< Luke 7 >
1 And when he had completed all his words in the hearing of the people, he entered Capernaum.
Bayan da Yesu ya gama fadar dukan abubuwan da zai fadi a jin kunnen dukan mutanen, sai ya shiga Kafarnahum.
2 Now the servant of a certain centurion was dying, due to an illness. And he was very dear to him.
Bawan wani jarumi, wanda yake kauna, ba shi da lafiya har ma ya kusa mutuwa.
3 And when he had heard about Jesus, he sent elders of the Jews to him, petitioning him, so that he would come and heal his servant.
Amma da ya ji labarin Yesu, jarumin ya aiki wadansu dattawan Yahudawa, ya ce a roki Yesu ya zo ya ceci bawansa daga mutuwa.
4 And when they had come to Jesus, they petitioned him anxiously, saying to him: “He is worthy that you should provide this to him.
Sa'adda su ka zo kusa da Yesu, su ka roke shi da gaske, cewa, “Wannan ya isa ka yi masa haka,
5 For he loves our nation, and he has built a synagogue for us.”
saboda shi mai kaunar kasar mu ne, kuma shi ne ya gina mana majami'a.
6 Then Jesus went with them. And when he was now not far from the house, the centurion sent friends to him, saying: “Lord, do not trouble yourself. For I am not worthy that you should enter under my roof.
Sai Yesu ya tafi tare da su. Amma sa'adda ya zo kusa da gidan mutumin, jarumin ya aiki abokansa su ka ce da shi, “Ubangiji kada ka damu domin ni ban isa ka zo gida na ba.
7 Because of this, I also did not consider myself worthy to come to you. But say the word, and my servant shall be healed.
Shi ya sa na ga ban isa in zo wurinka ba, ka yi magana kadai bawa na kuwa zai warke.
8 For I also am a man placed under authority, having soldiers under me. And I say to one, ‘Go,’ and he goes; and to another, ‘Come,’ and he comes; and to my servant, ‘Do this,’ and he does it.”
Gama ni ma mutum ne mai iko, ina da sojoji karkashina. Ina iya cewa da wannan, 'Ka je' sai ya tafi, in kuma ce da wani 'ka zo' sai ya zo, in kuma ce da bawa na, 'Yi kaza,' sai ya yi.”
9 And upon hearing this, Jesus was amazed. And turning to the multitude following him, he said, “Amen I say to you, not even in Israel have I found such great faith.”
Sa'adda Yesu ya ji haka, ya yi mamakin mutumin, ya juya wajen taron da su ke biye da shi, ya ce, “Na gaya maku, ko a cikin Isra'ila ban sami wani mai bangaskiya irin wannan ba”
10 And those who had been sent, upon returning to the house, found that the servant, who had been sick, was now healthy.
Daga nan wadanda a ka aika, suka dawo gida suka tarar da bawan cikin koshin lafiya.
11 And it happened afterwards that he went to a city, which is called Nain. And his disciples, and an abundant crowd, went with him.
Wani lokaci bayan wannan, ya zama Yesu yana tafiya wani gari da ake kira Na'im. Almajiransa su na tare da shi, da kuma taron mutane masu yawa.
12 Then, when he had drawn near to the gate of the city, behold, a deceased person was being carried out, the only son of his mother, and she was a widow. And a large crowd from the city was with her.
Sa'adda ya kusa da kofar garin, sai ga wani matacce ana dauke da shi. Kuma shi kadai ne da a wurin mahaifiyarsa. Ita kuwa gwauruwa ce, mutane da dama daga cikin gari suna tare da ita.
13 And when the Lord had seen her, being moved by mercy over her, he said to her, “Do not weep.”
Da ganin ta, sai Ubangiji ya cika da tausayi a game da ita ya ce da ita, “Kada ki yi kuka.”
14 And he drew near and touched the coffin. Then those who carried it stood still. And he said, “Young man, I say to you, arise.”
Sai ya zo ya taba makarar, sai masu dauke da shi su ka tsaya. Ya ce 'Saurayi na ce ma ka ka tashi.”
15 And the dead youth sat up and began to speak. And he gave him to his mother.
Sai mataccen ya tashi ya fara yin magana. Sai Yesu ya ba mahaifiyar danta.
16 Then fear fell over all of them. And they magnified God, saying: “For a great prophet has risen up among us,” and, “For God has visited his people.”
Sai tsoro ya kama su duka. Su ka kama yabon Allah, su na cewa, “An ta da wani annabi mai girma a cikinmu” kuma “Allah ya dubi mutanensa.”
17 And this word about him went out to all of Judea and to the entire surrounding region.
Wannan labari na Yesu, ya ba zu a cikin dukan Yahudiya da yankuna da su ke kewaye.
18 And the disciples of John reported to him concerning all these things.
Almajiran Yahaya suka gaya masa dukan wadannan abubuwa.
19 And John called two of his disciples, and he sent them to Jesus, saying, “Are you he who is to come, or should we wait for another?”
Sai Yahaya ya kira biyu daga cikin almajiransa, ya aike su wurin Ubangiji, suka ce da shi, “Kai ne mai zuwan nan, ko akwai wani wanda za mu saurari zuwansa?”
20 But when the men had come to him, they said: “John the Baptist has sent us to you, saying: ‘Are you he who is to come, or should we wait for another?’”
Sa'adda suka zo kusa da Yesu, sai mutanen suka ce, “Yahaya Mai Baftisma, ya aiko mu, mu tambaya, “Kai ne mai zuwan nan, ko akwai wani wanda za mu saurari zuwansa?”
21 Now in that same hour, he cured many of their diseases and wounds and evil spirits; and to many of the blind, he gave sight.
A cikin wannan lokaci, ya warkar da mutane da yawa daga cututtuka da matsaloli da miyagun ruhohi. Makafi da yawa sun sami ganin gari.
22 And responding, he said to them: “Go and report to John what you have heard and seen: that the blind see, the lame walk, the lepers are cleansed, the deaf hear, the dead rise again, the poor are evangelized.
Yesu, ya amsa ya ce masu, “Bayan kun tafi, ku ba Yohanna rahoton abin da ku ka ji da abin da ku ka gani. Makafi suna ganin gari, guragu suna tafiya, ana kuma tsarkake kutare. Kurame suna ji, ana tayar da matattu, ana gaya wa matalauta labari mai dadi.
23 And blessed is anyone who has not taken offense at me.”
Mai albarka ne mutumin da ya tsaya a kan ba da gaskiya gare ni saboda ayukan da na ke yi.”
24 And when the messengers of John had withdrawn, he began to speak about John to the crowds. “What did you go out to the desert to see? A reed shaken by the wind?
Bayan da mutanen da Yahaya ya aiko suka tafi, Yesu ya fara yi wa taron magana game da Yahaya. “Me ku ka tafi ku gani a cikin hamada, ciyawa wadda iska ta ke girgizawa?
25 Then what did you go out to see? A man clothed in soft garments? Behold, those who are in costly apparel and finery are in the houses of kings.
Amma me ku ka tafi domin ku gani, mutum mai saye da tufafi masu taushi? Duba mutanen da su ke saye da tufafi masu daraja, kuma suna rayuwa cikin jin dadi suna fadar sarakuna.
26 Then what did you go out to see? A prophet? Certainly, I tell you, and more than a prophet.
Amma me ku ka tafi domin ku gani, annabi ne? I, ina gaya ma ku, ya ma fi annabi.
27 This is he of whom it is written: “Behold, I send my Angel before your face, who shall prepare your way before you.”
Wannan shine wanda aka rubuta a kansa, “Duba, ina aika manzo na a gabanka, wanda za ya shirya maka hanya a gabanka.
28 For I say to you, among those born of women, no one is greater than the prophet John the Baptist. But he who is least in the kingdom of God is greater than he.”
Ina gaya maku, a cikin wadanda mata suka haifa, ba wanda ya fi Yahaya girma. Duk da haka, wanda ya fi kankanta a mulkin Allah, ya fi shi girma.
29 And upon hearing this, all the people and the tax collectors justified God, by being baptized with the baptism of John.
Sa'anda dukan mutane suka ji haka, har da ma su karbar haraji, suka shaida Allah mai adalci ne. Su na cikin wadanda Yahaya ya yi wa baftisma.
30 But the Pharisees and the experts in the law despised the counsel of God concerning themselves, by not being baptized by him.
Amma Farisawa da wadanda su ke kwararru a cikin shari'ar Yahudawa, wadanda ba shi ne ya yi masu baftisma ba, suka yi watsi da hikimar Allah don kansu.
31 Then the Lord said: “Therefore, to what shall I compare the men of this generation? And to what are they similar?
Sa'annan Yesu ya ce, “Da me zan kamanta mutanen wannan zamani? Da me suka yi kama?
32 They are like children sitting in the marketplace, talking with one another, and saying: ‘We sang to you, and you did not dance. We lamented, and you did not weep.’
Suna kama da yaran da suke wasa a kasuwa, wadanda suke magana da junansu suna cewa, “Mun yi maku busa, ba ku yi rawa ba. Mun yi makoki, ba ku yi kuka ba.”
33 For John the Baptist came, neither eating bread nor drinking wine, and you say, ‘He has a demon.’
Haka, Yahaya ya zo, bai ci gurasa ba, bai sha ruwan inabi ba, amma ku ka ce, 'Aljani ne yake mulkinsa.
34 The Son of man came, eating and drinking, and you say, ‘Behold, a voracious man and a drinker of wine, a friend of tax collectors and of sinners.’
Dan Mutum, ya zo, yana ci, yana sha, amma, kuka ki shi, kuna cewa dubi mutum mai hadama, mai shan ruwan inabi da yawa, abokin masu karbar haraji da masu zunubi!
35 But wisdom is justified by all her children.”
Amma hikimar Allah tana shaidar dukan 'yayanta.”
36 Then certain Pharisees petitioned him, so that they might eat with him. And he went into the house of the Pharisee, and he reclined at table.
Wata rana wani Bafarise, ya roki Yesu ya je ya ci abinci tare da shi. Bayan da Yesu ya shiga gidan Bafarisen, ya zauna a teburi domin ya ci abinci.
37 And behold, a woman who was in the city, a sinner, found out that he was reclining at table in the house of the Pharisee, so she brought an alabaster container of ointment.
Sai ga wata mace mai zunubi, ta fito daga cikin birni. Sa'anda ta ji labari Yesu yana gidan Bafarisen, domin ya ci abinci. Ta dauki tandun mai na alabastar mai kamshi.
38 And standing behind him, beside his feet, she began to wash his feet with tears, and she wiped them with the hair of her head, and she kissed his feet, and she anointed them with ointment.
Ta tsaya kusa da Yesu tana kuka. Ta fara jika kafafunsa da hawayenta, tana shafe kafafunsa da gashin kanta. Tana yi wa kafafunsa sumba, tana shafe su da turare.
39 Then the Pharisee, who had invited him, upon seeing this, spoke within himself, saying, “This man, if he were a prophet, would certainly know who and what kind of woman is this, who is touching him: that she is a sinner.”
Sa'anda Bafarisen da ya gaiyaci Yesu, ya ga haka, sai ya yi tunani a cikin ransa, da cewa, “In da wannan mutum annabi ne, da ya gane ko wacce irin mace ce, wannan da take taba shi, ita mai zunubi ce.”
40 And in response, Jesus said to him, “Simon, I have something to say to you.” So he said, “Speak, Teacher.”
Yesu ya amsa ya ce masa, “Siman, ina so in gaya maka wani abu.” Ya ce, “malam sai ka fadi!”
41 “A certain creditor had two debtors: one owed five hundred denarii, and the other fifty.
Yesu ya ce, “wani mutum mai ba da bashi yana bin wadansu mutane su biyu kudi, yana bin dayan sule dari, dayan kuma yana bin sa sule hamsin.
42 And since they did not have the ability to repay him, he forgave them both. So then, which of them loves him more?”
Da yake ba su da kudin da za su iya biyan sa, sai ya yafe masu, su duka biyu. A cikin su biyu, wanne ne zai fi nuna kauna ga wannan mutum?”
43 In response, Simon said, “I suppose that it is he to whom he forgave the most.” And he said to him, “You have judged correctly.”
Siman ya amsa ya ce, “Ina tsammani wanda ya yafe wa kudi da yawa.” Yesu ya amsa ya ce masa, “Ka shari'anta dai dai.”
44 And turning to the woman, he said to Simon: “Do you see this woman? I entered into your house. You gave me no water for my feet. But she has washed my feet with tears, and has wiped them with her hair.
Yesu ya juya wajen matar, ya ce da Siman, “Ka ga matan nan. Na shiga gidanka. Ba ka ba ni ruwa domin kafafuna ba, amma ita ta ba ni, da hawayenta ta wanke kafafuna, ta kuma shafe su da gashin kanta.
45 You gave no kiss to me. But she, from the time that she entered, has not ceased to kiss my feet.
Kai ba ka yi ma ni sumba ba, amma ita ta yi, tun sa'adda na shigo nan ba ta dena sumbatar kafafuna ba.
46 You did not anoint my head with oil. But she has anointed my feet with ointment.
Kai ba ka shafe kai na da mai ba, amma ita ta shafe kafafuna da turare.
47 Because of this, I tell you: many sins are forgiven her, because she has loved much. But he who is forgiven less, loves less.”
Saboda haka, ita wadda ta ke da zunubi da yawa ta bayar da mai yawa, ta kuma nuna kauna mai yawa. Amma shi wanda aka gafarta wa kadan, ya kuma nuna kauna kadan.”
48 Then he said to her, “Your sins are forgiven you.”
Daga nan sai ya ce mata, “An gafarta zunubanki.”
49 And those who sat at table with him began to say within themselves, “Who is this, who even forgives sins?”
Wadanda su ke a nan zaune tare da shi suka fara magana da junansu, “Wanene wannan wanda har yake gafarta zunubai?
50 Then he said to the woman: “Your faith has brought you salvation. Go in peace.”
Sai Yesu ya ce da matar, “Bangaskiyarki ta cece ki. Ki tafi da salama.”