< 1 Samuel 23 >

1 And they reported to David, saying, “Behold, the Philistines are fighting against Keilah, and they are plundering the grain stores.”
Sa’ad da aka ce wa Dawuda, “Duba ga Filistiyawa suna yaƙi da mutanen Keyila, suna kwashe musu hatsi a masussukai.”
2 Therefore, David consulted the Lord, saying, “Shall I go and strike down these Philistines?” And the Lord said to David, “Go, and you shall strike down the Philistines, and you shall save Keilah.”
Sai Dawuda ya nemi nufin Ubangiji, ya ce, “In tafi in fāɗa wa Filistiyawa da yaƙi?” Ubangiji kuwa ya ce masa, “Jeka ka yi yaƙi da Filistiyawa, ka ceci Keyila.”
3 And the men who were with David said to him, “Behold, we continue in fear here in Judea; how much more so, if we go into Keilah against the troops of the Philistines?”
Amma mutanen Dawuda suka ce masa, “Ga shi, a nan ma a Yahuda muna jin tsoro, balle mu tafi Keyila mu yi yaƙi da sojojin Filistiyawa!”
4 Therefore, David consulted the Lord again. And responding, he said to him: “Rise up, and go into Keilah. For I will deliver the Philistines into your hand.”
Dawuda ya sāke nemi nufin Ubangiji, sai Ubangiji ya ce masa, “Tashi ka gangara zuwa Keyila, gama zan ba da Filistiyawa a hannunka.”
5 Therefore, David and his men went into Keilah. And they fought against the Philistines, and they took away their cattle, and they struck them with a great slaughter. And David saved the inhabitants of Keilah.
Sa’an nan Dawuda da mutanensa suka tafi Keyila, suka yi yaƙi da Filistiyawa, suka kwashe musu shanunsu, suka jijji wa Filistiyawa ƙwarai, suka cece mutanen Keyila daga hannunsu.
6 And in that time, when Abiathar, the son of Ahimelech, was in exile with David, he had descended to Keilah, having an ephod with him.
(Abiyatar ɗan Ahimelek ya zo da efod sa’ad da ya gudo zuwa wurin Dawuda a Keyila.)
7 Then it was reported to Saul that David had gone to Keilah. And Saul said: “The Lord has delivered him into my hands. For he is enclosed, having entered into a city which has gates and bars.”
Shawulu ya sami labari cewa Dawuda ya tafi Keyila, sai ya ce, “Allah ya bashe shi a hannuna, domin Dawuda ya kulle kansa ke nan da ya shiga birnin da yake da ƙofofin da ake kulle da ƙarafa.”
8 And Saul instructed all the people to descend in order to fight against Keilah, and to besiege David and his men.
Shawulu ya kira dukan sojojinsa don yaƙi, su gangaro zuwa Keyila su mamaye Dawuda da mutanensa.
9 And when David had realized that Saul had secretly prepared evil against him, he said to Abiathar, the priest, “Bring the ephod.”
Da Dawuda ya ji labari Shawulu yana shirya hanyar da zai kashe shi, sai ya ce wa Abiyatar firist, “Kawo mini efod a nan.”
10 And David said: “O Lord God of Israel, your servant has heard a report that Saul is planning to go to Keilah, so that he may overturn the city because of me.
Dawuda ya ce, “Ya Ubangiji, Allah na Isra’ila, bawanka ya sami labari cewa tabbatacce Shawulu yana shirin zuwa Keyila yă hallaka garin saboda ni.
11 Will the men of Keilah deliver me into his hands? And will Saul descend, just as your servant has heard? O Lord God of Israel, reveal to your servant.” And the Lord said, “He will descend.”
Mutanen Keyila za su bashe ni a gare shi? Shawulu zai gangaro nan kamar yadda bawanka ya sami labari? Ya Ubangiji, Allah na Isra’ila, ka gaya wa bawanka.” Ubangiji ya ce, “Zai zo.”
12 And David said, “Will the men of Keilah deliver me, and the men who are with me, into the hands of Saul?” And the Lord said, “They will deliver you.”
Dawuda ya sāke cewa, “Mutanen Keyila za su bashe ni da mutanena ga Shawulu?” Ubangiji ya ce, “Za su yi.”
13 Therefore, David, and his men of about six hundred, rose up, and, departing from Keilah, they wandered here and there, aimlessly. And it was reported to Saul that David had fled from Keilah, and was saved. For this reason, he chose not to go out.
Saboda haka Dawuda da mutanensa wajen mutum ɗari shida suka bar Keyila, suka yi ta tafiya daga wannan wuri zuwa wancan. Sa’ad da aka gaya wa Shawulu cewa Dawuda ya tsere daga Keyila, sai ya fasa tafiya can.
14 Then David stayed in the desert, in very strong places. And he stayed on a mount in the wilderness of Ziph, on a shady mount. Nevertheless, Saul was seeking him every day. But the Lord did not deliver him into his hands.
Dawuda ya zauna a jeji cikin kogunan duwatsu da kuma tuddan jejin Zif. Kowace rana Shawulu ya yi ta neman Dawuda amma Allah bai bashe Dawuda a hannunsa ba.
15 And David saw that Saul had gone out, so that he might seek his life. Now David was in the desert of Ziph, in the woods.
A lokacin da Dawuda yana zaune a Horesh cikin jejin Zif, ya sami labari cewa Shawulu ya fito don yă kashe shi.
16 And Jonathan, the son of Saul, rose up and went to David in the woods, and he strengthened his hands in God. And he said to him:
Yonatan ɗan Shawulu kuwa ya tafi wurin Dawuda a Horesh, ya ƙarfafa shi yă dogara ga Allah.
17 “Do not be afraid. For the hand of my father, Saul, will not find you. And you shall reign over Israel. And I will be second to you. And even my father knows this.”
Ya ce, “Kada ka ji tsoro, mahaifina Shawulu ba zai taɓa sa hannu a kanka ba. Za ka zama sarki a Isra’ila, ni kuma in zama na biyu gare ka. Kai, ko mahaifina Shawulu ma ya san da haka.”
18 Therefore, they both struck a pact before the Lord. And David stayed in the woods. But Jonathan returned to his house.
Su biyunsu kuwa suka ɗaura yarjejjeniya a gaban Ubangiji. Sai Yonatan ya koma gida amma Dawuda ya zauna Horesh.
19 Then the Ziphites ascended to Saul at Gibeah, saying: “Behold, is not David hidden with us in very secure places in the woods on the hill of Hachilah, which is to the right of the desert?
Zifawa suka tafi wurin Shawulu a Gibeya suka ce masa, “Ashe, ba Dawuda ne yake ɓuya a cikinmu a kogwannin duwatsu a Horesh a bisan tudun Hakila, kudu da Yeshimon ba?
20 Now therefore, if your soul has desired to descend, then descend. Then it will be for us to deliver him into the hands of the king.”
Yanzu, ya sarki, ka gangaro, ka zo a duk lokacin da ka ga ya yi maka, ka zo mu kuma hakkinmu ne mu bashe shi a hannun sarki.”
21 And Saul said: “You have been blessed by the Lord. For you have grieved for my situation.
Shawulu ya ce, “Ubangiji ya yi muku albarka, gama kun damu da ni.
22 Therefore, I beg you, go forth, and prepare diligently, and act carefully. And consider the place where his foot may be, and who may have seen him there. For he thinks, concerning me, that I craftily plan treachery against him.
Ku tafi ku ƙara shiri. Ku san inda yakan tafi, wane ne kuma ya gan shi a can. An gaya mini cewa shi mai wayo ne sosai.
23 Consider and seek out all his hiding places, in which he may be concealed. And return to me with certainty about the matter, so that I may go with you. But if he would even press himself into the earth, I will search him out, amid all the thousands of Judah.”
Ku binciko duk wuraren da yakan ɓuya, sai ku dawo ku gaya mini tabbataccen labari. Sa’an nan zan tafi tare da ku in yana can. Zan nemi shi ko’ina cikin dukan kabilar Yahuda.”
24 And rising up, they went to Ziph before Saul. But David and his men were in the desert of Maon, in the plain to the right of Jeshimon.
Sai suka tashi suka koma Zif, suka sha gaban Shawulu. Dawuda da mutanensa kuwa suna jejin Mawon cikin Araba, kudu da Yeshimon.
25 Then Saul and his allies went to seek him. And this was reported to David. And immediately, he descended to the rock, and he moved about in the desert of Maon. And when Saul had heard of it, he pursued David in the desert of Maon.
Shawulu da mutanensa suka tafi neman Dawuda. Da Dawuda ya ji labari, sai ya gangara cikin duwatsu ya zauna a cikin jejin Mawon. Sa’ad da Shawulu ya ji haka, sai ya tafi jejin Mawon yana fafaran Dawuda.
26 And Saul went to one side of the mountain. But David and his men were on the other side of the mountain. Then David was despairing that he would be able to escape from the face of Saul. And Saul and his men enclosed David and his men in the manner of a crown, so that they might capture them.
Shawulu yana tafiya a gefe ɗaya na dutsen, Dawuda da mutanensa kuma suna a wancan gefe, suna hanzari su ɓace wa Shawulu. Sa’ad da Shawulu da sojojinsa suka kusa cimma Dawuda da mutanensa don su kama su,
27 And a messenger came to Saul, saying, “Hurry and come, because the Philistines have poured themselves out upon the land.”
sai wani manzo ya zo wurin Shawulu yana cewa, “Ka koma da sauri, Filistiyawa sun kawo wa ƙasar hari.”
28 Therefore, Saul turned back, ceasing in the pursuit of David, and he traveled to meet the Philistines. For this reason, they called that place, the Rock of Division.
Shawulu kuwa ya janye daga fafaran Dawuda, ya tafi yă ƙara da Filistiyawa. Dalilin ke nan da ake kiran wannan wuri Sela Hammalekot, wato, dutsen tserewa.
29 Then David ascended from there, and he lived in very secure places in Engedi.
Dawuda kuwa ya haura daga can ya zauna a kogwannin duwatsun En Gedi.

< 1 Samuel 23 >