< Matthew 21 >
1 And when they had drawn near to Jerusalem, and had arrived at Bethphage, at the Mount of Olives, then Jesus sent two disciples,
Da suka yi kusa da Urushalima suka kuma kai Betfaji da yake kan Dutsen Zaitun, sai Yesu ya aiki almajirai biyu,
2 saying to them: “Go into the town that is opposite you, and immediately you will find a donkey tied, and a colt with her. Release them, and lead them to me.
yana ce musu, “Ku je ƙauyen da yake gabanku, nan take za ku ga wata jaka a daure tare da ɗanta kusa da ita, a can. Ku kunce su ku kawo mini.
3 And if anyone will have said anything to you, say that the Lord has need of them. And he will promptly dismiss them.”
In wani ya yi muku wata magana, ku ce masa Ubangiji yana bukatarsu, zai kuwa mai da su nan da nan.”
4 Now all this was done in order to fulfill what was spoken through the prophet, saying,
Wannan ya faru ne don a cika abin da aka faɗa ta bakin annabin cewa,
5 “Tell the daughter of Zion: Behold, your king comes to you meekly, sitting on a donkey and on a colt, the son of one accustomed to the yoke.”
“Ku ce wa Diyar Sihiyona, ‘Duba, sarkinki yana zuwa gare ki, mai tawali’u yana a kan jaki, a kan aholaki, ɗan jaki.’”
6 Then the disciples, going out, did just as Jesus instructed them.
Almajiran suka tafi suka yi kamar yadda Yesu ya umarce su.
7 And they brought the donkey and the colt, and they laid their garments on them, and they helped him sit upon them.
Suka kawo jakar da ɗanta, suka shimfiɗa mayafansu a kansu, Yesu kuma ya zauna a kansu.
8 Then a very numerous crowd spread their garments on the way. But others cut branches from the trees and scattered them on the way.
Wani babban taron mutane suka shimfiɗa mayafansu a kan hanya, yayinda waɗansu suka sassari rassan itatuwa suka shisshimfiɗa a kan hanya.
9 And the crowds that preceded him, and those that followed, cried out, saying: “Hosanna to the Son of David! Blessed is he who comes in the name of the Lord. Hosanna in the highest!”
Taron mutanen da suke gabansa da kuma waɗanda suke binsa a baya suka yi ihu suna cewa, “Hosanna ga Ɗan Dawuda!” “Mai albarka ne wanda yake zuwa cikin sunan Ubangiji!” “Hosanna a cikin sama!”
10 And when he had entered into Jerusalem, the entire city was stirred up, saying, “Who is this?”
Sa’ad da Yesu ya shiga Urushalima, dukan birnin ya ruɗe, ana ta tambaya, “Wane ne wannan?”
11 But the people were saying, “This is Jesus, the Prophet from Nazareth of Galilee.”
Taron mutane suka amsa, “Wannan shi ne Yesu, annabin nan daga Nazaret a Galili.”
12 And Jesus entered into the temple of God, and he cast out all who were selling and buying in the temple, and he overturned the tables of the money changers and the chairs of the vendors of doves.
Yesu ya shiga filin haikali, ya kuma kori duk masu saya da sayarwa a can. Ya tutture tebur masu canjin kuɗi da kuma kujerun masu sayar da tattabarai.
13 And he said to them: “It is written: ‘My house shall be called a house of prayer. But you have made it into a den of robbers.’”
Ya ce musu, “A rubuce yake, ‘Za a ce da gidana, gidan addu’a,’amma kuna mai da shi ‘kogon’yan fashi.’”
14 And the blind and the lame drew near to him in the temple; and he healed them.
Makafi da guragu suka zo wurinsa a haikali, ya kuwa warkar da su.
15 Then the leaders of the priests and the scribes became indignant, seeing the miracles that he wrought, and the children crying out in the temple, saying, “Hosanna to the Son of David!”
Amma da manyan firistoci da malaman dokoki suka ga abubuwan banmamakin da ya yi, yara kuma suna ihu a filin haikali suna cewa, “Hosanna ga Ɗan Dawuda,” sai fushi ya kama su.
16 And they said to him, “Do you hear what these ones are saying?” But Jesus said to them, “Certainly. Have you never read: For out of the mouth of babes and infants, you have perfected praise?”
Suka tambaye shi suka ce, “Kana jin abin da waɗannan suke faɗa?” Yesu ya amsa ya ce, “I, ba ku taɓa karanta ba cewa, “‘Daga leɓunan yara da jarirai kai, Ubangiji, ka shirya wa kanka yabo’?”
17 And leaving them behind, he went out, beyond the city, into Bethania, and he lodged here.
Sai ya bar su, ya fita daga birnin ya tafi Betani, inda ya kwana.
18 Then, as he was returning to the city in the morning, he was hungry.
Kashegari da sassafe, yayinda yake kan hanyarsa ta komawa cikin birni, sai ya ji yunwa.
19 And seeing a certain fig tree beside the way, he approached it. And he found nothing on it, except only leaves. And he said to it, “May fruit never spring forth from you, for all time.” And immediately the fig tree was dried up. (aiōn )
Ganin itacen ɓaure kusa da hanya, sai ya je wajensa amma bai sami kome a kansa ba sai ganye. Sai ya ce masa, “Kada ka ƙara yin’ya’ya!” Nan da nan itacen ya yanƙwane. (aiōn )
20 And seeing this, the disciples wondered, saying, “How did it dry up so quickly?”
Sa’ad da almajiran suka ga haka, sai suka yi mamaki suna tambaya, “Yaya itacen ɓauren ya yanƙwane nan da nan haka?”
21 And Jesus responded to them by saying: “Amen I say to you, if you have faith and do not hesitate, not only shall you do this, concerning the fig tree, but even if you would say to this mountain, ‘Take and cast yourself into the sea,’ it shall be done.
Yesu ya amsa ya ce, “Gaskiya nake gaya muku, in kuna da bangaskiya, ba kuwa da wata shakka ba, ba kawai za ku iya yin abin da aka yi wa itacen ɓauren nan ba, amma za ku ma iya ce wa dutsen nan, ‘Je ka, ka jefa kanka cikin teku,’ sai yă faru.
22 And all things whatsoever that you shall ask for in prayer: believing, you shall receive.”
In kun gaskata, za ku karɓi duk abin da kuka roƙa a cikin addu’a.”
23 And when he had arrived at the temple, as he was teaching, the leaders of the priests and the elders of the people approached him, saying: “By what authority do you do these things? And who has given this authority to you?”
Sai Yesu ya shiga filin haikali, yayinda yake koyarwa, sai manyan firistoci da dattawan mutane suka zo wurinsa suka yi tambaya, “Da wane iko kake yin waɗannan abubuwa? Kuma wa ya ba ka wannan iko?”
24 In response, Jesus said to them: “I also will question you with one word: if you tell me this, I also will tell you by what authority I do these things.
Yesu ya amsa ya ce, “Ni ma zan yi muku tambaya guda. In kuka ba ni amsa, ni ma zan gaya muku ko da wane iko nake yin waɗannan abubuwa.
25 The baptism of John, where was it from? Was it from heaven, or from men?” But they thought within themselves, saying:
Baftismar Yohanna, daga ina ta fito? Daga sama ce, ko daga mutane?” Sai suka tattauna a junansu suka ce, “In muka ce, ‘Daga sama,’ zai ce, ‘To, me ya sa ba mu gaskata shi ba?’
26 “If we say, ‘From heaven,’ he will say to us, ‘Then why did you not believe him?’ But if we say, ‘From men,’ we have the crowd to fear, for they all hold John to be a prophet.”
In kuma muka ce, ‘Daga mutane,’ muna tsoron mutane, gama duk sun ɗauka Yohanna annabi ne.”
27 And so, they answered Jesus by saying, “We do not know.” So he also said to them: “Neither will I tell you by what authority I do these things.
Saboda haka suka amsa wa Yesu suka ce, “Ba mu sani ba.” Sai ya ce, “Ni ma ba zan gaya muku ko da wane iko nake yin waɗannan abubuwa ba.”
28 But how does it seem to you? A certain man had two sons. And approaching the first, he said: ‘Son, go out today to work in my vineyard.’
“Me kuka gani? An yi wani mutum wanda yake da’ya’ya biyu maza. Sai ya je wajen ɗan farin ya ce, ‘Ɗana, yau tafi gonar inabi ka yi aiki.’
29 And responding, he said, ‘I am not willing.’ But afterwards, being moved by repentance, he went.
“Ya amsa ya ce, ‘Ba zan tafi ba,’ amma daga baya ya sāke tunani, ya tafi.
30 And approaching the other, he spoke similarly. And answering, he said, ‘I am going, lord.’ And he did not go.
“Sai mahaifin ya tafi waje na biyun ya faɗa masa iri magana guda. Sai ya amsa ya ce, ‘Zan tafi, ranka yă daɗe,’ amma bai tafi ba.
31 Which of the two did the will of the father?” They said to him, “The first.” Jesus said to them: “Amen I say to you, that tax collectors and prostitutes shall precede you, into the kingdom of God.
“Wanne cikin yaran nan biyu ya yi abin da mahaifinsa yake so?” Suka amsa, “Na farin.” Yesu ya ce musu, “Gaskiya nake gaya muku, masu karɓar haraji da karuwai suna riga ku shiga mulkin Allah.
32 For John came to you in the way of justice, and you did not believe him. But the tax collectors and the prostitutes believed him. Yet even after seeing this, you did not repent, so as to believe him.
Gama Yohanna Mai Baftisma ya zo wurinku don yă nuna muku hanyar adalci, ba ku gaskata shi ba, amma masu karɓar haraji da karuwai sun gaskata. Har ma bayan kun ga wannan, ba ku tuba kun gaskata shi ba.”
33 Listen to another parable. There was a man, the father of a family, who planted a vineyard, and surrounded it with a hedge, and dug a press in it, and built a tower. And he loaned it out to farmers, and he set out to sojourn abroad.
“Ku saurari wani misali. An yi wani mai gona wanda ya yi gonar inabi. Ya kewaye ta da katanga, ya haƙa wurin matsin inabi a ciki, ya kuma gina hasumiyar gadi. Sa’an nan ya ba wa waɗansu manoma hayar gonar inabin, ya kuma yi tafiya.
34 Then, when the time of the fruits drew near, he sent his servants to the farmers, so that they might receive its fruits.
Da lokacin girbi ya yi kusa, sai ya aiki bayinsa wajen’yan hayan, su karɓo masa’ya’yan inabi.
35 And the farmers apprehended his servants; they struck one, and killed another, and stoned yet another.
“Amma’yan hayan suka kama bayinsa; suka dūke ɗaya, suka kashe ɗaya, suka kuma jajjefi na ukun.
36 Again, he sent other servants, more than before; and they treated them similarly.
Sai ya sāke aiken waɗansu bayi wurinsu, fiye da na dā yawa, amma’yan hayan suka yi musu kamar yadda suka yi wa na farin.
37 Then, at the very end, he sent his son to them, saying: ‘They will revere my son.’
A ƙarshe, sai ya aiki ɗansa a wurinsu. Ya ce, ‘Za su girmama ɗana.’
38 But the farmers, seeing the son, said among themselves: ‘This is the heir. Come, let us kill him, and then we will have his inheritance.’
“Amma da’yan hayan suka hangi ɗan, sai suka ce wa juna, ‘Wannan shi ne magājin. Ku zo, mu kashe shi, mu ci gādonsa.’
39 And apprehending him, they cast him outside the vineyard, and they killed him.
Saboda haka suka kama shi, suka jefar da shi bayan katangar gonar inabin, suka kashe shi.
40 Therefore, when the lord of the vineyard arrives, what will he do to those farmers?”
“To, idan mai gonar inabin ya zo, me zai yi da’yan hayan nan?”
41 They said to him, “He will bring those evil men to an evil end, and he will loan out his vineyard to other farmers, who shall repay to him the fruit in its time.”
Suka amsa suka ce, “Zai yi wa banzan mutanen nan mugun kisa, yă ba da hayar gonar inabin ga waɗansu’yan haya, waɗanda za su ba shi rabonsa na amfanin gona a lokacin girbi.”
42 Jesus said to them: “Have you never read in the Scriptures: ‘The stone that the builders have rejected has become the cornerstone. By the Lord has this been done, and it is wonderful in our eyes?’
Yesu ya ce musu, “Ashe, ba ku taɓa karanta a cikin Nassi cewa, “‘Dutsen da magina suka ƙi shi ne ya zama dutsen kusurwar gini. Ubangiji ne ya aikata wannan, kuma abin mamaki ne a idanunmu’?
43 Therefore, I say to you, that the kingdom of God will be taken away from you, and it shall be given to a people who shall produce its fruits.
“Saboda haka, ina gaya muku cewa za a karɓe mulkin Allah daga gare ku, a ba wa mutanen da za su ba da amfani.
44 And whoever will have fallen on this stone shall be broken, yet truly, on whomever it shall fall, it will crush him.”
Duk wanda ya fāɗi a kan dutsen nan, zai kakkarye. Amma duk wanda dutsen nan ya fāɗi a kansa, za a murƙushe shi.”
45 And when the leaders of the priests, and the Pharisees had heard his parables, they knew that he was speaking about them.
Da manyan firistoci da Farisiyawa suka ji misalan Yesu, sai suka gane cewa da su yake.
46 And though they sought to take hold of him, they feared the crowds, because they held him to be a prophet.
Suka nemi hanyar kama shi, amma suka ji tsoron taron, don mutane sun ɗauka shi annabi ne.