sashensa 54,400 ne.
7 In the tribe of Zebulon, the leader was Eliab the son of Helon.
Kabilar Zebulun za su yi sansani biye da su. Shugabansu shi ne Eliyab ɗan Helon.
8 All the army of fighting men from his stock were fifty-seven thousand four hundred.
Yawan mutanen sashensa 57,400 ne.
9 All who were numbered in the camp of Judah were one hundred eighty-six thousand four hundred. And these, by their companies, shall go forth first.
Dukan mazan da aka ba su aiki a sansanin Yahuda bisa ga sashensu sun kai 186,400. Su ne za su ja gaba.
10 In the camp of the sons of Ruben, toward the south side, the leader shall be Elizur the son of Shedeur.
A kudu, a nan ne sashe sansanin mutanen Ruben a ƙarƙashin ƙa’idarsu, za su yi sansani. Shugaban mutanen Ruben shi ne Elizur ɗan Shedeyur.
11 And the entire army of his fighting men, who were numbered, were forty-six thousand five hundred.
Yawan mutanen sashensa 46,500 ne.
12 Beside him, those of the tribe of Simeon were encamped, whose leader was Shelumiel the son of Zurishaddai.
Kabilar Simeyon za su yi sansani biye da su. Shugaban mutanensa shi ne Shelumiyel ɗan Zurishaddai.
13 And the entire army of his fighting men, who were numbered, were fifty-nine thousand three hundred.
Yawan mutanen sashensa 59,300 ne.
14 In the tribe of Gad, the leader was Eliasaph the son of Reuel.
Kabilar Gad za su zama na biye. Shugaban mutanensa shi ne Eliyasaf ɗan Reyuwel.
15 And the entire army of his fighting men, who were numbered, were forty-five thousand six hundred fifty.
Yawan mutanen sashensa 45,650 ne.
16 All who were counted in the camp of Ruben were one hundred fifty thousand and one thousand four hundred fifty, by their companies. These shall advance in the second place.
Dukan mazan da aka ba su aiki a sansanin Ruben, bisa ga sashensu sun kai 151,450. Su ne za su zama na biyu in za a tashi.
17 But the tabernacle of the testimony shall be lifted up by the officers of the Levites and their companies. In the manner in which it is set up, so also shall it be taken down. Each one shall advance according to their places and ranks.
Sa’an nan Lawiyawa ɗauke da Tentin Sujada za su kasance a tsakiyar sansani sa’ad da aka tashi tafiya. Za su kama hanya kamar yadda aka dokace su su zauna a sansani, kowa a wurinsa a ƙarƙashin ƙa’idarsu.
18 On the west side, there shall be the camp of the sons of Ephraim, whose leader was Elishama the son of Ammihud.
Ta wajen yamma kuma sashen Efraim za su yi sansani a ƙarƙashin ƙa’idarsu. Shugaban mutanensa, shi ne Elishama ɗan Ammihud.
19 The entire army of his fighting men, who were numbered, were forty thousand five hundred.
Yawan mutanen sashensa 40,500 ne.
20 And with them was the tribe of the sons of Manasseh, whose leader was Gamaliel the son of Pedahzur.
Kabilar Manasse ce za tă zama ta biye. Shugabansu shi ne Gamaliyel ɗan Fedazur.
21 And the entire army of his fighting men, who were numbered, were thirty-two thousand two hundred.
Yawan mutanen sashensa 32,200 ne.
22 In the tribe of the sons of Benjamin, the leader was Abidan the son of Gideoni.
Na biye da su su ne mutanen Benyamin. Shugaban mutanensu kuwa Abidan ɗan Gideyoni.
23 And the entire army of his fighting men, who were counted, were thirty-five thousand four hundred.
Yawan mutanen sashensa 35,400 ne.
24 All who were numbered in the camp of Ephraim were one hundred eight thousand one hundred, by their companies. These shall advance third.
Dukan mazan da aka ba su aiki a sansanin Efraim, bisa ga sashensu su kai 108,100 ne. Su ne za su zama na uku sa’ad da za a tashi.
25 Toward the north side, the sons of Dan were encamped, whose leader was Ahiezer the son of Ammishaddai.
A arewa za a sami sashen sansanin Dan, a ƙarƙashin ƙa’idarsu. Shugabansu shi ne Ahiyezer ɗan Ammishaddai.
26 The entire army of his fighting men, who were numbered, were sixty-two thousand seven hundred.
Yawan mutanen sashensa 62,700 ne.
27 Beside him, those of the tribe of Asher fixed their tents, whose leader was Pagiel the son of Ochran.
Kabilar Asher ce za tă zama ta biye. Shugabansu shi ne Fagiyel ɗan Okran.
28 The entire army of his fighting men, who were numbered, were forty thousand and one thousand five hundred.
Yawan mutanen sashensa 41,500 ne.
29 From the tribe of the sons of Naphtali, the leader was Ahira the son of Enan.
Kabilar Naftali za su zama na biye da su. Shugaban mutanen kuwa shi ne Ahira ɗan Enan.
30 The entire army of his fighting men were fifty-three thousand four hundred.
Yawan mutanen sashensa 53,400 ne
31 All who were numbered in the camp of Dan were one hundred fifty-seven thousand six hundred; and these shall advance at the very end.
Dukan mazan da aka ba su aiki a sansanin Efraim, bisa ga sashensu su kai 157,600. Su ne za su zama na ƙarshe, ƙarƙashin ƙa’idarsu.
32 This is the number of the sons of Israel, of their army divided by the houses of their kinships and their companies: six hundred three thousand five hundred fifty.
Waɗannan su ne Isra’ilawan da aka a ƙidaya bisa ga iyalansu. Dukansu da suke a sansani, mutane 603,550 ne.
33 But the Levites were not numbered among the sons of Israel. For so the Lord had instructed Moses.
Ba a dai ƙidaya Lawiyawa tare da sauran Isra’ilawa ba yadda Ubangiji ya umarci Musa.
34 And the sons of Israel acted according to all the things that the Lord had commanded. They were encamped by their companies, and they advanced by the families and houses of their fathers.
Saboda haka Isra’ilawa suka yi duk ko mene ne da Ubangiji ya umarci Musa. Ta haka ne suka yi sansani a ƙarƙashin ƙa’idarsu kowanne tare da kabilarsa da danginsa.

< Numbers 2 >