< Jeremiah 40 >

1 The word that came to Jeremiah from the Lord, after Nebuzaradan, the leader of the military, had released him from Ramah, where he had taken him, bound in chains, along with all those who were being carried away from Jerusalem and from Judah, and were being led to Babylon.
Sai magana ta zo wa Irmiya daga Ubangiji bayan Nebuzaradan shugaban matsaran sarki ya sake shi a Rama. Ya sami Irmiya a daure da sarƙoƙi a cikin sauran kamammu daga Urushalima da kuma Yahuda waɗanda ake kaiwa zaman bauta a Babilon.
2 Therefore, the leader of the military, taking Jeremiah, said to him: “The Lord your God has declared this evil over this place,
Sa’ad da shugaban matsaran ya sami Irmiya sai ya ce masa, “Ubangiji Allahnka ya sa wannan masifa saboda wannan wuri.
3 and he has brought it. And the Lord has done just as he has spoken. For you have sinned against the Lord, and you have not heeded his voice, and so this word has happened to you.
Yanzu kuma Ubangiji ya cika shi; ya yi kamar yadda ya faɗa. Dukan wannan ya faru domin kun yi zunubi ga Ubangiji ba ku kuwa yi masa biyayya ba.
4 Now therefore, behold, I have released you this day from the chains which were on your hands. If it pleases you to come with me into Babylon, then come. And I will set my eyes upon you. But if it displeases you to come with me into Babylon, then remain. Behold, all the land is in your sight. Whatever you will choose, and wherever it will please you to go, so shall you go, proceeding to that place.
Amma yau ina’yantar da kai daga sarƙoƙin da suke a hannuwanka. Zo mu tafi Babilon, in kana so, zan kuwa lura da kai; amma in ba ka so, kada ka zo. Ga shi, dukan ƙasar tana a gabanka; ka tafi duk inda ka so.”
5 And you may decline to come with me. For you may live with Gedaliah, the son of Ahikam, the son of Shaphan, whom the king of Babylon has made governor over the cities of Judah. Therefore, you may live with him in the midst of the people. And you may go wherever it will please you to go.” And the leader of the military also gave him foods and gifts, and he released him.
Amma, kafin Irmiya yă juya yă tafi, Nebuzaradan ya ƙara da cewa, “Ka koma wurin Gedaliya ɗan Ahikam, ɗan Shafan, wanda sarkin Babilon ya naɗa a kan garuruwan Yahuda, ka zauna da shi a cikin mutane, ko kuwa ka tafi duk inda ka ga dama.” Sa’an nan shugaban ya ba shi abinci da kuma kyauta sai ya bar shi ya tafi.
6 Then Jeremiah went to Gedaliah, the son of Ahikam, at Mizpah. And he lived with him in the midst of the people, those who had been left behind in the land.
Saboda haka Irmiya ya tafi wurin Gedaliya ɗan Ahikam, a Mizfa ya zauna tare da shi a cikin mutanen da aka bari a ƙasar.
7 And when all the leaders of the army, who had been dispersed throughout the regions, they and their associates, had heard that the king of Babylon had made Gedaliah, the son of Ahikam, governor of the land, and that he had committed to him the men, and women, and children, and the poor of the land, who had not been carried away to Babylon,
Sa’ad da dukan shugabannin hafsoshin tare da mutanen da suke a karkara suka ji cewa sarkin Babilon ya naɗa Gedaliya ɗan Ahikam gwamna a kan ƙasar ya kuma sa shi ya lura da maza, mata da’ya’yan da suke mafi talauci a ƙasar da waɗanda ba a kwashe zuwa zaman bauta a Babilon ba,
8 they went to Gedaliah at Mizpah, with Ishmael, the son of Nethaniah, and Johanan and Jonathan, the sons of Kareah, and Seraiah, the son of Tanhumeth, and the sons of Ephai, who were of Netophathi, and Jezaniah, the son of Maacathi, they and their men.
sai suka zo wurin Gedaliya a Mizfa, Ishmayel ɗan Netaniya, Yohanan da Yonatan’ya’yan Kareya, da Serahiya ɗan Tanhumet maza,’ya’yan Efai maza, mutumin Netofa, da Yezaniya ɗan mutumin Ma’aka da mutanensu.
9 And Gedaliah, the son of Ahikam, the son of Shaphan, swore to them and to their companions, saying: “Do not be afraid to serve the Chaldeans. Live in the land, and serve the king of Babylon, and it will be well with you.
Gedaliya ɗan Ahikam, ɗan Shafan, ya yi rantsuwa don yă tabbatar musu da mutanensu. Ya ce, “Kada ku ji tsoron bauta wa Babiloniyawa. Ku zauna a ƙasar ku bauta wa sarkin Babilon, zai kuma yi muku amfani.
10 Behold, I live at Mizpah, so that I may follow the instruction of the Chaldeans who are sent to us. But as for you, gather the vintage, and the harvest, and the oil, and store it up in your vessels, and dwell in your cities, which you hold.”
Ni kaina zan zauna a Mizfa in zama wakilinku a gaban Babiloniyawa waɗanda za su zo wurinmu, amma ku girbe ruwan inabi,’ya’yan itatuwa na kaka, da mai, ku zuba su a tulunan ajiyarku, ku kuma zauna a garuruwan da kuka ci.”
11 So then, all the Jews, who were in Moab, and among the sons of Ammon, and in Idumea, and in all the regions, when they had heard that the king of Babylon had left a remnant in Judea, and that he had made Gedaliah, the son of Ahikam, the son of Shaphan, governor over them,
Sa’ad da dukan Yahudawan da suke a Mowab, Ammon, Edom da sauran ƙasashe suka ji cewa sarkin Babilon ya bar raguwa a Yahuda ya kuma naɗa Gedaliya ɗan Ahikam, ɗan Shafan gwamna a kansu,
12 all the Jews, I say, returned from all the places to which they had fled, and they came into the land of Judah, to Gedaliah at Mizpah. And they gathered wine and an exceedingly great harvest.
sai suka dawo ƙasar Yahuda, wurin Gedaliya a Mizfa, daga dukan ƙasashen da suke a warwatse. Suka girbe ruwan inabi a yalwace da’ya’yan itatuwan kaka.
13 Then Johanan, the son of Kareah, and all the leaders of the army, who had been dispersed in the regions, came to Gedaliah at Mizpah.
Yohanan ɗan Kareya da dukan manyan sojoji da suke a karkara suka zo wurin Gedaliya a Mizfa
14 And they said to him: “Know that Baalis, the king of the sons of Ammon, has sent Ishmael, the son of Nethaniah, to strike down your life.” And Gedaliah, the son of Ahikam, did not believe them.
suka ce masa, “Ba ka san cewa Ba’alis sarkin Ammonawa ya aiki Ishmayel ɗan Netaniya ya ɗauke ranka ba?” Amma Gedaliya ɗan Ahikam bai gaskata su ba.
15 But Johanan, the son of Kareah, spoke to Gedaliah, separately, at Mizpah, saying: “I will go, and I will strike down Ishmael, the son of Nethaniah, without anyone knowing; otherwise he may kill you, and all the Jews will be scattered who have been gathered to you, and the remnant of Judah will perish.”
Sai Yohanan ɗan Kareya ya yi wa Gedaliya a Mizfa magana a asirce ya ce, “Bari in tafi in kashe Ishmayel ɗan Netaniya, ba kuwa wanda zai sani. Me zai sa ya ɗauke ranka ya watsar da dukan Yahudawan da suka taru kewaye da kai har waɗanda suka ragu na Yahuda su hallaka?”
16 And Gedaliah, the son of Ahikam, said to Johanan, the son of Kareah: “Do not do this word. For what you have said about Ishmael is false.”
Amma Gedaliya ɗan Ahikam ya ce wa Yohanan ɗan Kareya, “Kada ka yi irin wannan abu! Abin da kake faɗa game da Ishmayel ba gaskiya ba ne.”

< Jeremiah 40 >