< Isaiah 28 >

1 Woe to the crown of arrogance, to the inebriated of Ephraim, and to the falling flower, the glory of his exultation, to those who were at the top of the very fat valley, staggering from wine.
Kaito ga wannan rawani, girman kai na mashayan Efraim, ga fure mai yanƙwanewa, darajar kyansa, da aka sa a kan kwari mai ba da amfani, ga birnin nan, wadda take girman kan waɗanda aka ƙasƙantar da ruwan inabinsu!
2 Behold, the Lord is powerful and steadfast, like a storm of hail, like a crushing whirlwind, like the force of many waters, inundating, sent forth over a spacious land.
Duba, Ubangiji yana da wanda yake da iko da kuma ƙarfi. Kamar dutsen ƙanƙara da kuma iska mai ɓarna, kamar kwararowar ruwa da rigyawa mai kirmewa, zai jefa shi har ƙasa da ƙarfi.
3 The arrogant crown of the inebriated of Ephraim will be trampled underfoot.
Za a tattaka wannan rawani, girman kai na mashayan Efraim da ƙafa.
4 And the falling flower, the glory of his exultation, who is at the summit of the fat valley, will be like a premature fruit before the ripeness of autumn, which, when the onlooker beholds it, as soon he takes it in his hand, he will devour it.
Wannan fure mai yanƙwanewa, darajarar kyansa, da aka sa a kan kwari mai ba da amfani, zai zama kamar’ya’yan ɓaure, nunan fari, da zarar wani ya gani ya kuma tsinka, zai haɗiye shi.
5 In that day, the Lord of hosts will be the crown of glory and the wreath of exultation for the remnant of his people.
A wannan rana Ubangiji Maɗaukaki zai zama rawani mai daraja kyakkyawan rawani wa mutanensa da suka ragu.
6 And he will be the spirit of judgment for those who sit in judgment, and the strength of those who return from war to the gates.
Zai zama ruhun adalci gare shi wanda yake zaune a kujerar shari’a, wurin samun ƙarfi ga waɗanda suka kori abokan gāban da suka fāɗa musu da yaƙi a ƙofofi.
7 Yet truly, these also have been ignorant due to wine, and they have gone astray due to inebriation. The priest and the prophet have been ignorant because of inebriation. They have been absorbed by wine. They have staggered in drunkenness. They have not known the One who sees. They have been ignorant of judgment.
Da waɗannan kuma masu tangaɗi saboda sun sha ruwan inabi suke jiri don sun sha barasa Firistoci da annabawa suna tangaɗi saboda sun sha barasa sun kuma yi tatur da ruwan inabi; suna jiri saboda sun sha barasa, suna tangaɗi sa’ad da suke ganin wahayi, suna tuntuɓe sa’ad da suke ba da shawara.
8 For all the tables have been filled with vomit and filth, so much so that there was no place left.
Duk amai ya rufe teburori kuma babu wani wurin da ba a ɓata ba.
9 To whom will he teach knowledge? And to whom will he grant an understanding of what is heard? To those who have been weaned from the milk, who have been pulled away from the breasts.
“Wane ne yake so ya koyar? Ga wa yake bayyana saƙonsa? Ga yaran da aka yaye, ga waɗanda ba a daɗe da yayewa ba ne?
10 So then: command, and command again; command, and command again; expect, and expect again; a little here, and a little there.
Gama haka yake. Yi ka kuma yi, yi ka kuma yi, mulki a kan mulki, mulki a kan mulki; nan kaɗan, can kaɗan.”
11 For with the speech of lips and with a different language, he will speak to this people.
To da kyau, da leɓunan baƙi da ku harsunan da ba sani ba Allah zai yi magana da wannan mutane,
12 He said to them: “This is my rest. Refresh the weary,” and, “This is my refreshment.” And yet they were unwilling to listen.
waɗanda zai ce, “Wannan shi ne wurin hutu, bari waɗanda suka gaji su huta”; da kuma, “Wannan shi ne wurin wartsakewa” amma sun ƙi su saurara.
13 And so, the word of the Lord to them will be: “Command, and command again; command, and command again; expect, and expect again; a little here, and a little there,” so that they may go forward and fall backward, and so that they may be broken and ensnared and captured.
Saboda haka fa, maganar Ubangiji gare su za tă zama, Yi ka kuma yi, yi ka kuma yi, mulki akan mulki, mulki a kan mulki; nan kaɗan, can kaɗan, domin su tafi su kuma fāɗi da baya, su ji rauni a kuma kama su da tarko, a kai su zaman bauta.
14 Because of this, listen to the word of the Lord, you mocking men, who lord it over my people who are at Jerusalem.
Saboda haka ku saurari maganar Ubangiji, ku masu ba’a ku da kuke mulkin wannan mutane a Urushalima.
15 For you have said: “We struck a deal with death, and we formed a pact with Hell. When the inundating scourge passes through, it will not overwhelm us. For we have placed our hope in lies, and we are protected by what is false.” (Sheol h7585)
Kuna fariya cewa, “Mun yi alkawari da mutuwa, mun kuma yi yarjejjeniya da kabari. Sa’ad da zafi ya ratsa, ba zai taɓa mu ba, gama mun mai da ƙarya mafakarmu ruɗu kuma wurin ɓuyanmu.” (Sheol h7585)
16 For this reason, thus says the Lord God: Behold, I will set a stone within the foundations of Zion, a tested stone, a cornerstone, a precious stone, which has been established in the foundation: whoever trusts in him need not hurry.
Saboda haka ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka ya ce, “Duba, na kafa dutse a Sihiyona, dutsen da aka gwada, dutsen kusurwa mai daraja don tabbataccen tushe; wanda ya dogara gare shi ba zai taɓa shan kunya ba.
17 And I will establish judgment in weights, and justice in measures. And a hailstorm will overturn hope in what is false; and waters will inundate its protection.
Zan mai da gaskiya igiyar gwaji adalci kuma ɗan katakon gwajin ginin; ƙanƙara za tă share mafakarku, ƙarya, da ruwa kuma za su mamaye maɓuyanku.
18 And your deal with death will be abolished, and your pact with Hell will not stand. When the inundating scourge passes through, you will be trampled down by it. (Sheol h7585)
Za a soke alkawarinku da mutuwa; yarjejjeniyarku da kabari ba zai zaunu ba. Sa’ad da zafi mai ɓarna ya ratsa, zai hallaka ku. (Sheol h7585)
19 Whenever it passes through, it will take you away. For, at first light of morning, it will pass through, in the day and in the night, and vexation alone will make you understand what you hear.
A duk sa’ad da ya zo; ko da safiya, ko dare ko kuma da rana, zai yi ta ratsawa yana kwasanku.” Za ku zama kamar mutumin da ya zama abin karin magana,
20 For the bed has been narrowed, so much so that one alone would fall out, and the short blanket is not able to cover two.
wanda ya yi ƙoƙari yă kwanta a gajeren gado, yă kuma rufa da ɗan siririn bargo.
21 For the Lord will stand, just as at the mountain of divisions. He will be angry, just as in the valley which is in Gibeon, so that he may accomplish his work, his strange work, so that he may complete his work, his work which is foreign even to him.
Ubangiji zai tashi kamar yadda ya yi a Dutsen Feratsim, zai tā da kansa kamar a Kwarin Gibeyon don yă aikata aikinsa, aikinsa da ba a saba gani ba, yă kuma yi aikinsa, baƙon aikinsa.
22 And now, do not be willing to mock, lest your chains be tightened. For I have heard, from the Lord, the God of hosts, about the consummation and the abridgement concerning the entire earth.
Yanzu ku daina ba’arku, in ba haka ba sarƙoƙinku za su ƙara nauyi; Ubangiji, Ubangiji Maɗaukaki, ya faɗa mini game da hallakar da aka ƙaddara a kan dukan ƙasar.
23 Pay close attention, and listen to my voice! Attend and hear my eloquence!
Ku saurara ku kuma ji muryata; ku kasa kunne ku kuma ji abin da na faɗa.
24 Would the plowman, after plowing all day so that he may sow, instead cut open and hoe his soil?
Sa’ad da manomi ya yi noma don shuki, yakan ci gaba da noma ne? Yakan ci gaba da sara yana yin kunyoyi a ƙasa ne?
25 Will he not, when he has made the surface level, sow coriander, and scatter cumin, and plant wheat in rows, and barley, and millet, and vetch in their places?
Sa’ad da ya shirya wuri da kyau, ba yakan shuka kanumfari ya kuma yayyafa ɗaɗɗoya ba? Ba yakan shuka alkama a kunyoyinsa sha’ir a kunyoyinsa, tamba kuma a filinsa ba?
26 For he will be instructed in judgment; his God will teach him.
Allahnsa ya umarce shi ya kuma koya masa hanyar da take daidai.
27 For coriander cannot be threshed with a saw, and a cartwheel cannot revolve over cumin. Instead, coriander is shaken out with a stick, and cumin with a staff.
Ba a bugan kanumfari da ƙaton sanda ko a yi ta jujjuye ƙafar keke a kan ɗaɗɗoya; akan buga kanumfari da siririn sanda ɗaɗɗoya kuma da tsumagiya.
28 But grain for bread must be crushed. Truly, the thresher cannot thresh it unceasingly, and the cartwheel can neither disrupt it, nor break it with its surface.
Dole a niƙa hatsi don a yi burodi; saboda haka mutum ba zai yi ta bugun alkama, har yă ɓata tsabar ba. Ya san yadda zai sussuke alkamarsa, ba tare da ya ɓata tsabarta ba.
29 And this has gone forth from the Lord, the God of hosts, so that he may accomplish his miraculous plan and magnify justice.
Dukan wannan hikimar takan zo daga Ubangiji Maɗaukaki ne, shi da yake mashawarci mai banmamaki, mafifici kuma cikin hikima.

< Isaiah 28 >