< 1 Samuel 31 >
1 Now the Philistines were fighting against Israel. And the men of Israel fled before the face of the Philistines, and they fell down slain on mount Gilboa.
Filistiyawa suka yi yaƙi da Isra’ilawa, sai Isra’ilawa suka gudu a gaban Filistiyawa, aka kuma karkashe da yawa a dutsen Gilbowa.
2 And the Philistines rushed upon Saul, and upon his sons, and they struck down Jonathan, and Abinadab, and Malchishua, the sons of Saul.
Filistiyawa suka abka wa Shawulu da’ya’yansa maza, suka kashe’ya’yan Shawulu. Yonatan da Abinadab da Malki-Shuwa.
3 And the entire weight of the battle was turned against Saul. And the men who were archers pursued him. And he was severely wounded by the archers.
Yaƙin ya yi zafi ƙwarai kewaye da Shawulu, har maharba suka ji masa ciwo sosai bayan sun sha ƙarfinsa.
4 Then Saul said to his armor bearer, “Draw your sword and strike me, otherwise these uncircumcised may come and kill me, mocking me.” And his armor bearer was not willing. For he had been struck with an exceedingly great fear. And so, Saul took his own sword, and he fell upon it.
Sai Shawulu ya ce wa mai ɗauka masa makami, “Ka zare takobinka ka soke ni, kada waɗannan marasa kaciya su zo su ci mini mutunci, su kashe ni.” Amma mai ɗaukan makaman bai yarda ba don ya ji tsoro sosai. Sai Shawulu ya zāre takobinsa ya soki kansa.
5 And when his armor bearer had seen this, namely, that Saul had died, he too fell upon his sword, and he died with him.
Da mai ɗaukar makamai ya ga Shawulu ya mutu, sai shi ma ya zāre takobinsa ya soki kansa ya mutu.
6 Therefore, Saul died, and his three sons, and his armor bearer, and all his men, on the same day together.
Shawulu da yaransa uku da mai ɗaukar makamansa da dukan mutanensa suka mutu a rana ɗaya.
7 Then, seeing that the men of the Israelites had fled, and that Saul had died with his sons, the men of Israel who were across the valley or beyond the Jordan abandoned their cities, and they fled. And the Philistines went and lived there.
Sa’ad da Isra’ilawa na bakin kwari da waɗanda suke hayin Urdun suka ga sojojin Isra’ila suna gudu, Shawulu da yaransa uku kuma duk sun mutu, sai suka bar mallakansu suka sheƙa da gudu. Filistiyawa kuwa suka zo suka mamaye wuraren.
8 Then, when the next day arrived, the Philistines came, so that they might despoil the slain. And they found Saul and his three sons lying on mount Gilboa.
Kashegari, da Filistiyawa suka zo domin su washe kayan matattun, sai suka tarar Shawulu da’ya’yansa uku duk sun mutu, a dutsen Gilbowa.
9 And they cut off the head of Saul. And they despoiled him of the armor, and they sent it into the land of the Philistines all around, so that it might be announced in the temples of the idols and among their people.
Suka sare kansa suka tuɓe makamansa, suka aika manzanni a dukan ƙasar Filistiyawa, su ba da labarin a haikalin allolinsu da cikin mutanensu.
10 And they placed his armor in the temple of Ashtaroth. But his body they suspended on the wall of Bethshan.
Suka ajiye makaman Shawulu a cikin haikalin gumakan Ashtarot. Suka kafa gawarsa a kan katanga Bet-Shan.
11 And when the inhabitants of Jabesh Gilead had heard all that the Philistines had done to Saul,
Sa’ad da mutanen Yabesh Gileyad suka sami labarin abin da Filistiyawa suka yi wa Shawulu.
12 all the most valiant men rose up, and they walked all night, and they took the body of Saul and the bodies of his sons from the wall of Bethshan. And they went to Jabesh Gilead, and they burned them there.
Sai dukan jarumawansu suka tashi cikin dare suka tafi Bet-Shan suka saukar da gawar Shawulu da na’ya’yansa daga kan katangan Bet-Shan suka tafi Yabesh inda suka ƙone su.
13 And they took their bones, and they buried them in the forest of Jabesh. And they fasted for seven days.
Sai suka kwashi ƙasusuwansu suka binne a gindin itace tsamiya a Yabesh, suka kuma yi azumi kwana bakwai.