< Matthew 5 >

1 Then, seeing the crowds, he ascended the mountain, and when he had sat down, his disciples drew near to him,
Da Yesu ya ga taron jama'ar, sai ya hau saman dutse. Sa'adda ya zauna, almajiransa suka zo wurinsa.
2 and opening his mouth, he taught them, saying:
Ya bude bakinsa kuma ya koyar da su, yana cewa,
3 “Blessed are the poor in spirit, for theirs is the kingdom of heaven.
“Albarka ta tabbata ga masu talauci a ruhu, domin mulkin sama nasu ne.
4 Blessed are the meek, for they shall possess the earth.
Albarka ta tabbata ga masu makoki, domin za a ta'azantar da su.
5 Blessed are those who mourn, for they shall be consoled.
Albarka ta tabbata ga masu tawali'u, domin za su gaji duniya.
6 Blessed are those who hunger and thirst for justice, for they shall be satisfied.
Albarka ta tabbata ga masu yunwa da kishin adalci, domin za a kosar da su.
7 Blessed are the merciful, for they shall obtain mercy.
Albarka ta tabbata ga masu jinkai, domin za su samu jinkai.
8 Blessed are the pure in heart, for they shall see God.
Albarka ta tabbata ga masu tsabtar zuciya, domin za su ga Allah.
9 Blessed are the peacemakers, for they shall be called sons of God.
Albarka ta tabbata ga masu kawo salama, domin za a ce da su 'ya'yan Allah.
10 Blessed are those who endure persecution for the sake of justice, for theirs is the kingdom of heaven.
Albarka ta tabbata ga wadanda ake tsananta masu saboda adalci, domin mulkin sama nasu ne.
11 Blessed are you when they have slandered you, and persecuted you, and spoken all kinds of evil against you, falsely, for my sake:
Masu albarka ne ku sa'adda mutane suka zage ku, suka kuma tsananta maku, ko kuwa suka zarge ku da dukan miyagun abubuwa iri iri na karya, saboda ni.
12 be glad and exult, for your reward in heaven is plentiful. For so they persecuted the prophets who were before you.
Ku yi murna da matukar farin ciki, domin sakamakonku mai yawan gaske ne a sama. Ta haka ne mutane suka tsananta wa annabawa da suka yi rayuwa kafin ku.
13 You are the salt of the earth. But if salt loses its saltiness, with what will it be salted? It is no longer useful at all, except to be cast out and trampled under by men.
Ku ne gishirin duniya, amma idan gishiri ya sane yaya za a mai da dandanonsa? Ba zai kara anfani ga komai ba, sai ko a zubar da shi, a tattake a karkashin kafafun mutane.
14 You are the light of the world. A city set on a mountain cannot be hidden.
Ku ne hasken duniya, birnin da ke kan tudu ba shi boyuwa.
15 And they do not light a lamp and put it under a basket, but on a lampstand, so that it may shine to all who are in the house.
Mutane ba za su kunna fitila su sa ta karkashin kwando ba, sai ko a dora ta a mazaunin ta, domin ta ba da haske ga kowa da ke gidan.
16 So then, let your light shine in the sight of men, so that they may see your good works, and may glorify your Father, who is in heaven.
Bari hasken ku ya haskaka gaban mutane yadda za su ga kyawawan ayyukanku su kuma yabi Ubanku da ke cikin sama.
17 Do not think that I have come to loosen the law or the prophets. I have not come to loosen, but to fulfill.
Kada ku yi tsammanin na zo ne domin in rushe shari'a ko annabawa. Ban zo domin in rushe su ba, amma domin in cika su.
18 Amen I say to you, certainly, until heaven and earth pass away, not one iota, not one dot shall pass away from the law, until all is done.
Domin gaskiya ina gaya maku, har sama da kasa su shude, amma digo ko wasali daya ba za ya shude ba a cikin shari'ar, sai an cika dukan al'amura.
19 Therefore, whoever will have loosened one of the least of these commandments, and have taught men so, shall be called the least in the kingdom of heaven. But whoever will have done and taught these, such a one shall be called great in the kingdom of heaven.
Saboda haka duk wanda ya karya mafi kankanta daga cikin dokokin nan ko kuwa ya koya wa wasu su yi haka, za a kira shi mafi kankanta a cikin mulkin sama. Amma dukan wanda ya kiyaye su ko kuwa ya koyar da su, za a kira shi mafi girma a cikin mulkin sama.
20 For I say to you, that unless your justice has surpassed that of the scribes and the Pharisees you shall not enter into the kingdom of heaven.
Gama ina gaya maku cewa idan adalcin ku bai zarce adalcin marubuta da Farisawa ba, babu yadda za ku shiga mulkin sama.
21 You have heard that it was said to the ancients: ‘You shall not murder; whoever will have murdered shall be liable to judgment.’
Kun ji dai an ce wa mutanen da, 'Kada ka yi kisan kai,' kuma 'Duk wanda ya yi kisan kai yana cikin hatsarin hukunci.'
22 But I say to you, that anyone who becomes angry with his brother shall be liable to judgment. But whoever will have called his brother, ‘Idiot,’ shall be liable to the council. Then, whoever will have called him, ‘Worthless,’ shall be liable to the fires of Hell. (Geenna g1067)
Amma ina gaya muku, duk wanda ya yi fushi da dan'uwansa, yana cikin hatsarin hukunci. Kuma duk wanda ya ce da dan'uwansa, 'Kai mutumin banza!' yana cikin hatsarin tsayawa gaban majalisa, kowa kuma ya ce da dan'uwan sa 'Kai wawa!' yana cikin hatsarin shiga wutar jahannama. (Geenna g1067)
23 Therefore, if you offer your gift at the altar, and there you remember that your brother has something against you,
Saboda haka idan za ka yi baiko a bagadi sai ka tuna cewa dan'uwanka yana da damuwa da kai,
24 leave your gift there, before the altar, and go first to be reconciled to your brother, and then you may approach and offer your gift.
ka bar baikon ka a gaban bagadin, ka yi tafiyarka. Da farko dai, ka sasanta da dan'uwanka kafin ka zo ka mika baikon.
25 Be reconciled with your adversary quickly, while you are still on the way with him, lest perhaps the adversary may hand you over to the judge, and the judge may hand you over to the officer, and you will be thrown in prison.
Ka yi sulhu da mai karar ka tun kana hanyar zuwa gaban shari'a, domin kada mai karar ka ya mika ka ga alkali, alkali kuwa ya mika ka ga dogarai, za a kuwa jefa ka a kurkuku.
26 Amen I say to you, that you shall not go forth from there, until you have repaid the last quarter.
Gaskiya ina gaya maka, ba za ka taba fita daga can ba sai ko ka biya dukan kudin da ya ke binka.
27 You have heard that it was said to the ancients: ‘You shall not commit adultery.’
Kun dai ji an ce, 'Kada ka yi zina'.
28 But I say to you, that anyone who will have looked at a woman, so as to lust after her, has already committed adultery with her in his heart.
Amma ina gaya maku, duk wanda ya dubi mace, da muguwar sha'awa, ya riga ya yi zina da ita a zuciyarsa.
29 And if your right eye causes you to sin, root it out and cast it away from you. For it is better for you that one of your members perish, than that your whole body be cast into Hell. (Geenna g1067)
Idan idonka na dama zai sa ka tuntube, kwakule shi ka jefar daga gareka. Don gara daya daga cikin gabobinka ya halaka, da a jefa dukan jikin ka a jahannama. (Geenna g1067)
30 And if your right hand causes you to sin, cut it off and cast it away from you. For it is better for you that one of your members perish, than that your whole body go into Hell. (Geenna g1067)
Ko kuwa idan hannunka na dama zai sa ka tuntube, ka yanke shi ka jefar daga gare ka. Domin gara daya daga cikin gabobin ka ya halaka, da a jefa dukan jikinka a jahannama. (Geenna g1067)
31 And it has been said: ‘Whoever would dismiss his wife, let him give her a bill of divorce.’
An sake fada, 'Duk wanda ya kori matarsa, sai ya ba ta takaddar saki.'
32 But I say to you, that anyone who will have dismissed his wife, except in the case of fornication, causes her to commit adultery; and whoever will have married her who has been dismissed commits adultery.
Amma ina gaya maku ko wa ya saki matarsa, idan ba a kan laifin lalata ba, ya mai da ita mazinaciya kenan. Kuma duk wanda ya aure ta bayan sakin, ya yi zina kenan.
33 Again, you have heard that it was said to the ancients: ‘You shall not swear falsely. For you shall repay your oaths to the Lord.’
Kun sake ji an ce wa wadan da suke a zamanin da, 'Kada ku yi rantsuwar karya, amma ku yi rantsuwar ku ga Ubangiji.'
34 But I say to you, do not swear an oath at all, neither by heaven, for it is the throne of God,
Amma ina gaya maku, kada ku yi rantsuwa sam, ko da sama domin kursuyin Allah ne;
35 nor by earth, for it is his footstool, nor by Jerusalem, for it is the city of the great king.
ko kuwa da duniya, domin mazaunin kafafunsa ne, ko da Urushalima, domin birnin babban sarki ne.
36 Neither shall you swear an oath by your own head, because you are not able to cause one hair to become white or black.
Ko ma ace ku yi rantsuwa da kanku, domin ba za ku iya mai da gashin kanku baki ko fari ba.
37 But let your word ‘Yes’ mean ‘Yes,’ and ‘No’ mean ‘No.’ For anything beyond that is of evil.
Amma bari maganarku ta zama 'I, I', ko kuwa 'A'a, a'a.' Duk abin da ya wuce wannan, daga mugun yake.
38 You have heard that it was said: ‘An eye for an eye, and a tooth for a tooth.’
Kun dai ji an ce, “Ido a maimakon ido, hakori kuma a maimakon hakori.'
39 But I say to you, do not resist one who is evil, but if anyone will have struck you on your right cheek, offer to him the other also.
Amma ina gaya maku, kada ku yi jayayya da wanda ke mugu, a maimakon haka, ko wa ya mare ku a kuncin dama, ku juya masa dayan ma.
40 And anyone who wishes to contend with you in judgment, and to take away your tunic, release to him your cloak also.
Idan wani yana da niyyar kai kararku gaban shari'a saboda ya karbi rigarku, ku ba wannan mutumin mayafinku ma.
41 And whoever will have compelled you for one thousand steps, go with him even for two thousand steps.
Duk wanda ya tilasta ku ga tafiyar mil daya, ku je da shi biyu.
42 Whoever asks of you, give to him. And if anyone would borrow from you, do not turn away from him.
Ku ba kowa da ya tambaye ku, kuma kada ku hana kowa da ke neman rance a wurinku.
43 You have heard that it was said, ‘You shall love your neighbor, and you shall have hatred for your enemy.’
Kun ji abin da aka fada, 'Za ka kaunaci makwabcin ka ka ki magabcin ka.'
44 But I say to you: Love your enemies. Do good to those who hate you. And pray for those who persecute and slander you.
Amma ina gaya maku, ku kaunaci magabtan ku, ku yi addu'a domin masu tsananta maku, ku albarkaci wadanda suka la'ance ku, ku yi alheri ga wadanda suke kin ku,
45 In this way, you shall be sons of your Father, who is in heaven. He causes his sun to rise upon the good and the bad, and he causes it to rain upon the just and the unjust.
domin ku zama 'ya'yan Ubanku da ke cikin sama. Domin yakan sa rana ta haskaka wa mugu da mutumin kirki, kuma yakan aiko da ruwan sama ga adali da azzalumi.
46 For if you love those who love you, what reward will you have? Do not even tax collectors behave this way?
Domin idan kuna kaunar wadanda suke kaunarku, wanne lada kuka samu? Ba haka masu karban haraji ma suke yi ba?
47 And if you greet only your brothers, what more have you done? Do not even the pagans behave this way?
Kuma in kun gaida 'yan'uwanku kadai, me kuke yi fiye da sauran? Ba hakanan al'ummai ma suke yi ba?
48 Therefore, be perfect, even as your heavenly Father is perfect.”
Saboda haka, lalle ne ku zama cikakku, kamar yadda Ubanku na sama yake cikakke.

< Matthew 5 >