< Galatians 6 >

1 And, brothers, if a man has been overtaken by any offense, you who are spiritual should instruct someone like this with a spirit of leniency, considering that you yourselves might also be tempted.
’Yan’uwa, in an kama wani yana cikin yin zunubi, ku da kuke masu ruhaniya ya kamata ku komo da shi a kan hanya a hankali. Amma ku lura da kanku, domin kada maimakon dawowa da ɗan’uwanku, ku ma ku fāɗi cikin jarraba.
2 Carry one another’s burdens, and so shall you fulfill the law of Christ.
Ku ɗauki nawayar juna, a haka kuwa za ku cika dokar Kiristi.
3 For if anyone considers himself to be something, though he may be nothing, he deceives himself.
In wani yana tsammani shi wani abu ne alhali kuwa shi ba kome ba, ruɗin kansa yake yi.
4 So let each one prove his own work. And in this way, he shall have glory in himself only, and not in another.
Kowa yă auna ayyukansa. A sa’an nan ne zai iya yin taƙama da kansa, ba tare da kwatanta kansa da wani ba,
5 For each one shall carry his own burden.
gama kowa zai ɗauki kayansa.
6 And let him who is being taught the Word discuss it with him who is teaching it to him, in every good way.
Duk haka, wanda aka koya wa maganar Kiristi, bari yă raba abubuwan nan na alheri tare da wanda ya koyar da shi.
7 Do not choose to wander astray. God is not to be ridiculed. For whatever a man will have sown, that also shall he reap.
Kada a ruɗe ku. Ba a yi wa Allah ba’a. Mutum yakan girbe abin da ya shuka ne.
8 For whoever sows in his flesh, from the flesh he shall also reap corruption. But whoever sows in the Spirit, from the Spirit he shall reap eternal life. (aiōnios g166)
Wanda ya yi shuki don yă gamshi mutuntakarsa, daga wannan mutuntaka zai girbi hallaka. Wanda ya yi shuki domin yă gamshi Ruhu, daga Ruhu zai girbi rai madawwami. (aiōnios g166)
9 And so, let us not be deficient in doing good. For in due time, we shall reap without fail.
Kada mu gaji da yin nagarta, gama a daidai lokaci za mu girbe amfani, in ba mu fid da zuciya ba.
10 Therefore, while we have time, we should do good works toward everyone, and most of all toward those who are of the household of the faith.
Saboda haka, in da hali, bari mu aikata nagarta ga dukan mutane, musamman ga waɗanda suke na iyalin masu bi.
11 Consider what kind of letters I have written to you with my own hand.
Ku dubi irin manya-manyan harufan da na yi amfani da su yayinda nake rubuta muku da hannuna!
12 For as many of you as they desire to please in the flesh, they compel to be circumcised, but only so that they might not suffer the persecution of the cross of Christ.
Waɗanda suke son nuna bajinta a fili suna ƙoƙari su tilasta muku ku yi kaciya ne. Dalilin kaɗai da suke yin haka shi ne don gudu kada a tsananta musu saboda gicciyen Kiristi ne.
13 And yet, neither do they themselves, who are circumcised, keep the law. Instead, they want you to be circumcised, so that they may glory in your flesh.
Kai, su masu kaciya ma ba su kiyaye Doka ba, duk da haka suna so a yi muku kaciya don su yi taƙama kan an yi muku kaciya.
14 But far be it from me to glory, except in the cross of our Lord Jesus Christ, through whom the world is crucified to me, and I to the world.
Kada in taɓa yin taƙama ga kome sai dai a cikin gicciyen Ubangijinmu Yesu Kiristi, wanda ta wurinsa aka gicciye duniya a gare ni, aka kuma gicciye ni ga duniya.
15 For in Christ Jesus, neither circumcision nor uncircumcision prevails in any way, but instead there is a new creature.
Kaciya ko rashin kaciya ba wani abu ba ne; abin da yake da amfani shi ne sabuwar halitta.
16 And whoever follows this rule: may peace and mercy be upon them, and upon the Israel of God.
Salama da jinƙai su tabbata ga dukan waɗanda suke bin wannan ƙa’ida, har ma ga Isra’ila na Allah.
17 Concerning other matters, let no one trouble me. For I carry the stigmata of the Lord Jesus in my body.
A ƙarshe, kada kowa yă ƙara damuna, gama ina ɗauke da raunuka masu nuna ni bawan Ubangiji Yesu ne.
18 May the grace of our Lord Jesus Christ be with your spirit, brothers. Amen.
’Yan’uwa! Alherin Ubangijinmu Yesu Kiristi yă kasance tare da ruhunku. Amin.

< Galatians 6 >