< Mark 2 >
1 And after some days, he again entered into Capernaum.
Da ya dawo Kafarnahum bayan yan kwanaki kadan, aka ji cewa yana gida.
2 And it was heard that he was in the house. And so many gathered that there was no room left, not even at the door. And he spoke the word to them.
Da yawa suka taru a can, ba wuri har kofa, sai Yesu ya yi masu magana.
3 And they came to him, bringing a paralytic, who was being carried by four men.
Sai wadansu mutane su ka zo wurinsa dauke da wuni mutum shanyayye, mutane hudu na dauke da shi.
4 And when they were not able to present him to him because of the crowd, they uncovered the roof where he was. And opening it, they lowered down the stretcher on which the paralytic was lying.
Lokacin da ba su iya zuwa kusa da shi ba domin yawan jama'a, sai su ka daye jinkar dakin daidai da inda ya ke. Bayan da suka huda ramin suka saukar da gado wanda shanyayyen ke kwance a kai.
5 Then, when Jesus had seen their faith, he said to the paralytic, “Son, your sins are forgiven you.”
Da ganin bangaskiyarsu, Yesu ya ce wa shanyayyen mutumin, “Da, an gafarta maka zunuban ka”.
6 But some of the scribes were sitting in that place and thinking in their hearts:
Amma wadansu marubuta da ke zaune a nan, suka yi tunani aransu.
7 “Why is this man speaking in this way? He is blaspheming. Who can forgive sins, but God alone?”
Yaya wannan mutum zai yi magana haka? Ya yi sabo! wa ke iya gafarta zunubi “sai Allah kadai?”
8 At once, Jesus, realizing in his spirit that they were thinking this within themselves, said to them: “Why are you thinking these things in your hearts?
Nan da nan Yesu ya sani a ruhunsa, abinda suke tunani a tsakaninsu. Ya ce masu, “Me ya sa kuke tunanin wannan a zuciyarku?
9 Which is easier, to say to the paralytic, ‘Your sins are forgiven you,’ or to say, ‘Rise up, take up your stretcher, and walk?’
Me yafi sauki a cewa shanyayyen mutumin, 'An gafarta maka zunuban ka' ko kwa a ce masa, 'tashi, ka dauki shinfidarka, ka yi tafiyarka'?
10 But so that you may know that the Son of man has authority on earth to forgive sins,” he said to the paralytic:
Amma domin ku san cewa Dan mutum na da ikon gafarta zunubi a duniya, ya ce wa shanyayyen,
11 “I say to you: Rise up, take up your stretcher, and go into your house.”
''Na ce maka, tashi, dauki tabarmanka, ka tafi gidan ka.”
12 And immediately he got up, and lifting up his stretcher, he went away in the sight of them all, so that they all wondered. And they honored God, by saying, “We have never seen anything like this.”
Sai nan da nan ya tashi ya dauki tabarmarsa, ya fita gidan a gabansu, dukansu su ka yi mamaki, su ka girmama Allah, ''suka ce ba mu taba ganin abu irin wannan ba.”
13 And he departed again to the sea. And the entire crowd came to him, and he taught them.
Ya sake fita gefen tafki, dukan taron jama'a suka zo wurinsa, sai ya koya masu.
14 And as he was passing by, he saw Levi of Alphaeus, sitting at the customs office. And he said to him, “Follow me.” And rising up, he followed him.
Sa'adda ya na wucewa, ya ga Levi dan Halfa yana zaune a wurin karbar haraji, sai ya ce masa, “Ka biyo ni.” Ya tashi, ya bi shi.
15 And it happened that, as he sat at table in his house, many tax collectors and sinners sat at table together with Jesus and his disciples. For those who followed him were many.
Sa'adda Yesu ya shiga gidan Levi yana cin abinci, masu karbar haraji da masu zunubi da yawa su ka zo wurinsa da almajiransa, jama'a masu yawan gaske suka ka bi shi.
16 And the scribes and the Pharisees, seeing that he ate with tax collectors and sinners, said to his disciples, “Why does your Teacher eat and drink with tax collectors and sinners?”
Da Marubuta wadanda su ke Farisawa, sun ga cewa Yesu na cin abinci da masu zunubi da masu karbar haraji, sai su ka ce wa almajiransa, “Me ya sa ya ke ci da masu karbar haraji da mutane masu zunubi?”
17 Jesus, having heard this, said to them: “The healthy have no need of a doctor, but those who have maladies do. For I came not to call the just, but sinners.”
Da Yesu ya ji wannan ya ce masu, “Mutane wadanda ke da lafiya a jiki ba su bukatar likita; sai dai ko marasa lafiya ke bukatarsa. Ban zo domin in kira mutane masu a dalci ba, amma mutane masu zunubi.”
18 And the disciples of John, and the Pharisees, were fasting. And they arrived and said to him, “Why do the disciples of John and of the Pharisees fast, but your disciples do not fast?”
Almajiran Yahaya da Farisawa suna azumi, sai wadansu mutane suka zo suka ce, “Don me almajiran Yahaya da almajiran Farisawa na azumi amma na ka almajiran ba su yi?”
19 And Jesus said to them: “How can the sons of the wedding fast while the groom is still with them? During whatever time they have the groom with them, they are not able to fast.
Sai Yesu yace masu, “Abokan ango, za su yi azumi sa'adda ango yake tare da su? muddin suna tare da ango ba za su yi azumi ba.
20 But the days will arrive when the groom will be taken away from them, and then they shall fast, in those days.
Amma kwanaki za su zo da za a dauki angon daga gare su, a wadancan kwanakin ne, za su yi azumi.
21 No one sews a patch of new cloth onto an old garment. Otherwise, the new addition pulls away from the old, and the tear becomes worse.
Babu wanda zai dinka sabuwar riga ya hada ta da tsohuwar riga, sai rigar ta yage, kuma ta yi mummunar yagewa.
22 And no one puts new wine into old wineskins. Otherwise, the wine will burst the wineskins, and the wine will pour out, and the wineskins will be lost. Instead, new wine must be put into new wineskins.”
Babu wanda zai sa sabon ruwan inabi a cikin tsohuwar salka, ai sai salkar ta fashe kuma ruwan inabin ya zube. duka biyu ruwan inabin da salkar arasa su. A maimakon haka, sai ka sanya sabon ruwan inabi cikin sabuwar salka.”
23 And again, while the Lord was walking through the ripe grain on the Sabbath, his disciples, as they advanced, began to separate the ears of grains.
A ranar asabar Yesu ya tafi cikin gonakin hatsi, sai almajiransa su ka fara zagar hatsi,
24 But the Pharisees said to him, “Behold, why are they doing what is not lawful on the Sabbaths?”
Sai Farisawa su ka ce masa, “Duba, don me suke yin abin da bai dace a yi ranar Asabar ba?”
25 And he said to them: “Have you never read what David did, when he had need and was hungry, both he and those who were with him?
Yace masu, Ba ku karanta ba abinda Dauda ya yi sa'adda yake jin yunwa, shi da mutanen da ke tare da shi?
26 How he went into the house of God, under the high priest Abiathar, and ate the bread of the Presence, which it was not lawful to eat, except for the priests, and how he gave it to those who were with him?”
Yadda ya shiga gidan Ubangiji, sa'adda Abiyata ya ke babban firist, ya ci gurasa da ke ta firist wadda bai dace wani ya ci ba sai Firistoci. Har kuma ya ba wadanda ke tare da shi.”
27 And he said to them: “The Sabbath was made for man, and not man for the Sabbath.
Yesu yace, “Asabar an yi ta don mutum ne, ba a yi mutum don Asabar ba.
28 And so, the Son of man is Lord, even of the Sabbath.”
Saboda haka, Dan Mutum Ubangiji ne, har da na Asabar.”