< Luke 20 >
1 And it happened that, on one of the days when he was teaching the people in the temple and preaching the Gospel, the leaders of the priests, and the scribes, gathered together with the elders,
Wata rana da Yesu yana koyar da mutane, yana musu wa’azin bishara a filin haikalin, sai manyan firistoci da malaman dokoki, tare da dattawan suka zo wurinsa.
2 and they spoke to him, saying: “Tell us, by what authority do you do these things? Or, who is it that has given you this authority?”
Suka ce masa, “Gaya mana, da wane iko kake yin waɗannan abubuwa. Wa ya ba ka wannan ikon?”
3 And in response, Jesus said to them: “I will also question you about one word. Respond to me:
Ya amsa ya ce, “Ni ma zan yi muku wata tambaya. Ku faɗa mini,
4 The baptism of John, was it from heaven, or of men?”
baftismar Yohanna, daga sama ne ta fito, ko kuwa daga wurin mutane ne?”
5 So they discussed it among themselves, saying: “If we say, ‘From heaven,’ he will say, ‘Then why did you not believe him?’
Sai suka yi shawara da junansu, suka ce, “In muka ce, ‘Daga sama ne,’ zai tambaya, ‘To, don me ba ku gaskata shi ba?’
6 But if we say, ‘Of men,’ the whole people will stone us. For they are certain that John was a prophet.”
Amma in kuma muka ce, ‘Daga mutane ne,’ dukan mutanen za su jajjefe mu da duwatsu, domin sun tabbata cewa, Yohanna annabi ne.”
7 And so they responded that they did not know where it was from.
Don haka, sai suka amsa cewa, “Ba mu san inda ta fito ba.”
8 And Jesus said to them, “Neither will I tell you by what authority I do these things.”
Yesu ya ce, “To, ni ma ba zan gaya muku, ko da wane iko ne, nake yin waɗannan abubuwa ba.”
9 Then he began to tell the people this parable: “A man planted a vineyard, and he loaned it to settlers, and he was on a sojourn for a long time.
Sai ya ci gaba da gaya wa mutanen wannan misali ya ce, “Wani mutum ya yi gonar inabi, sai ya ba da hayarta ga waɗansu manoma, sa’an nan ya yi wata doguwar tafiya.
10 And in due time, he sent a servant to the farmers, so that they would give to him from the fruit of the vineyard. And they beat him and drove him away, empty-handed.
A lokacin girbi, sai ya aiki bawa zuwa wurin masu hayan, don su ba shi daga cikin’ya’yan inabin. Amma’yan hayan suka yi wa bawan nan dūka, suka kore shi hannu wofi.
11 And he continued to send another servant. But beating him and treating him with contempt, they likewise sent him away, empty-handed.
Ya sāke aikan wani bawa, shi ma suka yi masa dūka, suka kunyata shi, suka kuma kore shi hannu wofi.
12 And he continued to send a third. And wounding him also, they drove him away.
Har yanzu, ya sāke aikan na uku, amma suka ji masa rauni, suka jefar da shi waje.
13 Then the lord of the vineyard said: ‘What shall I do? I will send my beloved son. Perhaps when they have seen him, they will respect him.’
“Sai mai gonar inabin ya ce, ‘Me zan yi? Zan aiki ɗana da nake ƙauna, wataƙila za su girmama shi.’
14 And when the settlers had seen him, they discussed it among themselves, saying: ‘This one is the heir. Let us kill him, so that the inheritance will be ours.’
“Amma da’yan hayan suka gan shi, sai suka tattauna zancen, suka ce, ‘Wannan shi ne magājin, mu kashe shi sa’an nan gādon zai zama namu!’
15 And forcing him outside of the vineyard, they killed him. What, then, will the lord of the vineyard do to them?”
Sai suka fitar da shi waje, suka kashe shi. “To, me mai gonar inabin zai yi da su?
16 “He will come and destroy those settlers, and he will give the vineyard to others.” And upon hearing this, they said to him, “Let it not be.”
Zai zo ya karkashe masu hayan nan, ya ba wa waɗansu gonar inabin.” Da mutanen suka ji wannan, sai suka ce, “Allah ya sawwaƙa!”
17 Then, gazing at them, he said: “Then what does this mean, which is written: ‘The stone which the builders have rejected, the same has become the head of the corner?’
Yesu ya zura musu ido ya ce, “To, mene ne ma’anar abin da aka rubuta cewa, “‘Dutsen da magina suka ƙi, shi ne kuwa ya zama dutsen kan ginin’
18 Everyone who falls on that stone will be shattered. And anyone upon whom it falls will be crushed.”
Duk wanda ya fāɗi a kan dutsen nan, zai kakkarye. Kuma in dutsen nan ya fāɗi a kan wani, zai murƙushe shi.”
19 And the leaders of the priests, and the scribes, were seeking to lay hands on him in that same hour, but they feared the people. For they realized that he had spoken this parable about them.
Malaman dokoki da manyan firistoci, suka nemi hanyar kama shi nan da nan, domin sun san cewa, ya yi wannan misali a kansu ne, amma suna jin tsoron mutane.
20 And being attentive, they sent traitors, who would pretend that they were just, so that they might catch him in his words and then hand him over to the power and authority of the procurator.
Sai suka sa masa ido, suka aiki’yan leƙen asiri, waɗanda suka nuna kamar su masu gaskiya ne, suna nufin su kama shi game da abin da zai faɗa, domin su ba da shi ga gwamna mai mulki, da mai iko.
21 And they questioned him, saying: “Teacher, we know that you speak and teach correctly, and that you do not consider anyone’s status, but you teach the way of God in truth.
Sai’yan leƙen asirin suka tambaye shi, suka ce, “Malam, mun sani kana faɗin, kuma kana koyar da abin da yake daidai, ba ka kuma nuna bambanci, amma kana koyar da hanyar Allah bisa ga gaskiya.
22 Is it lawful for us to pay the tribute to Caesar, or not?”
Daidai ne mu biya haraji ga Kaisar, ko babu?”
23 But realizing their deceitfulness, he said to them: “Why do you test me?
Ya gane makircinsu, sai ya ce musu,
24 Show me a denarius. Whose image and inscription does it have?” In response, they said to him, “Caesar’s.”
“Nuna mini dinari. Hoton wane ne, kuma rubutun wane ne a kai?” Suka amsa, “Na Kaisar.”
25 And so, he said to them: “Then repay the things that are Caesar’s, to Caesar, and the things that are God’s, to God.”
Sai ya ce musu, “Ku ba wa Kaisar abin da yake na Kaisar, ku kuma ba wa Allah abin da yake na Allah.”
26 And they were not able to contradict his word before the people. And being amazed at his answer, they were silent.
Ba su iya kama shi a kan abin da ya faɗa a fili ba. Amsarsa ya ba su mamaki, shi ya sa suka yi shiru.
27 Now some of the Sadducees, who deny that there is a resurrection, approached him. And they questioned him,
Waɗansu Sadukiyawa da suke cewa, ba tashin matattu, suka zo wurin Yesu da tambaya cewa,
28 saying: “Teacher, Moses wrote for us: If any man’s brother will have died, having a wife, and if he does not have any children, then his brother should take her as his wife, and he should raise up offspring for his brother.
“Malam, Musa ya rubuta mana cewa, ‘In ɗan’uwan wani mutum ya mutu, ya bar mata amma ba’ya’ya, dole mutumin ya aure gwauruwar, ya samo wa ɗan’uwansa’ya’ya.’
29 And so there were seven brothers. And the first took a wife, and he died without sons.
To, an yi waɗansu’yan’uwa bakwai. Na fari ya auri wata mace, ya mutu ba’ya’ya.
30 And the next one married her, and he also died without a son.
Na biyun,
31 And the third married her, and similarly all seven, and none of them left behind any offspring, and they each died.
da na ukun suka aure ta. Haka nan dukansu bakwai suka mutu babu’ya’ya.
32 Last of all, the woman also died.
A ƙarshe, ita macen ma ta mutu.
33 In the resurrection, then, whose wife will she be? For certainly all seven had her as a wife.”
Shin, a tashin matattu, matar wa za tă zama? Tun da su bakwan nan, sun aure ta.”
34 And so, Jesus said to them: “The children of this age marry and are given in marriage. (aiōn )
Yesu ya amsa ya ce, “Mutanen zamanin nan suna aure, suna kuma ba da aure, (aiōn )
35 Yet truly, those who shall be held worthy of that age, and of the resurrection from the dead, will neither be married, nor take wives. (aiōn )
amma su waɗanda aka ga sun cancantar kasancewa a zamanin can, da kuma na tashin matattu, ba za su yi aure, ko su ba da aure ba. (aiōn )
36 For they can no longer die. For they are equal to the Angels, and they are children of God, since they are children of the resurrection.
Kuma ba za su sāke mutuwa ba, gama su kamar mala’iku ne. Su’ya’yan Allah ne, tun da su’ya’yan tashin matattu ne.
37 For in truth, the dead do rise again, as Moses also showed beside the bush, when he called the Lord: ‘The God of Abraham, and the God of Isaac, and the God of Jacob.’
Amma bisa ga labari na bishiya nan, mai cin wuta da Musa ya gani a jeji, ko Musa ma, ya nuna cewa, matattu suna tashi. Gama ya kira Ubangiji, ‘Allah na Ibrahim, da Allah na Ishaku, da kuma Allah na Yaƙub.’
38 And so he is not the God of the dead, but of the living. For all are alive to him.”
Shi ba Allah na matattu ba ne, amma na masu rai ne, gama a gare shi, duka na da rai.”
39 Then some of the scribes, in response, said to him, “Teacher, you have spoken well.”
Sai waɗansu malaman dokoki suka amsa suka ce, “Ka faɗi daidai, malam!”
40 And they no longer dared to question him about anything.
Kuma ba wanda ya sami ƙarfin halin yin masa waɗansu tambayoyi.
41 But he said to them: “How can they say that the Christ is the son of David?
Sai Yesu ya ce musu, “Yaya suke cewa, ‘Kiristi ɗan Dawuda ne?’
42 Even David himself says, in the book of Psalms: ‘The Lord said to my Lord, sit at my right hand,
Dawuda da kansa ya faɗa a cikin Zabura, “‘Ubangiji ya ce wa Ubangijina, “Zauna a hannun damana,
43 until I set your enemies as your footstool.’
sai na sa abokan gābanka su zama matashin sawunka.”’
44 Therefore, David calls him Lord. So how can he be his son?”
Dawuda ya kira shi ‘Ubangiji.’ Ta, yaya zai zama ɗansa?”
45 Now in the hearing of all the people, he said to his disciples:
Yayinda dukan mutane suna cikin sauraronsa, sai Yesu ya ce wa almajiransa,
46 “Be cautious of the scribes, who choose to walk in long robes, and who love greetings in the marketplace, and the first chairs in the synagogues, and the first places at table during feasts,
“Ku yi hankali da malaman dokoki. Sukan so sa manyan riguna suna zaga, suna sha’awan karɓan gaisuwa a wuraren kasuwanci, da kuma wuraren zama mafi daraja a majami’u, da wuraren bangirma a bukukkuwa.
47 who devour the houses of widows, feigning long prayers. These will receive the greater damnation.”
Suna mamaye gidajen gwauraye, kuma don burga, suna dogayen addu’o’i. Ga irin waɗannan mutane, za a yi musu hukunci mai tsanani sosai.”