< Jeremiah 25 >
1 The word that came to Jeremiah about all the people of Judah, in the fourth year of Jehoiakim, the son of Josiah, the king of Judah. The same is the first year of Nebuchadnezzar, the king of Babylon.
Magana ta zo wa Irmiya game da dukan mutanen Yahuda a shekara ta huɗu ta Yehohiyakim ɗan Yosiya sarkin Yahuda, wadda ta kasance shekara ta fari ta Nebukadnezzar sarkin Babilon.
2 And the prophet Jeremiah spoke to all the people of Judah, and to all the inhabitants of Jerusalem, saying:
Saboda haka Irmiya annabi ya ce wa dukan mutanen Yahuda da dukan mazaunan Urushalima.
3 “From the thirteenth year of Josiah, the son of Amon, the king of Judah, even until this day, which is the twenty-third year, the word of the Lord has been given to me, and I have spoken to you, rising while it was still night, and speaking, and yet you have not listened.
Shekaru ashirin da uku, daga shekara ta goma sha uku ta Yosiya ɗan Amon sarkin Yahuda har zuwa wannan rana, maganar Ubangiji ta zo mini na kuma yi muku magana sau da sau, amma ba ku saurara ba.
4 And the Lord has sent to you all his servants, the prophets, rising at first light, and sending, and yet you have not listened, and you have not inclined your ears, so that you would hear,
Ko da yake Ubangiji ya aika dukan bayinsa annabawa gare ku sau da sau, ba ku saurara ba, ba ku kuma kula ba.
5 when he said: Return, each one from his evil way, and from your wicked thoughts. And you shall dwell in the land, which the Lord has given to you and to your fathers, from ancient times and even forever.
Sun ce, “Ku juye yanzu, kowannenku, daga mugayen hanyoyinku da mugayen ayyukanku, za ku kuwa iya zauna a ƙasar da Ubangiji ya ba ku da kuma kakanninku har abada abadin.
6 And do not choose to go after strange gods, so that you would serve them and adore them. And do not provoke me to wrath by the works of your hands. And then I will not afflict you.
Kada ku bi waɗansu alloli don ku bauta ku kuma yi musu sujada; kada ku tsokane ni in yi fushi da abin da hannuwanku suka yi. Sa’an nan ba zan kawo muku lahani ba.”
7 And yet you have not listened to me, says the Lord, and so you have provoked me to anger with the works of your hands, to your own harm.”
“Amma ba ku saurare ni ba,” in ji Ubangiji, “kun tsokane ni da abin da kuka yi da hannuwanku, kuka kuma kawo lahani wa kanku.”
8 Because of this, thus says the Lord of hosts: “Since you have not listened to my words,
Saboda haka Ubangiji Maɗaukaki ya ce, “Domin kun ƙi ku saurara ga maganata,
9 behold, I will send for and take all the associates of the north, says the Lord, and Nebuchadnezzar, the king of Babylon, my servant, and I will lead them over this land, and over its inhabitants, and over all the nations that are around it. And I will destroy them, and I will set them in the midst of stupor and hissing, and continual desolations.
zan kira dukan mutanen arewa da bawana Nebukadnezzar sarkin Babilon,” in ji Ubangiji, “zan kuma kawo su su yi gāba da wannan ƙasa da mazaunanta da kuma gāba da dukan al’ummai da suke kewaye. Zan hallaka su sarai in kuma mai da su abin bantsoro da abin dariya, za su kuma zama kufai har abada.
10 And I will perish from them the voice of gladness and the voice of rejoicing, the voice of the groom and the voice of the bride, the sound of the millstone and the light of the lamp.
Zan kawar da muryoyin farin ciki da murna daga gare su, muryoyin amarya da na ango, ƙarar dutsen niƙa da hasken fitila.
11 And this entire land will be in desolation and in stupor. And all these nations will serve the king of Babylon, for seventy years.
Dukan wannan ƙasa za tă zama kango, kuma waɗannan al’ummai za su bauta wa sarkin Babilon shekaru saba’in.
12 And when the seventy years have been completed, I will visit their iniquity upon the king of Babylon, and upon that nation, and upon the land of the Chaldeans, says the Lord. And I will set it in continual desolations.
“Amma sa’ad da shekaru saba’in ɗin suka cika, zan hukunta sarkin Babilon da kuma al’ummarsa, ƙasar Babiloniyawa, saboda laifinsu,” in ji Ubangiji, “in kuma mai da ita kango har abada.
13 And I will lead over that land all my words, which I have spoken against it, all that has been written in this book, everything whatsoever that Jeremiah has prophesied against all the nations.
Zan kawo wa wannan ƙasa dukan abubuwan na yi magana a kanta, dukan abubuwan da aka rubuta a wannan littafi, abubuwan da Irmiya kuma ya yi annabci a kan dukan al’ummai.
14 For they have served them, though these were populous nations and great kings. And I will repay them according to their works and according to the deeds of their hands.”
Su kansu al’ummai da sarakuna masu yawa za su bautar da su; zan sāka musu bisa ga ayyukansu da aikin hannuwansu.”
15 For thus says the Lord of hosts, the God of Israel: “Take the chalice of the wine of this fury from my hand. And you shall cause all the nations, to which I will send you, to drink from it.
Ga abin da Ubangiji, Allah na Isra’ila, ya faɗa mini, “Ka karɓi kwaf ruwan inabin nan na fushina a wurina, ka sa dukan al’umman da na aike ka gare su, su sha.
16 And they will drink, and be stirred up, and become maddened, before the face of the sword that I will send among them.”
Sa’ad da suka sha, za su yi ta tangaɗi su kuma yi hauka saboda takobin da zan aika a cikinsu.”
17 And I received the chalice from the hand of the Lord, and I caused all the nations, to which the Lord has sent me, to drink from it:
Saboda haka na karɓi kwaf daga hannun Ubangiji na sa dukan al’ummai waɗanda ya aiko ni wurinsu su sha.
18 Jerusalem, and the cities of Judah, and its kings, and its leaders, so that I gave them over to desolation, and stupor, and hissing, and a curse, just as it is this day.
Urushalima da garuruwan Yahuda, sarakunan da fadawanta, don su mai da su kufai da kuma abin bantsoro da ba’a da la’ana, yadda suke a yau;
19 “But as for Pharaoh, the king of Egypt, and his servants, and his leaders, and all his people,
Fir’auna sarkin Masar, ma’aikatansa, fadawansa da dukan mutanensa,
20 and the entire populace in general: all the kings of the land of the south, and all the kings of the land of the Philistines, and Ashkelon, and Gaza, and Ekron, and the remnant of Ashdod,
da dukan baƙin da suke can; dukan sarakunan Uz; dukan sarakunan Filistiyawa (waɗannan na Ashkelon, Gaza, Ekron da mutanen da aka bari a Ashdod);
21 and Idumea, and Moab, and the sons of Ammon,
Edom, Mowab da Ammon;
22 and all the kings of Tyre, and all the kings of Sidon, and the kings of the land of the islands that are across the sea,
dukan sarakunan Taya da Sidon; sarakunan bakin teku a ƙetaren teku;
23 and Dedan, and Tema, and Buz, and all those who have shaved off their hair,
Dedan, Tema, Buz da dukan waɗanda suke a manisantan wurare;
24 and all the kings of Arabia, and all the kings of the west, who live in the desert,
dukan sarakunan Arabiya da dukan sarakunan baƙin da suke zama a hamada;
25 and all the kings of Zimri, and all the kings of Elam, and all the kings of Media,
dukan sarakunan Zimri, Elam da Mediya;
26 and likewise, all the kings of the north from near to far, each one facing his brother, and all the kingdoms upon the face of the earth, and the king of Sesac: all these shall drink after them.
da kuma dukan sarakunan arewa, nesa da kuma kusa, bi da bi, dukan mulkokin duniya. Bayan dukansu kuma, sai sarkin Sheshak ma yă sha.
27 And you shall say to them: Thus says the Lord of hosts, the God of Israel: Drink, and be inebriated, and vomit, and fall down. And you shall not rise up before the face of the sword that I will send among you.
“Sa’an nan na faɗa musu cewa, ‘Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki, Allah na Isra’ila, yana cewa ku sha, ku bugu ku kuma yi amai, ku fāɗi, kada kuma ku ƙara tashi saboda takobin da zan aiko muku.’
28 And if they refuse to receive the cup from your hand and to drink, you shall say to them: Thus says the Lord of hosts: Certainly, you shall drink!
Amma in suka ki su karɓi kwaf ɗin daga hannunka su sha, ka faɗa musu cewa, ‘Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki yana cewa dole ku sha!
29 For behold, I am beginning to afflict the city in which my name has been invoked, and will you be innocent and immune? You will not be immune! For I will call the sword over all the inhabitants of the earth, says the Lord of hosts.
Ga shi, na sa masifa tă yi aiki cikin birnin da ake kira da sunana, kuna gani za ku tafi ba hukunci? Ba za ku tafi ba hukunci ba, gama ina kawo wa dukan mazaunan duniya takobi, in ji Ubangiji Maɗaukaki.’
30 And you shall prophesy to them all these words, and you shall say to them: The Lord will roar from on high, and he will utter his voice from his holy habitation. When roaring, he will roar over the place of his beauty. He will call out, like those who chant in rhythm as they trample the grapes, against all the inhabitants of the earth.
“Yanzu ka yi annabcin dukan waɗannan maganganu a kansu ka kuma ce musu, “‘Ubangiji zai yi ruri daga bisa; zai yi tsawa daga mazauninsa mai tsarki ya kuma yi ruri da ƙarfi a kan ƙasarsa. Zai yi ihu kamar waɗanda suke matsin’ya’yan inabi, yi ihu a kan dukan waɗanda suke zaune a duniya.
31 The sound of it will penetrate even to the ends of the earth. For the Lord is entering into judgment with the nations. He himself is entering into judgment with all flesh. I have delivered the impious to the sword, says the Lord.”
Hayaniya za tă taso har iyakar duniya, gama Ubangiji zai kawo tuhume-tuhume a kan al’ummai; zai kawo shari’a a kan dukan’yan adam ya kuma kashe mugaye da takobi,’” in ji Ubangiji.
32 Thus says the Lord of hosts: “Behold, an affliction will go forth from nation to nation, and a great whirlwind will go forth from the ends of the earth.
Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki yana cewa, “Duba! Masifa tana yaɗuwa daga al’umma zuwa al’umma; hadari mai girma yana tasowa daga iyakar duniya.”
33 And the slain of the Lord will be, on that day, from one end of the earth, even to the other end. They will not be mourned, and they will not be gathered, and they will not be buried. They will lie upon the face of the earth like dung.
A lokacin waɗanda Ubangiji ya kashe za su kasance a ko’ina, daga wannan bangon duniya zuwa wancan. Ba za a yi kuka dominsu, ba za a tattara su don a binne ba, amma za su zama kamar juji da an tsiba a ƙasa.
34 Wail, O shepherds, and cry out! And sprinkle yourselves with ashes, O nobles of the flock! For the days have been completed that lead to your slaughter and your destruction. And you will fall like precious vessels.
Ku yi kuka ku kuma yi makoki, ku makiyaya; ku yi ta birgima a ƙura, ku shugabannin garke. Gama lokacin da za a yanka ku ya zo; za ku fāɗi ku kuma farfasa kamar tukunyar yumɓu mai kyau.
35 And escape will flee from the shepherds, and safety will flee from the nobility of the flock.”
Makiyaya ba za su sami wurin da za su gudu su tafi ba, shugabannin garke ba za su sami wurin kuɓuta ba.
36 There is a voice of outcry from the shepherds, and a wailing among the nobles among the flock! For the Lord has laid waste to their pastures.
Ji kukan makiyaya, kururuwan shugabannin garke, gama Ubangiji yana hallaka wurin kiwo.
37 And the fields of peace have been silenced before the face of the fury of the Lord.
Rafi mai gudu a hankali zai zama kango saboda zafin fushin Ubangiji.
38 He has abandoned those he sheltered like a lion. For the earth has become a desolation before the face of the anger of the dove, and before the face of the fury of the Lord.
Kamar zaki zai bar wurin ɓuyarsa, ƙasarsu kuma za tă zama kufai saboda takobin masu danniya da kuma saboda zafin fushin Ubangiji.