< Galatians 3 >

1 O senseless Galatians, who has so fascinated you that you would not obey the truth, even though Jesus Christ has been presented before your eyes, crucified among you?
Ya ku Galatiyawa marasa azanci! Wa ya ruɗe ku? A idanunku aka bayyana Yesu Kiristi gicciyeyye a sarari.
2 I wish to know only this from you: Did you receive the Spirit by the works of the law, or by the hearing of faith?
Zan so in san abu guda tak daga gare ku. Kun karɓi Ruhu ta wurin kiyaye Doka ne, ko kuwa ta wurin gaskata abin da kuka ji?
3 Are you so foolish that, though you began with the Spirit, you would now end with the flesh?
Ashe, rashin azancinku har ya kai ga haka? Bayan kun fara da Ruhu, a yanzu kuma da halin mutuntaka za ku ƙarasa?
4 Have you been suffering so much without a reason? If so, then it is in vain.
Ashe, wahaloli dabam-dabam da kuka sha sun zama a banza ke nan? Haka zai yiwu kuwa?
5 Therefore, does he who distributes the Spirit to you, and who works miracles among you, act by the works of the law, or by the hearing of the faith?
Allah ya ba ku Ruhunsa yana kuma aikata ayyukan banmamaki a cikinku saboda kuna kiyaye Doka ne, ko kuwa domin kuna gaskatawa abin da kuka ji ne?
6 It is just as it was written: “Abraham believed God, and it was reputed to him unto justice.”
Ku dubi Ibrahim mana, “Ya gaskata Allah, aka kuwa lissafta wannan adalci ne a gare shi.”
7 Therefore, know that those who are of faith, these are the sons of Abraham.
Ku sani fa, waɗannan waɗanda suka gaskata,’ya’yan Ibrahim ne.
8 Thus Scripture, foreseeing that God would justify the Gentiles by faith, foretold to Abraham: “All nations shall be blessed in you.”
Nassi ya hanga cewa Allah zai kuɓutar da Al’ummai ta wurin bangaskiya, ya kuwa sanar wa Ibrahim wannan bisharar tun kafin lokaci yă yi cewa, “Dukan al’ummai za su sami albarka ta wurinka.”
9 And so, those who are of faith shall be blessed with faithful Abraham.
Saboda haka waɗanda suke da bangaskiya sun sami albarka tare da Ibrahim, mutumin bangaskiya.
10 For as many as are of the works of the law are under a curse. For it has been written: “Cursed is everyone who does not continue in all the things that have been written in the book of the Law, so as to do them.”
Dukan waɗanda suka dogara ga kiyaye Doka la’anannu ne, gama a rubuce yake cewa, “La’ananne ne duk wanda bai ci gaba da yi dukan abubuwan da aka rubuta a Littafin Doka ba.”
11 And, since in the law no one is justified with God, this is manifest: “For the just man lives by faith.”
A fili yake ba wanda zai kuɓuta a gaban Allah ta wurin Doka, domin “Mai adalci zai rayu ta wurin bangaskiya.”
12 But the law is not of faith; instead, “he who does these things shall live by them.”
Doka ba tă dangana ga bangaskiya ba; a maimakon haka, “Mutumin da ya aikata waɗannan abubuwa zai rayu ta wurinsu.”
13 Christ has redeemed us from the curse of the law, since he became a curse for us. For it is written: “Cursed is anyone who hangs from a tree.”
Kiristi ya fanshe mu daga la’anar Doka ta wurin zama la’ana saboda mu, gama a rubuce yake cewa, “La’ananne ne duk wanda aka rataye a kan itace.”
14 This was so that the blessing of Abraham might reach the Gentiles through Christ Jesus, in order that we might receive the promise of the Spirit through faith.
Ya fanshe mu domin albarkar da aka yi wa Ibrahim yă zo ga Al’ummai, ta wurin Kiristi Yesu, domin ta wurin bangaskiya mu karɓi alkawarin Ruhu.
15 Brothers (I speak according to man), if a man’s testament has been confirmed, no one would reject it or add to it.
’Yan’uwa, bari in yi muku misali da rayuwarmu ta yau da kullum. Kamar dai yadda ba mai kawarwa ko yă ƙara wani abu cikin alkawarin da mutane suka kafa, haka yake a wannan batu.
16 The promises were made to Abraham and to his offspring. He did not say, “and to descendents,” as if to many, but instead, as if to one, he said, “and to your offspring,” who is Christ.
Alkawaran nan fa ga Ibrahim ne aka faɗa da kuma wani zuriyarsa. Nassi bai ce, “da zuriyoyi ba” wanda ya nuna kamar mutane da yawa, amma “ga zuriyarka,” wanda yake nufin mutum ɗaya, wanda shi ne Kiristi.
17 But I say this: the testament confirmed by God, which, after four hundred and thirty years became the Law, does not nullify, so as to make the promise empty.
Abin da nake nufi shi ne, Dokar da aka shigar ita bayan shekaru 430, ba tă kawar da alkawarin da Allah ya yi tun dā ba.
18 For if the inheritance is of the law, then it is no longer of the promise. But God bestowed it to Abraham through the promise.
Gama da a ce gādon yă dangana a kan doka ne, ai, da ba zai dangana a kan alkawari ba; amma Allah cikin alherinsa ya ba wa Ibrahim gādon ta wurin alkawari.
19 Why, then, was there a law? It was established because of transgressions, until the offspring would arrive, to whom he made the promise, ordained by Angels through the hand of a mediator.
To, don me aka kawo Doka? An yi ƙari da Doka ne don fitowa da laifi fili har kafin na zuriyan nan ya zo, wanda aka yi wa alkawarin, an ba da doka ta wurin mala’iku ne, aka kuma danƙa ta a hannun matsakanci.
20 Now a mediator is not of one, yet God is one.
Kuma akan bukaci wani a tsakani ne idan da mutum biyu ake zance, Allah kuwa ɗaya ne.
21 So then, was the law contrary to the promises of God? Let it not be so! For if a law had been given, which was able to give life, truly justice would be of the law.
To, Dokar ce tana gāba da alkawaran Allah ke nan? Sam, ko kaɗan! Gama da a ce an ba da Dokar da tana iya ba da rai, tabbatacce, da sai a sami adalci ta wurin Doka.
22 But Scripture has enclosed everything under sin, so that the promise, by the faith of Jesus Christ, might be given to those who believe.
Amma Nassi ya kulle kome a ƙarƙashin ikon zunubi, domin abin da aka yi alkawarin nan, da ake bayar ta wurin bangaskiya a cikin Yesu Kiristi, a ba da shi ga waɗanda suka gaskata.
23 But before the faith arrived, we were preserved by being enclosed under the law, unto that faith which was to be revealed.
Kafin bangaskiyan nan tă zo, mun kasance a daure a kurkuku a ƙarƙashin Doka, a kulle sai da bangaskiyar da za tă zo ta bayyana.
24 And so the law was our guardian in Christ, in order that we might be justified by faith.
Ta haka aka sa Dokar ta zama jagorarmu zuwa ga Kiristi don mu sami kuɓuta ta wurin bangaskiya.
25 But now that faith has arrived, we are no longer under a guardian.
Yanzu da bangaskiya ta zo, ba sauran zamanmu a ƙarƙashin Doka.
26 For you are all sons of God, through the faith which is in Christ Jesus.
Dukanku’ya’yan Allah ne ta wurin bangaskiya cikin Kiristi Yesu.
27 For as many of you as have been baptized in Christ have become clothed with Christ.
Gama dukanku da aka yi muku baftisma cikin Kiristi, kuna sanye da Kiristi ke nan.
28 There is neither Jew nor Greek; there is neither servant nor free; there is neither male nor female. For you are all one in Christ Jesus.
Babu bambanci tsakanin mutumin Yahuda da mutumin Al’ummai, bawa da’yantacce, namiji da ta mace, gama dukanku ɗaya ne cikin Kiristi Yesu.
29 And if you are Christ’s, then are you the offspring of Abraham, heirs according to the promise.
In kuwa ku na Kiristi ne, to, ku zuriyar Ibrahim ne, magāda kuma bisa ga alkawarin nan.

< Galatians 3 >