< Acts 2 >

1 And when the days of Pentecost were completed, they were all together in the same place.
Da ranar Fentikos ta zo, dukansu suna tare wuri daya.
2 And suddenly, there came a sound from heaven, like that of a wind approaching violently, and it filled the entire house where they were sitting.
Nan da nan sai ga wata kara daga sama kamar ta babbar iska, kuma ta sauko ta cika duka gidan inda suke zaune.
3 And there appeared to them separate tongues, as if of fire, which settled upon each one of them.
Sai ga wasu harsuna kamar na wuta sun bayyana a garesu aka rarraba su, kuma suka zauna bisa kowannensu.
4 And they were all filled with the Holy Spirit. And they began to speak in various languages, just as the Holy Spirit bestowed eloquence to them.
Dukansu suka cika da Ruhu Mai Tsarki suka fara magana da wadansu harsuna, yadda Ruhu ya ba su iko su yi magana.
5 Now there were Jews staying in Jerusalem, pious men from every nation that is under heaven.
A lokacin akwai Yahudawa dake zaune a Urushalima, mutanen Allah, daga kowace kasa karkashin sama.
6 And when this sound occurred, the multitude came together and was confused in mind, because each one was listening to them speaking in his own language.
Da suka ji wannan kara jama'a duk suka taru suka rude saboda kowannensu ya ji suna magana da harshensa.
7 Then all were astonished, and they wondered, saying: “Behold, are not all of these who are speaking Galileans?
Suka yi mamaki matuka; suka ce, ''Lallai, wadannan duka ba Galiliyawa ba ne?
8 And how is it that we have each heard them in our own language, into which we were born?
Yaya mu ke jinsu duka, kowannensu na magana a cikin harshen da aka haife mu?
9 Parthians and Medes and Elamites, and those who inhabit Mesopotamia, Judea and Cappadocia, Pontus and Asia,
Fisiyawa da Mediyawa da Elimawa, da Yahudawa da Kafadokiya, cikin Fontus da Asiya,
10 Phrygia and Pamphylia, Egypt and the parts of Libya which are around Cyrene, and new arrivals of the Romans,
cikin Firgia da Bamfiliya, cikin Masar da yankunan Libiya ta wajen Sur, da baki daga Roma,
11 likewise Jews and new converts, Cretans and Arabs: we have heard them speaking in our own languages the mighty deeds of God.”
Yahudawa da tubabbun cikin Yahudanci, Kiretawa da Larabawa, duk munji su suna fadi a harshenmu game da manyan ayyukan Allah.''
12 And they were all astonished, and they wondered, saying to one another: “But what does this mean?”
Dukansu suka yi mamaki suka rikice; suka ce da junansu, ''Menene ma'anar wannan?''
13 But others mockingly said, “These men are full of new wine.”
Amma wasu suka yi ba'a suka ce, ''Sun bugu ne da sabon ruwan inabi.''
14 But Peter, standing up with the eleven, lifted up his voice, and he spoke to them: “Men of Judea, and all those who are staying in Jerusalem, let this be known to you, and incline your ears to my words.
Amma Bitrus ya tashi tare da sha dayan, ya daga murya ya ce da su, ''Mutanen Yahuda da dukanku dake zaune a Urushalima, bari ku san wannan; ku saurari maganata.
15 For these men are not inebriated, as you suppose, for it is the third hour of the day.
Domin wadannan mutanen ba buguwa suka yi ba yadda kuke zato, domin yanzu karfe tara ne na safe kawai.
16 But this is what was spoken of by the prophet Joel:
Amma wannan shine abinda aka fada ta wurin annabi Yowel.
17 ‘And this shall be: in the last days, says the Lord, I will pour out, from my Spirit, upon all flesh. And your sons and your daughters shall prophesy. And your youths shall see visions, and your elders shall dream dreams.
Allah ya ce, 'Haka zai kasance a kwanakin karshe, zan zubo Ruhuna a kan dukan mutane, 'ya'yanku maza da mata za su yi anabci, kuma samarinku za su ga wahayoyi, kuma tsofaffinku za su yi mafarkai.
18 And certainly, upon my men and women servants in those days, I will pour out from my Spirit, and they shall prophesy.
Haka kuma a bisa bayi na maza da mata, a kwanakin nan zan zubo da Ruhuna, kuma za su yi anabci.
19 And I will bestow wonders in heaven above, and signs on earth below: blood and fire and the vapor of smoke.
Zan nuna al'ajibai a sararin sama da kuma alamu a bisa duniya, jini da wuta, da girgije.
20 The sun shall be turned into darkness and the moon into blood, before the great and manifest day of the Lord arrives.
Rana zata juya ta koma duhu kuma wata ya koma jini, kafin Babbar ranan nan ta Ubangiji ta zo.
21 And this shall be: whoever shall invoke the name of the Lord will be saved.’
Zai kuma zama dukan wanda ya kira ga sunan Ubangiji zai sami ceto.
22 Men of Israel, hear these words: Jesus the Nazarene is a man confirmed by God among you through the miracles and wonders and signs that God accomplished through him in your midst, just as you also know.
Mutanen Isra'ila, ku saurari wadannan magana. Yesu Banazare, mutumin da Allah ya tabbatar da shi gareku ta wurin manyan ayyuka da ban mamaki da alamu da Allah ya yi ta wurinsa a tsakiyarku, kamar yadda ku da kanku kuka sani.
23 This man, under the definitive plan and foreknowledge of God, was delivered by the hands of the unjust, afflicted, and put to death.
Saboda tabbataccen shiri da riga sani na Allah, aka bayar dashi, ku kuma, ta hannun mutane 'yan tawaye, kuka gicciye shi kuma kuka kashe shi.
24 And he whom God has raised up has broken the sorrows of Hell, for certainly it was impossible for him to be held by it. (questioned)
Wanda Allah ya tayar, bayan ya cire zafin mutuwa daga gareshi, saboda ba zai yiwu ba ta rike shi.
25 For David said about him: ‘I foresaw the Lord always in my sight, for he is at my right hand, so that I may not be moved.
Gama, game da shi, 'Ina ganin Ubangiji a gabana ko yaushe, domin yana gefen hannun damana saboda kada in firgita.
26 Because of this, my heart has rejoiced, and my tongue has exulted. Moreover, my flesh shall also rest in hope.
Saboda haka zuciyata na farin ciki harshena yana yin murna. Kuma, jikina zai zauna gabagadi.
27 For you will not abandon my soul to Hell, nor will you allow your Holy One to see corruption. (Hadēs g86)
Gama ba za ka watsar da raina a lahira ba, ba kuwa za ka bar Mai Tsarkinka ya ga ruba ba. (Hadēs g86)
28 You have made known to me the ways of life. You will completely fill me with happiness by your presence.’
Ka bayyana mani hanyar rai; da fuskarka zaka cika ni da farin ciki.
29 Noble brothers, permit me to speak freely to you about the Patriarch David: for he passed away and was buried, and his sepulcher is with us, even to this very day.
'Yan'uwa, zan yi magana da ku gabagadi game da baba Dauda: ya mutu kuma aka bizne shi, kuma kabarinsa na nan tare da mu har yau.
30 Therefore, he was a prophet, for he knew that God had sworn an oath to him about the fruit of his loins, about the One who would sit upon his throne.
Domin haka, don shi annabi ne kuma ya san Allah ya yi masa alkawari da rantsuwa cewa daga cikin zuriyarsa zai sanya wani bisa kursiyinsa.
31 Foreseeing this, he was speaking about the Resurrection of the Christ. For he was neither left behind in Hell, nor did his flesh see corruption. (Hadēs g86)
Ya hango wannan al'amari kuma ya yi magana game da tashin Almasihu, 'Ba ayi watsi da shi ba a lahira, kuma jikinsa bai ga rubewa ba.' (Hadēs g86)
32 This Jesus, God raised up again, and of this we are all witnesses.
Wannan Yesun - Allah ya tashe shi, wanda dukanmu shaidu ne.
33 Therefore, being exalted to the right hand of God, and having received from the Father the Promise of the Holy Spirit, he poured this out, just as you now see and hear.
Saboda haka yadda aka tashe shi zuwa hannun dama na Allah kuma ya karbi alkawarin Ruhu Mai Tsarki daga wurin Uba, shine ya zubo mana wannan da kuke gani kuma kuke ji.
34 For David did not ascend into heaven. But he himself said: ‘The Lord said to my Lord: Sit at my right hand,
Dauda bai hau zuwa sama ba, amma ya ce, ''Ubangiji ya ce wa Ubangijina, “Zauna hannun dama na,
35 until I make your enemies your footstool.’
har sai na maida makiyanka abin takawar sawunka.'''
36 Therefore, may the entire house of Israel know most certainly that God has made this same Jesus, whom you crucified, both Lord and Christ.”
Saboda haka, bari gidan Isra'ila su sani tabbas wannan Yesun wanda kuka gicciye, Allah ya maishe shi Ubangiji da kuma Almasihu.
37 Now when they had heard these things, they were contrite in heart, and they said to Peter and to the other Apostles: “What should we do, noble brothers?”
Da suka ji haka sai suka soku a zukatansu, suka cewa Bitrus da sauran manzanni, '''Yan'uwa me za mu yi?''
38 Yet truly, Peter said to them: “Do penance; and be baptized, each one of you, in the name of Jesus Christ, for the remission of your sins. And you shall receive the gift of the Holy Spirit.
Sai Bitrus ya ce masu, ''Ku tuba ayi wa kowannenku baftisma, cikin sunan Yesu Almasihu domin gafarar zunubanku, kuma za ku karbi baiwar Ruhu Mai Tsarki.
39 For the Promise is for you and for your sons, and for all who are far away: for whomever the Lord our God will have called.”
Domin alkawarin a gareku ne da 'ya'yanku da duk wadanda ke nesa, dukan iyakar mutanen da Ubangiji Allahnmu zai kira.''
40 And then, with very many other words, he testified and he exhorted them, saying, “Save yourselves from this depraved generation.”
Da maganganu da yawa ya ba da shaida kuma ya karfafa su; ya ce, ''Ku ceci kan ku daga wannan muguwar tsara.''
41 Therefore, those who accepted his discourse were baptized. And about three thousand souls were added on that day.
Sai suka karbi maganar sa kuma aka yi ma su baftisma, a wannan rana kuma aka sami karin rayuka wajen dubu uku.
42 Now they were persevering in the doctrine of the Apostles, and in the communion of the breaking of the bread, and in the prayers.
Su ka cigaba cikin koyarwar manzanni da zumunta, cikin kakkaryawar gurasa da kuma cikin addu'o'i.
43 And fear developed in every soul. Also, many miracles and signs were accomplished by the Apostles in Jerusalem. And there was a great awe in everyone.
Tsoro ya sauko bisa kowane rai, kuma aka yi abubuwan ban mamaki da alamu da yawa ta wurin manzannin.
44 And then all who believed were together, and they held all things in common.
Duka wadanda suka ba da gaskiya suna tare kuma komai nasu na kowanensu ne,
45 They were selling their possessions and belongings, and dividing them to all, just as any of them had need.
kuma suka saida kadarorinsu da mallakarsu kuma suka rarrabawa kowa, bisa ga irin bukatar da kowannensu yake da ita.
46 Also, they continued, daily, to be of one accord in the temple and to break bread among the houses; and they took their meals with exultation and simplicity of heart,
A kowace rana suka cigaba tare da nufi daya a cikin haikali, suna kakkarya gurasa a gidaje, kuma suna raba abinci tsakaninsu cikin farin ciki da tawali'u a zuciya;
47 praising God greatly, and holding favor with all the people. And every day, the Lord increased those who were being saved among them.
Suna yabon Allah kuma suna da tagomashi a gaban dukan mutane. Ubangiji kuma kullum yana kara masu wadanda suke samun ceto.

< Acts 2 >