< Acts 14 >

1 Now it happened in Iconium that they entered together into the synagogue of the Jews, and they spoke in such a way that a copious multitude of both Jews and Greeks believed.
A lokacin da Bulus da Barnaba sun shiga garin Ikoniya suka shiga majami'an Yahudawa suka yi wa'azi yadda har mutane da yawa daga cikin Yahudawa da Hellinawa suka ba da gaskiya.
2 Yet truly, the Jews who were unbelieving had incited and enflamed the souls of the Gentiles against the brothers.
Amma Yahudawa da basu yi biyayya ba, suka zuga al'umman har suka yi fushi da 'yan'uwan.
3 And so, they remained for a long time, acting faithfully in the Lord, offering testimony to the Word of his grace, providing signs and wonders done by their hands.
Suka zauna a wurin na tsawon lokaci, suna yni maganarsu gabagadi da ikon Ubangiji, yana kuma shaidar sakon alherinsa. Ya yi wannan ta wurin alamu da al'ajibai ta hannun Bulus da Barnaba.
4 Then the multitude of the city was divided. And certainly, some were with the Jews, yet truly others were with the Apostles.
Saboda haka mutanen garin sun rabu: wadansun su suka bi ra'ayin Yahudawa, wasu kuwa sun bi manzannin.
5 Now when an assault had been planned by the Gentiles and the Jews with their leaders, so that they might treat them with contempt and stone them,
Al'umman garin da Yahudawa sun nemi jan hankali shugabanninsu, don su wulakanta Bulus da Barnaba, su jajjefe su,
6 they, realizing this, fled together to Lystra and Derbe, cities of Lycaonia, and to the entire surrounding region.
da suka gane haka suka gudu zuwa biranen Likoniya, Listira da Darbe, da garuruwa wadanda ke kewaye da su,
7 And they were evangelizing in that place.
a can suka yi wa'azin bishara.
8 And a certain man was sitting at Lystra, disabled in his feet, lame from his mother’s womb, who had never walked.
A Listira akwai wani wanda ke zaune bai taba tashi da kafafunsa ba, don shi gurgu ne tun daga haihuwa.
9 This man heard Paul speaking. And Paul, gazing at him intently, and perceiving that he had faith, so that he might be healed,
Wannan mutumin ya ji Bulus yana magana. Bulus ya kafa masa ido, ya gane mutumin na da bangaskiya da za a warkar da shi. Sai ya ce masa da murya mai karfi, “Tashi ka tsaya akan kafafunka”
10 said with a loud voice, “Stand upright upon your feet!” And he leaped up and walked around.
Sai mutumin ya yi tsalle ya fara tafiya da kafafunsa, yana yawo.
11 But when the crowds had seen what Paul had done, they lifted up their voice in the Lycaonian language, saying, “The gods, having taken the likenesses of men, have descended to us!”
Da jama'an garin sun ga abin da Bulus ya yi, suka tada muryarsu suna cewa da Likoniyanci, “Ai alloli sun ziyarce mu daga sama, da kamanin mutane.”
12 And they called Barnabas, ‘Jupiter,’ yet truly they called Paul, ‘Mercury,’ because he was the lead speaker.
Suna kiran Barnaba da sunan “Zafsa,” Bulus kuwa suka kira shi da sunan “Hamisa” domin shine yafi yin magana.
13 Also, the priest of Jupiter, who was outside the city, in front of the gate, bringing in oxen and garlands, was willing to offer sacrifice with the people.
Sai firist din zafsa wanda dakin yin masa sujada na kofar birni; ya kawo bijimai biyu da furannin da aka saka su kamar gammo; shi da jama'arsa suna so su yi masa hadaya.
14 And as soon as the Apostles, Barnabas and Paul, had heard this, tearing their tunics, they leapt into the crowd, crying out
Amma da manzannin, wato Barnaba da Bulus, su ka ji labarin, suka yage rigunansu, suka hanzarta zuwa gun taron mutanen.
15 and saying: “Men, why would you do this? We also are mortals, men like yourselves, preaching to you to be converted, from these vain things, to the living God, who made heaven and earth and the sea and all that is in them.
Suna ta cewa, “Kuji! Ku mutane don me kuke wannan abin? Mu fa mutane ne kamarku. Mun kawo maku labari mai dadi ne, da cewa, ku rabu da abubuwa marar amfani, ku koma ga Allah mai rai, wanda ya hallici sama da kasa da teku da dukan abubuwa da ke cikinsu.
16 In previous generations, he permitted all nations to walk in their own ways.
A da dai ya bar mutane su yi abinda suka ga dama.
17 But certainly, he did not leave himself without testimony, doing good from heaven, giving rains and fruitful seasons, filling their hearts with food and gladness.”
Duk da haka, bai bar kansa ba tare da shaida ba, don yana bada abubuwa masu kyau, yana ba ku ruwan sama, lokatai masu albarka, ya cika ranku da abinci da farin ciki.”
18 And by saying these things, they were barely able to restrain the crowds from immolating to them.
Duk da wadannan kalmomin da kyar, Bulus da Barnaba suka iya tsayar da su daga yi masu hadaya.
19 Now certain Jews from Antioch and Iconium arrived there. And having persuaded the crowd, they stoned Paul and dragged him outside of the city, thinking him to be dead.
Amma wasu Yahudawa daga Antakiya da wasunsu daga Ikoniya suka rinjayi tarun jama'ar. Suka jajjefi Bulus suka ja shi zuwa wajen garin, suna ganin kamar ya mutu.
20 But as the disciples were standing around him, he got up and entered the city. And the next day, he set out with Barnabas for Derbe.
Duk da haka da almajirai suka kewaye shi a tsaitsaye, sai ya tashi ya koma cikin garin. Washegari, ya tafi Darba tare Barnaba.
21 And when they had evangelized that city, and had taught many, they returned again to Lystra and to Iconium and to Antioch,
Bayan sun yi wa'azin bishara a wannan birnin suka kuma sami almajirai da yawa, suka dawo Listira, da Ikoniya da Antikiya.
22 strengthening the souls of the disciples, and exhorting them that they should remain always in the faith, and that it is necessary for us to enter into the kingdom of God through many tribulations.
Suna karfafa zuciyar almajiran su rike bangaskiyarsu, su ci gaba da ita, suna ce masu, “Ta wurin jimrewa mai yawa zamu shiga mulkin Allah, don haka dole ne mu sha wahala.”
23 And when they had established priests for them in each church, and had prayed with fasting, they commended them to the Lord, in whom they believed.
Da suka zabar masu dattawa a kowace iklisiya, sai suka yi addu'oi da azumi, suka mika su ga Ubangiji, ga wanda suka gaskanta a gareshi.
24 And traveling by way of Pisidia, they arrived in Pamphylia.
Sa'annan sun bi ta Bisidiya suka kai Bamfiliya.
25 And having spoken the word of the Lord in Perga, they went down into Attalia.
Da suka yi maganarsu a Biriya, sun wuce zuwa har Italiya.
26 And from there, they sailed to Antioch, where they had been commended to the grace of God for the work which they had now accomplished.
Ta jirgin ruwa zuwa Antakiya, a nan ne aka mika su ga alherin Allah don aikin da suka gama a yanzu.
27 And when they had arrived and had gathered together the church, they related what great things God had done with them, and how he had opened the door of faith to the Gentiles.
Da isowarsu Antakiya sun tara 'yan iklisiya a wuri daya, sun ba da labarin dukan abin da Allah ya yi ta wurinsu. Da yadda Ya bude kofa a wurin al'ummai ta bangaskiya.
28 And they remained for no small amount of time with the disciples.
Sun zauna tare da almajiran na tsawon lokaci.

< Acts 14 >