< Deuteronomy 26 >
1 “And when you will have entered into the land which the Lord your God will give to you to possess, and when you will have obtained it and are living within it:
Sa’ad da kuka shiga ƙasar da Ubangiji Allahnku yake ba ku gādo, kuka mallake ta, kuka kuma zauna a cikinta,
2 you shall take the first of all your crops, and place them in a basket, and you shall travel to the place which the Lord your God will choose, so that his name may be invoked there.
sai ku ɗauki’ya’yan fari na dukan amfanin gonar ƙasar da Ubangiji Allahnku yake ba ku, ku zuba a kwando. Sa’an nan ku je wurin da Ubangiji Allahnku ya zaɓa yă zama mazauni don Sunansa,
3 And you shall approach the priest who will be in those days, and you shall say to him: ‘I profess this day, before the Lord your God, that I have entered into the land about which he swore to our fathers that he would give it to us.’
ku faɗa wa firist da yake aiki a lokacin, “Na sakankance yau ga Ubangiji Allahnka, cewa na zo ƙasar da Ubangiji ya rantse zai ba wa kakanninmu.”
4 And the priest, taking up the basket from your hand, shall place it before the altar of the Lord your God.
Firist ɗin zai karɓi kwandon daga hannuwanku yă sa shi a ƙasa a gaban bagaden Ubangiji Allahnku.
5 And you shall say, in the sight of the Lord your God: ‘The Syrian pursued my father, who descended into Egypt, and he sojourned there in a very small number, and he increased into a great and strong nation and into an innumerable multitude.
Sa’an nan za ku furta a gaban Ubangiji Allahnku cewa, “Mahaifina mutumin Aram ne mai yawo, ya gangara zuwa Masar da mutane kaɗan, ya zauna a can, ya kuma zama babban al’umma, mai iko da kuma mai yawa.
6 And the Egyptians afflicted us, and they persecuted us, imposing upon us the most grievous burdens.
Amma Masarawa suka wulaƙanta mu suka sa muka sha wahala, suna sa mu aikin dole.
7 And we cried out to the Lord, the God of our fathers. He heard us, and he looked with favor upon our humiliation, and hardship, and distress.
Sai muka yi kuka ga Ubangiji Allahn kakanninmu, Ubangiji kuwa ya ji kukanmu, ya kuma azabar da muke sha, da wahalar da muke sha, da danniyar da suke yin mana.
8 And he led us away from Egypt, with a strong hand and an outstretched arm, with a mighty terror, with signs and wonders.
Sai Ubangiji ya fitar da mu daga Masar da hannu mai ƙarfi da kuma iko, da razana mai girma da kuma alamu banmamaki da al’ajabai.
9 And he led us into this place, and he delivered to us the land flowing with milk and honey.
Ya kawo mu wannan wuri, ya kuma ba mu wannan ƙasa, ƙasa mai zub da madara da kuma zuma;
10 And because of this, I now offer the first fruits of the land which the Lord has given to me.’ And you shall leave them in the sight of the Lord your God, and you shall adore the Lord your God.
yanzu kuwa na kawo’ya’yan fari na gonar da kai, ya Ubangiji ka ba ni.” Sai ku sa kwandon a gaban Ubangiji Allahnku, sa’an nan ku rusuna a gabansa.
11 And you shall feast on all the good things which the Lord your God will give to you and to your house: you, and the Levite, and the new arrival who is with you.
Ku da Lawiyawa da baƙin da suke a cikinku, za ku yi murna cikin dukan abubuwa masu kyau da Ubangiji Allahnku ya ba ku tare da gidanku.
12 When you will have completed the tithing of all your crops, in the third year of tithes, you shall give it to the Levite, and to the new arrival, and to the orphan, and to the widow, so that they may eat within your gates and be satisfied.
Sa’ad da kuka gama fitar da kashi ɗaya bisa goma na dukan amfanin gona a shekara ta uku, shekarar zakka, za ku ba da su ga Balawe, baƙo, maraya da kuma gwauruwa, don su ci a cikin garuruwanku su ƙoshi.
13 And you shall say, in the sight of the Lord your God: ‘I have taken what was sanctified from my house, and I have given it to the Levite, and to the new arrival, and to the orphan and the widow, just as you have commanded me. I have not transgressed your commandments, nor have I forgotten your precepts.
Sa’an nan ku faɗa wa Ubangiji Allahnku, “Na cire tsattsarkan rabo daga gidana na kuma ba wa Balawe, baƙo, maraya da gwauruwa, bisa ga dukan abin da ka umarta. Ban ja gefe daga umarnanka ko in manta da wani a cikinsu ba.
14 I have not eaten from these things in my grief, nor have I separated them due to any kind of uncleanness, nor have I expended any of these things in funerals. I have obeyed the voice of the Lord my God, and I have done all things just as you have instructed me.
Ban ci wani daga cikin tsattsarkan rabo yayinda nake makoki, ko in cire wani rabo mai tsarki yayinda nake marar tsarki, ko in miƙa wani sashensa ga matattu ba. Na yi biyayya ga Ubangiji Allahna, na aikata kome da ka umarce ni.
15 Look with favor from your sanctuary and from your lofty habitation amid the heavens, and bless your people Israel and the land which you have given to us, just as you swore to our fathers, a land flowing with milk and honey.’
Ka duba ƙasa daga sama, mazauninka mai tsarki, ka albarkace mutanenka Isra’ila da kuma ƙasar da ka ba mu kamar yadda ka yi wa kakanninmu alkawari da rantsuwa, ƙasa mai zub da madara da zuma.”
16 Today the Lord your God has instructed you to carry out these commandments and judgments, and to keep and fulfill them, with all your heart and with all your soul.
Yau Ubangiji Allahnku ya umarce ku ku bi waɗannan ƙa’idodi da kuma dokoki, cikin natsuwa ku kiyaye su da dukan zuciyarku da kuma dukan ranku.
17 Today, you have chosen the Lord to be your God, so that you may walk in his ways, and keep his ceremonies and commandments and judgments, and obey his command.
Kun furta a wannan rana cewa Ubangiji shi ne Allahnku, cewa za ku kuma yi tafiya a hanyoyinsa, cewa za ku kiyaye ƙa’idodinsa, umarnansa da kuma dokokinsa, kuka kuma ce za ku yi masa biyayya.
18 Today, the Lord has chosen you, so that you may be his particular people, just as he has spoken to you, and so that you may keep all his precepts,
Ubangiji kuwa ya furta a wannan rana cewa ku mutanensa ne, mallakarsa kamar yadda ya yi alkawari, da kuma cewa za ku kiyaye dukan umarnansa.
19 and so that he may cause you to be more exalted than all the nations which he has created, for the sake of his own praise and name and glory, in order that you may be a holy people for the Lord your God, just as he has spoken.”
Ya furta cewa zai sa ku zama masu yabo, masu suna, masu daraja, fiye da dukan al’umman da ya yi. Za ku zama jama’a tsattsarka ta Ubangiji Allahnku, kamar yadda ya yi alkawari.