< Luke 22 >

1 Now the days of the Feast of Unleavened Bread, which is called Passover, were approaching.
Anan nan idin gurasa mara yisti ya yi kusa, wanda a ke kira Idin ketarewa.
2 And the leaders of the priests, and the scribes, were seeking a way to execute Jesus. Yet truly, they were afraid of the people.
Manyan firistoci da marubuta suka yi shawara yadda za su kashe Yesu, gama suna jin tsoron mutane.
3 Then Satan entered into Judas, who was surnamed Iscariot, one of the twelve.
Shaidan ya shiga Yahuza Iskariyoti, daya daga cikin goma sha biyun.
4 And he went out and was speaking with the leaders of the priests, and the magistrates, as to how he might hand him over to them.
Yahuza ya je ya yi shawara da manyan firistoci da Jarumawa yadda zai ba da Yesu a garesu.
5 And they were glad, and so they made an agreement to give him money.
Suka yi farin ciki, suka yarda su ba shi kudi.
6 And he made a promise. And he was seeking an opportunity to hand him over, apart from the crowds.
Sai ya yarda, sai ya nimi dama yadda zai ba da shi garesu a lokacin da babu taro.
7 Then the day of Unleavened Bread arrived, on which it was necessary to kill the Pascal lamb.
Ranar idin gurasa mara yisti ya yi, da dole za a yi hadayan rago na Idin ketarewa.
8 And he sent Peter and John, saying, “Go out, and prepare the Passover for us, so that we may eat.”
Yesu ya aiki Bitrus da Yahaya, ya ce masu, “Ku je ku shirya mana abincin Idin ketarewa, domin mu ci.”
9 But they said, “Where do you want us to prepare it?”
Suka tambaye shi, “A ina ka ke so mu shirya?”
10 And he said to them: “Behold, as you are entering into the city, a certain man will meet you, carrying a pitcher of water. Follow him to the house into which he enters.
Ya amsa masu, “Ku ji, sa'adda ku ka shiga birnin, wani mutum mai dauke da tulun ruwa zai same ku. Ku bishi zuwa cikin gidan da za ya shiga.
11 And you shall say to the father of the household: ‘The Teacher says to you: Where is the guestroom, where I may eat the Passover with my disciples?’
Sai ku gaya wa mai gidan, 'Malam ya ce, “Ina dakin baki, inda zan ci abincin Idin ketarewa da almajirai na?'”
12 And he will show you a large cenacle, fully furnished. And so, prepare it there.”
Zai nuna maku babban bene wanda yake a shirye. Ku shirya a can.”
13 And going out, they found it to be just as he had told them. And they prepared the Passover.
Sai suka tafi, suka sami komai kamar yadda ya gaya masu. Sai suka shirya abincin Idin ketarewan.
14 And when the hour had arrived, he sat down at table, and the twelve Apostles with him.
Sa'adda lokacin ya yi, ya zauna da almajiran.
15 And he said to them: “With longing have I desired to eat this Passover with you, before I suffer.
Sai ya ce masu, “Ina da marmari matuka in ci wannan abincin Idin ketarewa da ku kamin in sha wahala.
16 For I say to you, that from this time, I will not eat it, until it is fulfilled in the kingdom of God.”
Gama na ce maku, ba zan ci shi kuma ba, sai dai an cika shi a mulkin Allah.”
17 And having taken the chalice, he gave thanks, and he said: “Take this and share it among yourselves.
Sai Yesu ya dauki koko, sa'adda ya yi godiya, sai yace, “Karba wannan, ku rarraba a tsakaninku.
18 For I say to you, that I will not drink from the fruit of the vine, until the kingdom of God arrives.”
Gama ina ce maku, ba zan sha wannan ruwan inabi kuma ba, sai dai mulkin Allah ya zo.”
19 And taking bread, he gave thanks and broke it and gave it to them, saying: “This is my body, which is given for you. Do this as a commemoration of me.”
Sai ya dauki gurasa, sa'adda ya yi godiya, ya kakkarya shi, sai ya ba su, cewa, “Wannan jikina ne wanda aka bayar dominku. Ku yi wannan domin tunawa da ni.”
20 Similarly also, he took the chalice, after he had eaten the meal, saying: “This chalice is the new covenant in my blood, which will be shed for you.
Sai ya dauki kokon kuma bayan jibi, cewa, “Wannan koko sabon alkawari ne cikin jinina, wanda aka zubar dominku.
21 But in truth, behold, the hand of my betrayer is with me at table.
Amma ku yi lura. Wanda zai bashe ni yana tare da ni a teburi.
22 And indeed, the Son of man goes according to what has been determined. And yet, woe to that man by whom he will be betrayed.”
Gama Dan Mutum zai tafi lallai kamar yadda aka kaddara. Amma kaiton wannan mutum da shine za ya bashe shi!”
23 And they began to inquire among themselves, as to which of them might do this.
Sai suka fara tambaya a tsakaninsu, wanene a cikinmu da zai yi wannan abu.
24 Now there was also a contention among them, as to which of them seemed to be the greater.
Sai gardama ta tashi a tsakaninsu game da wanene mafi girma.
25 And he said to them: “The kings of the Gentiles dominate them; and those who hold authority over them are called beneficent.
Ya ce masu, “Sarakunan al'ummai suna nuna iko akansu, kuma wadanda suke da iko a kansu ana ce da su masu mulki da daraja.
26 But it must not be so with you. Instead, whoever is greater among you, let him become the lesser. And whoever is the leader, let him become the server.
Amma kada ya zama haka da ku. A maimakon haka, bari wanda ya ke mafi girma a cikinku ya zama mafi kankanta. Bari wanda yafi muhimmanci kuma ya zama kamar mai hidima.
27 For who is greater: he who sits at table, or he who serves? Is not he who sits at table? Yet I am in your midst as one who serves.
Gama wanene yafi girma, wanda ya zauna a teburi, ko kuwa wanda yake yin hidima? Ba wanda ya zauna a teburi ba? Duk da haka ina kamar mai hidima a tsakaninku.
28 But you are those who have remained with me during my trials.
Amma ku ne wadanda ku ke tare da ni a cikin jarabobina.
29 And I dispose to you, just as my Father has disposed to me, a kingdom,
Na baku mulki, kamar yadda Ubana ya ba ni mulki,
30 so that you may eat and drink at my table in my kingdom, and so that you may sit upon thrones, judging the twelve tribes of Israel.”
domin ku ci ku kuma sha a teburi na mulkina. Za ku zauna a kan kursiyai kuna shari'anta kabilun nan goma sha biyu na Israila.
31 And the Lord said: “Simon, Simon! Behold, Satan has asked for you, so that he may sift you like wheat.
Siman, Siman, ka yi hankali, shaidan ya nemi izini a bada kai domin ya tankade ka kamar alkama.
32 But I have prayed for you, so that your faith may not fail, and so that you, once converted, may confirm your brothers.”
Amma na yi maka addu'a, saboda kada bangaskiyarka ta fadi. Bayan da ka juyo kuma, ka karfafa 'yan'uwanka.”
33 And he said to him, “Lord, I am prepared to go with you, even to prison and to death.”
Bitrus ya ce masa, “Ubangiji, ina shirye in tafi tare da kai zuwa cikin kurkuku da zuwa mutuwa.”
34 And he said, “I say to you, Peter, the rooster will not crow this day, until you have three times denied that you know me.” And he said to them,
Yesu ya amsa masa, “Ina gaya maka, Bitrus, kamin caran zakara a yau, za ka yi musu na sau uku cewa ba ka sanni ba.”
35 “When I sent you without money or provisions or shoes, did you lack anything?”
Sa'annan Yesu ya ce masu, “Lokacin da na aike ku babu jaka, ko burgami ko takalma, ko kun rasa wani abu? Sai suka amsa, “Babu.”
36 And they said, “Nothing.” Then he said to them: “But now, let whoever has money take it, and likewise with provisions. And whoever does not have these, let him sell his coat and buy a sword.
Ya kuma ce masu, “Amma yanzu, wanda ya ke da jaka, bari ya dauka, da kuma burgami. Wanda ba shi da takobi sai ya sayar da taguwarsa ya sayi guda.
37 For I say to you, that what has been written must still be fulfilled in me: ‘And he was esteemed with the wicked.’ Yet even these things about me have an end.”
Gama ina ce maku, abin da aka rubuta game da ni dole sai ya cika, 'An lisafta shi kamar daya daga cikin masu karya doka.' Gama abinda aka fada akaina ya cika.”
38 So they said, “Lord, behold, there are two swords here.” But he said to them, “It is sufficient.”
Sai suka ce, “Ubangiji, duba! Ga takuba biyu.” Sai ya ce masu, “Ya isa.”
39 And departing, he went out, according to his custom, to the Mount of Olives. And his disciples also followed him.
Bayan cin abincin yamma, Yesu ya tafi, kamar yadda ya saba yi, zuwa dutsen Zaitun, sai almajiran suka bi shi.
40 And when he had arrived at the place, he said to them: “Pray, lest you enter into temptation.”
Sa'adda suka iso, ya ce masu, “Ku yi addu'a domin kada ku shiga cikin jaraba.”
41 And he was separated from them by about a stone’s throw. And kneeling down, he prayed,
Ya rabu da su misalin nisan jifa, sai ya durkusa kasa ya yi addu'a,
42 saying: “Father, if you are willing, take this chalice away from me. Yet truly, let not my will, but yours, be done.”
yana cewa “Uba, in ka yarda, ka dauke wannan kokon daga gareni. Ko da yake ba nufina ba, amma bari naka nufin ya kasance.”
43 Then an Angel appeared to him from heaven, strengthening him. And being in agony, he prayed more intensely;
Sai mala'ika daga sama ya bayyana a wurinsa, yana karfafa shi.
44 and so his sweat became like drops of blood, running down to the ground.
Yana cikin wahala sosai, sai ya dukufa cikin addu'a, har zufarsa kuma tana diga a kasa kamar gudajen jini.
45 And when he had risen up from prayer and had gone to his disciples, he found them sleeping out of sorrow.
Sa'adda ya tashi daga addu'arsa, sai ya zo wurin almajiran, ya same su suna barci domin bakin cikinsu,
46 And he said to them: “Why are you sleeping? Rise up, pray, lest you enter into temptation.”
sai ya tambaye su, “Don me kuke barci? Tashi ku yi addu'a, saboda kada ku shiga cikin jaraba.”
47 While he was still speaking, behold, a crowd arrived. And he who is called Judas, one of the twelve, went ahead of them and approached Jesus, in order to kiss him.
Sa'adda yana cikin magana, sai, ga taron jama'a suka bayana, tare da Yahuza, daya daga cikin sha biyun, ya na jagabansu. Sai ya zo kusa da Yesu domin ya yi masa sumba,
48 And Jesus said to him, “Judas, do you betray the Son of man with a kiss?”
amma Yesu ya ce masa, “Yahuza, za ka ba da Dan Mutum da sumba?”
49 Then those who were around him, realizing what was about to happen, said to him: “Lord, shall we strike with the sword?”
Sa'adda wadanda suke kewaye da Yesu suka ga abin da yake faruwa, sai suka ce, “Ubangiji, mu yi sara da takobi ne?”
50 And one of them struck the servant of the high priest and cut off his right ear.
Sai daya daga cikinsu ya kai wa bawan babban firist sara a kunne, sai ya yanke masa kunnensa na dama.
51 But in response, Jesus said, “Permit even this.” And when he had touched his ear, he healed him.
Yesu ya ce, “Ya isa haka.” Sai ya taba kunnensa, sai ya warkar da shi.
52 Then Jesus said to the leaders of the priests, and the magistrates of the temple, and the elders, who had come to him: “Have you gone out, as if against a thief, with swords and clubs?
Yesu yace wa manyan firistoci, da masu tsaron haikali, da dattawa wadanda suke gaba da shi, “Kun fito kamar za ku kama dan fashi, da takuba da sanduna?
53 When I was with you each day in the temple, you did not extend your hands against me. But this is your hour and that of the power of darkness.”
Sa'adda nake tare da ku kowace rana a haikali, ba ku kama ni ba. Amma wannan shine lokacinku, da kuma ikon duhu.”
54 And apprehending him, they led him to the house of the high priest. Yet truly, Peter followed at a distance.
Suka kama shi, sai suka tafi da shi, suka kawo shi cikin gidan babban firist. Amma Bitrus yana binsa daga nesa.
55 Now as they were sitting around a fire, which had been kindled in the middle of the atrium, Peter was in their midst.
Bayan da suka hura wuta a tsakiyar gidan da suka zazzauna tare, Bitrus ya zaune a tsakaninsu.
56 And when a certain woman servant had seen him sitting in its light, and had looked at him intently, she said, “This one was also with him.”
Sai wata baranya ta ganshi ya zauna a hasken wuta, sai ta zura masa ido ta ce, “Wannan mutum ma yana tare da shi.”
57 But he denied him by saying, “Woman, I do not know him.”
Amma Bitrus ya yi musu, yana cewa, “Mace, ban san shi ba.”
58 And after a little while, another one, seeing him, said, “You also are one of them.” Yet Peter said, “O man, I am not.”
Bayan dan karamin lokaci sai wani mutum ya gan shi, sai ya ce, “Kaima kana daya daga cikinsu.” Amma Bitrus ya ce, “Mutumin, ba ni ba ne.”
59 And after the interval of about one hour had passed, someone else affirmed it, saying: “Truly, this one also was with him. For he is also a Galilean.”
Bayan sa'a daya sai wani mutum ya nace da cewa, “Gaskiya wannan mutum yana tare da shi, gama shi dan Galili ne.”
60 And Peter said: “Man, I do not know what you are saying.” And at once, while he was still speaking, the rooster crowed.
Amma Bitrus ya ce, “Mutumin, ban san abin da kake fada ba.” Sai nan da nan, da yana cikin magana, sai zakara ta yi cara.
61 And the Lord turned around and looked at Peter. And Peter remembered the word of the Lord that he had said: “For before the rooster crows, you will deny me three times.”
Yana juyawa, sai Ubangiji ya dubi Bitrus. Sai Bitrus ya tuna kalmar Ubangiji, sa'adda ya ce masa, “Kafin zakara ya yi cara yau za ka musunce ni sau uku.”
62 And going out, Peter wept bitterly.
Da fitowarsa waje, Bitrus ya yi kuka mai zafi.
63 And the men who were holding him ridiculed him and beat him.
Sai mutanen da ke tsare da Yesu suka yi masa ba'a da bulala kuma.
64 And they blindfolded him and repeatedly struck his face. And they questioned him, saying: “Prophesy! Who is it that struck you?”
Bayan da suka rufe masa idanu, suka tambaye shi, cewa, “Ka yi annabci! Wa ya buge ka?”
65 And blaspheming in many other ways, they spoke against him.
Suka yi wadansu miyagun maganganu na sabo game da Yesu.
66 And when it was daytime, the elders of the people, and the leaders of the priests, and the scribes convened. And they led him into their council, saying, “If you are the Christ, tell us.”
Da gari ya waye, sai dattawa suka hadu tare, da manyan firistoci da marubuta. Sai suka kai shi cikin majalisa
67 And he said to them: “If I tell you, you will not believe me.
suka ce, “Gaya mana, in kai ne Almasihu.” Amma yace masu, “Idan na gaya maku, ba za ku gaskanta ba,
68 And if I also question you, you will not answer me. Neither will you release me.
idan na yi maku tambaya, ba za ku amsa ba.
69 But from this time, the Son of man will be sitting at the right hand of the power of God.”
Amma nan gaba, Dan Mutum zai zauna a hannun dama na ikon Allah.”
70 Then they all said, “So you are the Son of God?” And he said. “You are saying that I am.”
Suka ce masa, “Ashe kai Dan Allah ne?” Sai Yesu ya ce masu, “Haka kuka ce, nine.”
71 And they said: “Why do we still require testimony? For we have heard it ourselves, from his own mouth.”
Suka ce, “Don me muke neman shaida? Gama mu da kanmu munji daga bakinsa.”

< Luke 22 >