< Job 29 >

1 Job also added to this, using figures of speech, and he said:
Ayuba ya ci gaba da jawabinsa,
2 Who will grant to me that I might be as I was in former months, according to the days when God kept watch over me?
“Da ma ina nan lokacin da ya wuce baya can, kwanakin da Allah yake lura da ni,
3 At that time, his lamp shined over my head, and by his light, I walked through the darkness.
lokacin da fitilarsa take haske a kaina na yi tafiya cikin duhu tare da haskensa.
4 I was then just as in the days of my youth, when God was privately in my tabernacle.
Kwanakin da nake tasowa, lokacin da abokantakar Allah ta sa wa gidana albarka,
5 At that time, the Almighty was with me and my children surrounded me.
lokacin da Maɗaukaki yana tare da ni, kuma’ya’yana suna kewaye da ni,
6 Then, I washed my feet with butter, and a boulder poured out rivers of oil for me.
lokacin da ake zuba madara a inda nake takawa, duwatsu kuma suna ɓulɓulo mini man zaitun.
7 When I went to the gate of the city, or to the main street, they prepared a chair for me.
“Sa’ad da na je ƙofar birni na zauna a bainin jama’a,
8 The youths saw me and hid themselves, and the elders, rising up, remained standing.
matasan da suka gan ni sukan ja gefe tsofaffi kuma suka tashi tsaye;
9 The leaders stopped talking, and they placed a finder over their mouth.
sarakuna suka yi shiru suka rufe bakunansu da hannuwansu;
10 The commanders subdued their voice, and their tongue adhered to their throat.
Muryar manya ta yi tsit harshensu ya manne a rufin bakunansu.
11 The ear that heard me, blessed me, and the eye that saw me, gave testimony for me.
Duk wanda ya ji ni ya yaba mini waɗanda suka gan ni kuma sun amince da ni,
12 This was because I had freed the poor, who cried out, and the orphan, who had no helper.
domin na ceci matalauta waɗanda suka nemi taimako, da marasa mahaifi waɗanda ba su da wanda zai taimake su.
13 The blessing of him who would have been destroyed came upon me, and I consoled the heart of the widow.
Mutumin da yake bakin mutuwa ya sa mini albarka. Na faranta wa gwauruwa zuciya.
14 I put on justice, and I clothed myself with my judgment, like a robe and a diadem.
Na yafa adalci ya zama suturata; gaskiya ita ce rigata da rawanina.
15 I was an eye for the blind and a foot for the lame.
Ni ne idon makafi kuma ƙafa ga guragu.
16 I was the father of the poor; and if I lacked knowledge about any case, I investigated very diligently.
Ni mahaifi ne ga masu bukata; na tsaya wa baƙo.
17 I crushed the jaws of the impious, and I took away prey from his teeth.
Na karya ƙarfin mugaye na ƙwato waɗanda suke riƙe da haƙoransu.
18 And I said, “I will die in my little nest, and like a palm tree, I will multiply my days.
“Na yi tunani cewa, ‘Zan mutu a cikin gidana, kwanakina da yawa kamar turɓayar ƙasa.
19 My root has been spread beside the waters, and the dew will remain with my harvest.
Jijiyoyina za su kai cikin ruwa, kuma raɓa za tă kwanta a rassana dukan dare.
20 My glory will always be restored, and my bow will be restored to my hand.”
Ɗaukakata za tă kasance tare da ni garau, bakana koyaushe sabo ne a hannuna.’
21 Those who heard me, expected vindication, and they listened closely in silence to my counsel.
“Mutane suna mai da hankali su saurare ni, suna yin shiru don su ji shawarata.
22 To my words, they dared to add nothing, and my eloquence poured over them.
Bayan da na yi magana, ba su ƙara ce kome ba. Maganata ta shige su.
23 They waited for me as for rain, and they opened their mouth as for belated rains.
Sukan jira ni kamar yadda ake jiran ruwan sama. Sukan sha daga cikin maganganuna kamar mai shan ruwan bazara.
24 If I had ever laughed at them, they would not have believed it, and the light of my face was not cast down towards the ground.
Sa’ad da na yi musu murmushi da ƙyar sukan yarda; hasken fuskata yana da daraja a gare su.
25 If I wished to go to them, I sat down first, and, though I sat like a king surrounded by an army, yet I was a comforter to those who mourned.
Na zaɓar masu inda za su bi na kuma zauna kamar sarkinsu; na zauna kamar sarki a cikin rundunansu; ina nan kamar mai yi wa masu makoki ta’aziyya.

< Job 29 >