< Luke 12 >

1 Then, as great crowds were standing so close that they were stepping on one another, he began to say to his disciples: “Beware of the leaven of the Pharisees, which is hypocrisy.
Da jimawa kadan, bayan da mutane da yawa suka taru kwarai har suna tattaka junansu. Sai ya fara yin magana da almajiransa. “Ku yi lura da yisti na Farisawa, wanda shine manufunci.
2 For there is nothing covered, which will not be revealed, nor anything hidden, which will not be known.
Amma ba abin da ke rufe wanda ba za a tone ba, ba kuma abin da ke boye wanda ba za a sani ba.
3 For the things that you have spoken in darkness will be declared in the light. And what you have said in the ear in bedrooms will be proclaimed from the housetops.
Saboda haka ba abin da za ku fadi a asirce wanda ba za a ji shi a cikin sarari ba. Abin da ku ka fadi da rada cikin lungu, za a yi shelarsa a ko'ina.
4 So I say to you, my friends: Do not be fearful of those who kill the body, and afterwards have no more that they can do.
Ina gaya maku abokaina, kada ku ji tsoron wanda da za su kashe jiki. Bayan haka kuma ba abin da za su iya yi.
5 But I will reveal to you whom you should fear. Fear him who, after he will have killed, has the power to cast into Hell. So I say to you: Fear him. (Geenna g1067)
Bari in gargade ku a kan wanda za ku ji tsoronsa. Ku ji tsoron shi wanda bayan ya kashe zai iya jefa ku cikin jahannama. I, ina ce maku ku ji tsoronsa. (Geenna g1067)
6 Are not five sparrows sold for two small coins? And yet not one of these is forgotten in the sight of God.
Ba a kan sayar da 'yan tsuntsaye biyar a kan anini biyu ba? Duk da haka, Allah ba zai manta da ko daya daga cikinsu ba.
7 But even the very hairs of your head have all been numbered. Therefore, do not be afraid. You are worth more than many sparrows.
Har ma gashin da ke kan ku ya san yawan su. Kada ku ji tsoro, ku kun fi tsuntsaye daraja a wurinsa.
8 But I say to you: Everyone who will have confessed me before men, the Son of man will also confess him before the Angels of God.
Ina gaya maku, dukan wanda za ya shaida ni a gaban mutane, Dan Mutum kuma za ya shaida shi a gaban mala'kun Allah.
9 But everyone who will have denied me before men, he will be denied before the Angels of God.
Kuma dukan wanda ya ki ni a gaban mutane, za a ki shi a gaban mala'ikun Allah.
10 And everyone who speaks a word against the Son of man, it will be forgiven of him. But of him who will have blasphemed against the Holy Spirit, it will not be forgiven.
Dukan wanda ya yi magana gaba da Dan Mutum, za a gafarta masa. Amma shi wanda ya yi sabon Ruhu Mai Tsarki, ba za a gafarta masa ba.
11 And when they will lead you to the synagogues, and to magistrates and authorities, do not choose to be worried about how or what you will answer, or about what you might say.
Idan suka kawo ku gaban majami'a, ko gaban masu shari'a, ko gaban masu iko, kada ku damu da abin da za ku fada domin ku kare kanku. Ko kuwa abin da za ku ce.
12 For the Holy Spirit will teach you, in the same hour, what you must say.”
Gama Ruhu Mai Tsarki zai koya maku abin da za ku fadi a wannan lokaci.”
13 And someone from the crowd said to him, “Teacher, tell my brother to share the inheritance with me.”
Sai wani a cikin taron ya ce masa, “Malam, ka yi wa dan'uwana magana ya raba gado da ni
14 But he said to him, “Man, who has appointed me as judge or arbitrator over you?”
Yesu ya ce masa, “Kai, wanene ya sa ni in zama alkali, ko matsakanci a kanku?”
15 So he said to them: “Be cautious and wary of all avarice. For a person’s life is not found in the abundance of the things that he possesses.”
Sai kuma ya ce masu, “Ku yi lura kada ku zama masu hadama, gama ba abin da mutum ya mallaka ne ya fi mahimmanci a cikin rayuwar sa ba.”
16 Then he spoke to them using a comparison, saying: “The fertile land of a certain wealthy man produced crops.
Sa'annan Yesu ya fada masu wani misali, ya ce, “Gonar wani mutum ta bada amfani sosai,
17 And he thought within himself, saying: ‘What should I do? For I have nowhere to gather together my crops.’
ya yi tunani, ya ce, 'Me zan yi, domin ba ni da wurin da zan iya ajjiye amfanin gonata?'
18 And he said: ‘This is what I will do. I will tear down my barns and build larger ones. And into these, I will gather all the things that have been grown for me, as well as my goods.
Sai ya ce, na san abin da zan yi. Zan rushe rumbuna na in gina wadansu manya-manya, a nan zan ajjiye hatsi na da dukan abubuwa.
19 And I will say to my soul: Soul, you have many goods, stored up for many years. Relax, eat, drink, and be cheerful.’
Sai in ce da raina, “Ya raina, kana da abu da yawa da aka ajjiye dominka, sai ka huta, ka ci, ka sha, ka yi murna.”
20 But God said to him: ‘Foolish one, this very night they require your soul of you. To whom, then, will those things belong, which you have prepared?’
Amma sai Allah ya ce da shi, 'Wawan mutum, a cikin daren nan ana son ranka daga wurinka. Kayan da ka tara ka shirya wa kanka, na wa za su zama?'
21 So it is with him who stores up for himself, and is not wealthy with God.”
Haka wanda ya tara wa kansa dukiya yake, idan ba shi da dukiya a wurin Allah.”
22 And he said to his disciples: “And so I say to you: Do not choose to be anxious about your life, as to what you may eat, nor about your body, as to what you will wear.
Yesu, ya ce da almajiransa, “Saboda haka ina cewa da ku, kada ku damu da rayuwarku, wato, abin da za ku ci, ko abin da za ku sa a jikinku.
23 Life is more than food, and the body is more than clothing.
Gama rai ya fi abinci, jiki kuma ya fi tufafi.
24 Consider the ravens. For they neither sow nor reap; there is no storehouse or barn for them. And yet God pastures them. How much more are you, compared to them?
Ku dubi hankaki wadanda ba sa yin shuka, ba sa yin girbi. Ba su da rumbuna ko dakunan ajjiya, amma Allah ya na ciyar da su. Ku fa kun fi tsuntsaye daraja!
25 But which of you, by thinking, is able to add one cubit to his stature?
Wanene a cikinku ta wurin sha'awarsa za ya iya karawa kansa kwanaki?
26 Therefore, if you are not capable, in what is so little, why be anxious about the rest?
Idan ba ku iya yi wa kanku dan karamin abu ba, me ya sa za ku damu da sauran abubuwa?
27 Consider the lilies, how they grow. They neither work nor weave. But I say to you, not even Solomon, in all his glory, was clothed like one of these.
Ku dubi furanni a daji - yadda suke yin girma. Ba su kan yi aiki ba, ba su kan yi kadi ba. Ina gaya maku, ko Sulaimanu, a cikin darajarsa, bai sa tufafin da suka fi nasu kyau ba.
28 Therefore, if God so clothes the grass, which is in the field today and thrown into the furnace tomorrow, how much more you, O little in faith?
Idan Allah ya sa wa ciyawa tufafi masu kyau haka, wadda yau tana nan, gobe kuma a sa ta a wuta, ta yaya zai kasa sa maku tufafi, ku masu kankantar bangaskiya!
29 And so, do not choose to inquire as to what you will eat, or what you will drink. And do not choose to be lifted up on high.
Kada ku damu da abin da za ku ci, ko abin da za ku sha, kuma kada ku yi alhini.
30 For all these things are sought by the Gentiles of the world. And your Father knows that you have need of these things.
Gama dukan al'umman duniya suna neman wadannan abubuwa, kuma Ubanku ya san kuna bukatar wada nan abubuwan.
31 Yet truly, seek first the kingdom of God, and his justice, and all these things shall be added to you.
Amma ku bidi mulkinsa, wadannan abubuwa kuma za a kara maku su.
32 Do not be afraid, little flock; for it has pleased your Father to give you the kingdom.
Kada ku ji tsoro, ku 'yan kanana, domin da murna Ubanku zai ba ku mulkin.
33 Sell what you possess, and give alms. Make for yourselves purses that will not wear out, a treasure that will not fall short, in heaven, where no thief approaches, and no moth corrupts.
Ku sayar da abin da ku ke da shi ku ba matalauta. Kuyi wa kanku jakukkuna wadanda ba za su lalace ba, ku yi ajjiya cikin sama inda abin ba ya karewa, inda barayi ba za su iya zuwa ba, kwari kuma ba za su iya lalatawa ba.
34 For where your treasure is, there will your heart be also.
Domin inda dukiyarka take, can zuciyarka za ta kasance kuma.
35 Let your waists be girded, and let lamps be burning in your hands.
Ku rage tsawon tufafinku, ku yi dammara, ya zama fitilarku tana ci koyaushe,
36 And let you yourselves be like men awaiting their lord, when he will return from the wedding; so that, when he arrives and knocks, they may open to him promptly.
ku kuma zama kamar wadanda suke jiran mai gidansu ya dawo daga gidan buki, domin duk sa'adda ya zo ya kwankwasa kofa, nan da nan za su bude masa.
37 Blessed are those servants whom the Lord, when he returns, will find being vigilant. Amen I say to you, that he will gird himself and have them sit down to eat, while he, continuing on, will minister to them.
Masu albarka ne wadannan bayi, wadanda ubangijinsu za ya tarar suna jiran dawowar sa. Gaskiya ni ke gaya ma ku, zai yi dammara yasa su zazzauna ya ba su abinci shi da kansa.
38 And if he will return in the second watch, or if in the third watch, and if he will find them to be so: then blessed are those servants.
Ko da ubangijinsu ya zo da dare, ko da tsakar dare, ya tarar da su a shirye suna jiransa. Masu albarka ne wadannan bayi.
39 But know this: that if the father of the family knew at what hour the thief would arrive, he would certainly stand watch, and he would not permit his house to be broken into.
Kuma ku san wannan, da mai gida ya san lokacin da barawo zai zo, ba zai bari a fasa masa gida a shiga ba.
40 You also must be prepared. For the Son of man will return at an hour that you will not realize.”
Sai ku zauna da shiri fa domin ba ku san lokacin da Dan Mutum zai dawo ba.”
41 Then Peter said to him, “Lord, are you telling this parable to us, or also to everyone?”
Sai Bitrus ya ce masa, “Ubangiji, mu ka ke fadawa wannan misali, ko ga kowa da kowa ne?”
42 So the Lord said: “Who do you think is the faithful and prudent steward, whom his Lord has appointed over his family, in order to give them their measure of wheat in due time?
Sai Ubangiji ya ce, “Wanne shugaba ne, mai aminci, mai hikima kuma wanda ubangijinsa za ya damka bayinsa a hannunsa, domin ya kula da su, ya ba su abincinsu a kan lokaci?
43 Blessed is that servant if, when his Lord will return, he will find him acting in this manner.
Mai albarka ne wannan bawa, wanda ubangijinsa za ya tarar da shi yana yin abin da aka sa shi ya yi.
44 Truly I say to you, that he will appoint him over all that he possesses.
Hakika, ina gaya maku, zai danka dukan malakarsa a gareshi.
45 But if that servant will have said in his heart, ‘My Lord has made a delay in his return,’ and if he has begun to strike the men and women servants, and to eat and drink, and to be inebriated,
Amma idan wannan bawa, ya ce a cikin zuciyarsa, 'Ubangiji na yayi jinkirin dawowa,' sai ya fara dukan bayin, maza da mata abokan bautarsa, ya ci ya sha, ya bugu,
46 then the Lord of that servant will return on a day which he hoped not, and at an hour which he knew not. And he will separate him, and he will place his portion with that of the unfaithful.
ubangijin bawan nan zai dawo a lokacin da bawan bai sa tsammani ba, kuma a cikin lokacin da bai sani ba, ya daddatsa shi gunduwa-gunduwa, ya kuma hada shi da marasa aminci.
47 And that servant, who knew the will of his Lord, and who did not prepare and did not act according to his will, will be beaten many times over.
Bawan nan, ya san halin ubagijinsa, amma bai shirya yayi abin da ubangijinsa yake so ba. Zai sha duka da bulala da yawa.
48 Yet he who did not know, and who acted in a way that deserves a beating, will be beaten fewer times. So then, of all to whom much has been given, much will be required. And of those to whom much has been entrusted, even more will be asked.
Amma shi wanda bai sani ba, kuma yayi abin da ba daidai ba, ba zai sha duka da bulala da yawa ba. Dukan wanda aka ba abu da yawa, za a kuma nemi abu da yawa daga wurinsa. Kuma ga wanda aka ba abu da yawa amana, za a nemi abu mafi yawa daga gareshi.
49 I have come to cast a fire upon the earth. And what should I desire, except that it may be kindled?
Na zo domin in sa wuta a duniya, na so da ta riga ta kama.
50 And I have a baptism, with which I am to be baptized. And how I am constrained, even until it may be accomplished!
Amma ni, ina da baftisma wadda za a yi mani baftisma da ita, kuma na kagara, da an riga an yi ta!
51 Do you think that I have come to give peace to the earth? No, I tell you, but division.
Kuna zaton na zo duniya domin in kawo salama? Na ce maku a'a, amma tsattsaguwa.
52 For from this time on, there will be five in one house: divided as three against two, and as two against three.
Daga yanzu za a sami mutane biyar a cikin gida daya, kuma za su rarrabu, mutane uku suna gaba da biyu, biyun kuma suna gaba da ukun.
53 A father will be divided against a son, and a son against his father; a mother against a daughter and a daughter against a mother; a mother-in-law against her daughter-in-law, and a daughter-in-law against her mother-in-law.”
Da da mahaifi za su yi gaba da juna, dan zai yi gaba da mahaifinsa. Mahaifiya za ta yi gaba da diyarta, diya kuma gaba da mahafiyarta; uwar miji za ta yi gaba da matar danta, matar da kuma gaba da uwar mijinta.”
54 And he also said to the crowds: “When you see a cloud rising from the setting of the sun, immediately you say, ‘A rain cloud is coming.’ And so it does.
Yesu, ya kuma gaya wa taron, “Da kun ga hadari ya taso daga yamma, nan da nan sai ku ce za a yi ruwa, haka kuwa ya kan zama.
55 And when a south wind is blowing, you say, ‘It will be hot.’ And so it is.
Idan iska tana busowa daga kudu sai ku ce za a yi zafi mai tsanani, haka kuwa ya kan faru.
56 You hypocrites! You discern the face of the heavens, and of the earth, yet how is it that you do not discern this time?
Munafukai, kun iya fasarta yanayin kasa da sama, amma baku iya fasarta abin da yake faruwa yanzu ba?
57 And why do you not, even among yourselves, judge what is just?
Me ya sa ba ku iya gane abin da zai tamake ku?
58 So, when you are going with your adversary to the ruler, while you are on the way, make an effort to be freed from him, lest perhaps he may lead you to the judge, and the judge may deliver you to the officer, and the officer may cast you into prison.
Idan kuna tafiya wurin shari'a da abokin husumarka, ka yi kokari ku daidaita tun a kan hanya domin kada ya kai ka wurin mai shari'a. Domin kada mai shari'a ya mika ka ga mai tsaron kurkuku, shi kuwa mai tsaron kurkuku ba zai nuna maka sani a cikin kurkuku ba.
59 I tell you, you will not depart from there, until you have paid the very last coin.”
Na gaya maka, ba za ka iya fitowa ba sai ka biya dukan kudin da a ke binka?

< Luke 12 >