< Exodus 7 >
1 And the Lord said to Moses: “Behold, I have appointed you as the god of Pharaoh. And Aaron, your brother, will be your prophet.
Sai Ubangiji ya ce wa Musa, “Duba, na maishe ka kamar Allah ga Fir’auna, ɗan’uwanka Haruna kuma zai zama annabinka.
2 You will speak to him all that I command you. And he will speak to Pharaoh, so that he may release the sons of Israel from his land.
Za ka faɗi kome da na umarce ka, ɗan’uwanka Haruna kuwa zai faɗa wa Fir’auna, yă bar Isra’ilawa su fita daga ƙasarsa.
3 But I will harden his heart, and I will multiply my signs and wonders in the land of Egypt,
Amma zan taurare zuciyar Fir’auna, kuma ko da na ninka mu’ujizai da kuma alamu a Masar,
4 and he will not listen to you. And I will send my hand over Egypt, and I will lead my army and my people, the sons of Israel, from the land of Egypt, through very great judgments.
ba zai saurare ku ba. Don haka zan miƙa hannuna a kan Masar, in murƙushe ta da bala’i iri-iri, bayan haka zan fitar da taron mutanen Isra’ila daga ƙasar Masar ta wurin hukuntaina masu girma.
5 And the Egyptians will know that I am the Lord, who has extended my hand over Egypt, and who has led the sons of Israel from their midst.”
Masarawa kuwa za su san cewa ni ne Ubangiji sa’ad da na miƙa hannuna a kan Masar, na kuma fitar da Isra’ilawa daga gare ta.”
6 And so, Moses and Aaron did just as the Lord had instructed. And so it was done.
Musa da Haruna suka aikata yadda Ubangiji ya umarce su.
7 Now Moses was eighty years old, and Aaron eighty-three, when they spoke to Pharaoh.
Musa yana da shekara tamanin da haihuwa, Haruna kuma yana da shekara tamanin da uku, sa’ad da suka yi magana da Fir’auna.
8 And the Lord said to Moses and Aaron:
Ubangiji ya ce wa Musa da Haruna,
9 “When Pharaoh will say to you, ‘Show signs,’ you shall say to Aaron, ‘Take your staff, and cast it down before Pharaoh, and it will be turned into a snake.’”
“Sa’ad da Fir’auna ya ce muku, ‘Aikata wani al’ajabi,’ sai ka ce wa Haruna, ‘Ɗauki sandanka ka jefa shi a ƙasa, a gaban Fir’auna,’ zai kuwa zama maciji.”
10 And so Moses and Aaron entered to Pharaoh, and they did just as the Lord had commanded. And Aaron took the staff in the sight of Pharaoh and his servants, and it was turned into a snake.
Sai Musa da Haruna suka tafi wurin Fir’auna, suka yi yadda Ubangiji ya umarce su. Haruna ya jefa sandansa ƙasa, a gaban Fir’auna da bayinsa, sai sandan ya zama maciji.
11 Then Pharaoh called the wise men and the sorcerers. And they also, by Egyptian incantations and certain secrets, did similarly.
Fir’auna kuwa ya kira masu hikima da masu sihiri, sai bokayen Masarawa ma suka yi irin abubuwan nan da bokancinsu.
12 And each one cast down their staffs, and they were turned into serpents. But the staff of Aaron devoured their staffs.
Kowannensu ya jefa sandansa ƙasa, ya kuwa zama maciji. Amma sandan Haruna ya haɗiye sandunansu.
13 And the heart of Pharaoh was hardened, and he did not listen to them, just as the Lord had instructed.
Duk da haka zuciyar Fir’auna ta taurare, bai kuwa saurare su ba, kamar dai yadda Ubangiji ya riga ya faɗa.
14 Then the Lord said to Moses: “The heart of Pharaoh has been hardened; he is not willing to release the people.
Sa’an nan Ubangiji ya ce wa Musa, “Zuciyar Fir’auna taurariya ce, ya ƙi yă bar mutanen su tafi.
15 Go to him in the morning; behold, he will go out to the waters. And you will stand to meet him above the bank of the river. And you will take, in your hand, the staff that was turned into a serpent.
Ka je wurin Fir’auna da safe, yayinda za shi kogi. Ka jira a bakin Nilu don ka sadu da shi, ka ɗauki sandan nan da ya canja zuwa maciji a hannunka.
16 And you will say to him: ‘The Lord God of the Hebrews sent me to you, saying: Release my people in order to sacrifice to me in the desert. And even until the present time, you were not willing to listen.
Sa’an nan ka ce masa, ‘Ubangiji, Allah na Ibraniyawa, ya aiko ni in faɗa maka, Ka bar mutanena su tafi domin su yi mini sujada a hamada. Amma har yanzu ba ka yi biyayya ba.
17 Therefore, thus says the Lord: In this you will know that I am the Lord. Behold, I will strike, with the staff that is in my hand, the water of the river, and it will be turned into blood.
Ga abin da Ubangiji ya ce, da wannan za ka san cewa ni ne Ubangiji. Da sandan da yake hannuna zan bugi ruwan Nilu, zai kuma zama jini.
18 Also, the fishes that are in the river will die, and the waters will be polluted, and the Egyptians will be afflicted when they drink the water of the river.’”
Kifi a ciki Nilu za su mutu, ruwan kuma zai yi ɗoyi; Masarawa ba za su iya shan ruwansa ba.’”
19 The Lord also said to Moses: “Say to Aaron: ‘Take your staff; and extend your hand over the waters of Egypt, and over their rivers and streams and marshes and all the pools of waters, so that they may be turned into blood. And let there be blood throughout all the land of Egypt, as much in vessels of wood as in those of stone.’”
Ubangiji ya ce wa Musa, “Ka ce wa Haruna, ‘Ka ɗauki sandanka, ka miƙa hannunka kan ruwan Masar, kan kogunansu da rafuffukansu da kududdufansu da kuma dukan tafkunansu, za su zama jini.’ Jini zai kasance ko’ina a Masar, har ma a cikin abubuwan ajiyar ruwansu da aka yi da itace da kuma dutse.”
20 And Moses and Aaron did just as the Lord had instructed. And lifting up the staff, he struck the water of the river in the sight of Pharaoh and his servants. And it was turned into blood.
Musa da Haruna suka yi yadda Ubangiji ya umarta. Ya ɗaga sandansa a gaban Fir’auna da bayinsa, ya bugi ruwan Nilu, dukan ruwan kuwa ya zama jini.
21 And the fishes that were in the river died, and the river was polluted, and the Egyptians were not able to drink the water of the river, and there was blood throughout the entire land of Egypt.
Kifin da suke cikin Nilu suka mutu, kogin kuwa ya yi wari sosai yadda Masarawa ba su iya shan ruwan ba. Jini ya bazu ko’ina a Masar.
22 And the sorcerers of the Egyptians, with their incantations, did similarly. And the heart of Pharaoh was hardened, he did not listen to them, just as the Lord had instructed.
Amma bokayen Masar ma suka yi abubuwan nan da sihirinsu, sai zuciyar Fir’auna ta taurare; bai saurari Musa da Haruna ba, kamar dai yadda Ubangiji ya riga ya faɗa.
23 And he turned himself away, and he entered his house, neither did he apply his heart to this turn of events.
A maimakon yă saurara, sai ya juya ya koma fadarsa, bai ma damu da abin da aka yi ba.
24 Then all the Egyptians dug along the borders of the river for water to drink. For they were not able to drink from the water of the river.
Sai dukan Masarawa suka yi ta tonon gefen Nilu don su sami ruwan sha, domin ba su iya shan ruwan kogin ba.
25 And seven days were completed, after the Lord struck the river.
Kwana bakwai suka wuce bayan da Ubangiji ya bugi kogin.