< Esther 7 >

1 And so the king and Haman entered to drink with the queen.
Saboda haka sarki da Haman suka tafi cin abinci wurin sarauniya Esta.
2 And the king said to her again on the second day, after he was warmed with wine, “What is your request, Esther, so that it may be given to you? And what do you want done? Even if you ask for half of my kingdom, you will obtain it.”
Yayinda suke shan ruwan inabi a rana ta biyun nan, sai sarki ya sāke tambaya, “Sarauniya Esta, me kike so? Za a ba ki. Mene ne roƙonki? Ko da rabin masarautata ne, za a ba ki.”
3 She answered him, “If I have found favor in your eyes, O king, and if it pleases you, spare my soul, I ask you, and spare my people, I beg you.
Sai Sarauniya Esta ta amsa ta ce, “In na sami tagomashi a wurinka, ya sarki, in kuma mai girma ya yarda, a bar ni da raina, wannan shi ne roƙona. Ka kuma sa kada a kashe mutanena, wannan ita ce bukata.
4 For I and my people have been handed over to be crushed, to be slain, and to perish. And if we were only being sold as servants and slaves, the evil might be tolerable, and I would have mourned in silence. But now our enemy is one whose cruelty overflows upon the king.”
Gama an sayar da ni da mutanena don a hallaka, a karkashe mu, a kuma ƙi mu. Da a ce an sayar da mu kamar bayi maza da mata ne, da na yi shiru, domin wannan zai zama abin da bai taka kara ya karye ba, har da za a dami sarki a kai.”
5 And king Artaxerxes answered and said, “Who is this, and of what power, that he would dare to do these things?”
Sarki Zerzes ya tambayi Sarauniya Esta ya ce, “Wane ne shi? Ina mutumin da ya yi ƙarfin halin yin wannan karambani?”
6 And Esther said, “This is our most wicked enemy and foe: Haman!” Hearing this, Haman was suddenly dumbfounded, unable to bear the faces of the king and the queen.
Esta ta ce, “Maƙiyi da abokin gāban, shi ne wannan mugun Haman.” Sai Haman ya tsorota a gaban sarki da sarauniya.
7 But the king, being angry, rose up and, from the place of the feast, entered into the arboretum of the garden. Haman likewise rose up to entreat Esther the queen for his soul, for he understood that evil was prepared for him by the king.
Sarki ya tashi cikin fushi, ya bar ruwan inabinsa, ya fita zuwa cikin lambun fada. Amma da Haman ya gane cewa sarki ya riga ya yanke shawara a kan ƙaddararsa, ya dakata domin yă roƙi sarauniya Esta saboda ransa.
8 When the king returned from the arboretum of the garden and entered into the place of the feast, he found Haman collapsed on the couch on which Esther lay, and he said, “And now he wishes to oppress the queen, in my presence, in my house!” The word had not yet gone out of the king’s mouth, and immediately they covered his face.
Sarki yana dawowa daga lambun fada zuwa babban zauren liyafan ke nan, sai ga Haman ya fāɗi a kan shimfiɗar da Esta take zaune. Sarki ya tā da murya da ƙarfi ya ce, “Har ma zai ci mutuncin sarauniya yayinda take tare da ni a cikin gida?” Sarki bai ma rufe baki ba, sai bayin sarki suka rufe fuskar Haman.
9 And Harbona, one of the eunuchs who stood in ministry to the king, said, “Behold the wood, which he had prepared for Mordecai, who spoke up on behalf of the king, stands in Haman’s house, having a height of fifty cubits.” The king said to him, “Hang him from it.”
Sai Harbona, ɗaya daga cikin bābānni masu yi wa sarki hidima ya ce, “Akwai wurin rataye mai laifi da tsayinsa ya kai ƙafa saba’in da biyar yana nan tsaye kusa da gidan Haman. Ya gyara shi ne domin a rataye Mordekai, wanda ya yi cece sarki wanda ya tone makircin masu niyya su hallaka sarki.” Sai sarki ya ce, “Ku rataye shi a kansa!”
10 And so Haman was hanged on the gallows, which he had prepared for Mordecai, and the king’s anger was quieted.
Saboda haka suka rataye Haman a kan wurin rataye mai laifin da shi Haman ya shirya saboda Mordekai. Sa’an nan sarki ya huce.

< Esther 7 >