< 2 Timothy 1 >

1 Paul, an Apostle of Jesus Christ through the will of God, in accord with the promise of the life which is in Christ Jesus,
Bulus, manzon Almasihu Yesu ta wurin nufin Allah, bisa ga alkawarin rai da ke cikin Almasihu Yesu,
2 to Timothy, most beloved son. Grace, mercy, peace, from God the Father and from Christ Jesus our Lord.
zuwa ga Timoti, kaunataccen da: Alheri, jinkai, da salama daga Allah Uba da Almasihu Yesu Ubangijinmu.
3 I give thanks to God, whom I serve, as my forefathers did, with a pure conscience. For without ceasing I hold the remembrance of you in my prayers, night and day,
Na gode wa Allah, wanda na ke bautawa tun daga kakannina, da lamiri mai tsabta, sa'adda na ke tuna wa da kai cikin addu'o'ina koyaushe (dare da rana).
4 desiring to see you, recalling your tears so as to be filled with joy,
Sa'adda na tuna da hawayenka, na yi marmarin ganinka, saboda in cika da farin ciki.
5 calling to mind the same faith, which is in you unfeigned, which also first dwelt in your grandmother, Lois, and in your mother, Eunice, and also, I am certain, in you.
An tunashshe ni game da sahihiyar bangaskiyarka, wadda ta samo asali daga kakarka Loyis da mahaifiyarka Afiniki. Na kuma tabbata ta na zaune a cikinka.
6 Because of this, I admonish you to revive the grace of God, which is in you by the imposition of my hands.
Wannan shine dalilin da ni ke tunashshe ka cewa ka sake rura baiwar Allah da ke cikinka wadda ka samu sa'adda na dibiya maka hannuwana.
7 For God has not given us a spirit of fear, but of virtue, and of love, and of self-restraint.
Domin Allah bai ba mu ruhun tsoro ba, amma na iko da kauna da kamun kai.
8 And so, do not be ashamed of the testimony of our Lord, nor of me, his prisoner. Instead, collaborate with the Gospel in accord with the virtue of God,
Saboda haka kada ka ji kunyar shaida ga me da Ubangijinmu, ko ni, Bulus, daurarrensa. Maimakon haka, ka zama a shirye ka sha wahala domin bishara bisa ga ikon Allah.
9 who has freed us and has called us to his holy vocation, not according to our works, but according to his own purpose and grace, which was given to us in Christ Jesus, before the ages of time. (aiōnios g166)
Allah ne ya cecemu kuma ya kira mu da kira mai tsarki. Ya yi wannan, ba ta wurin ayyukanmu ba, amma ta wurin shirinsa da alherinsa. Ya ba mu wadannan abubuwan a cikin Almasihu Yesu kafin farkon zamanai. (aiōnios g166)
10 And this has now been made manifest by the illumination of our Savior Jesus Christ, who certainly has destroyed death, and who has also illuminated life and incorruption through the Gospel.
Amma yanzu an bayyana ceton Allah ta wurin bayyanuwar mai cetonmu Almasihu Yesu. Almasihu ne ya kawo karshen mutuwa ya kuma kawo rai marar karshe da ya bayyana ta wurin bishara.
11 Of this Gospel, I have been appointed a preacher, and an Apostle, and a teacher of the Gentiles.
Domin wannan, an zabe ni mai wa'azi, manzo da mallami zuwa ga al'ummai.
12 For this reason, I also suffer these things. But I am not confounded. For I know in whom I have believed, and I am certain that he has the power to preserve what was entrusted to me, unto that day.
Domin wannan dalili na ke shan wahalar wadannan abubuwa. Amma ban ji kunya ba, domin na san shi, wanda na gaskanta. Na sakankance zai iya adana abinda na mika masa har zuwa ranan nan.
13 Hold to the kind of sound words that you have heard from me in the faith and love which is in Christ Jesus.
Ka adana misalin amintattun sakwanni da ka ji daga gare ni, ta wurin bangaskiya da kauna da ke cikin Almasihu Yesu.
14 Guard the good entrusted to you through the Holy Spirit, who lives within us.
Abu mai kyau da Allah ya danka maka, ka tsare shi ta wurin Ruhu Mai Tsarki, da ke zaune a cikinmu.
15 Know this: that all those who are in Asia have turned away from me, among whom are Phigellus and Hermogenes.
Ka dai sani, dukkan wadanda su ke zama a Asiya sun juya mani baya. A cikin kungiyar akwai Fijalas da Harmajanas.
16 May the Lord have mercy on the house of Onesiphorus, because he has often refreshed me, and he has not been ashamed of my chains.
Bari Ubangiji ya yi wa iyalin Onisifaras jinkai, domin ya na yawan yi mani hidima, kuma ba ya jin kunyar sarkata.
17 Instead, when he had arrived in Rome, he anxiously sought me and found me.
Maimakon haka, sa'adda ya ke a Roma, ya neme ni da kokarin gaske, ya kuma same ni.
18 May the Lord grant to him to obtain mercy from the Lord in that day. And you know well in how many ways he has ministered to me at Ephesus.
Bari Ubangiji ya sa, ya sami jinkai daga gare shi a wannan rana. Dukkan hanyoyin da ya taimake ni a kasar Afisa, kun sani sarai.

< 2 Timothy 1 >