< 1 Kings 5 >

1 Hiram, the king of Tyre, also sent his servants to Solomon. For he heard that they had anointed him king in place of his father. Now Hiram had been a friend to David the entire time.
Sa’ad da Hiram sarkin Taya ya ji an shafe Solomon sarki yă gāji mahaifinsa Dawuda, sai ya aika da jakadunsa zuwa wurin Solomon, gama shi da Dawuda abokai ne sosai dukan kwanakinsa.
2 Then Solomon sent to Hiram, saying:
Solomon ya mayar da wannan saƙo ga Hiram ya ce,
3 “You know the will of my father David, and that he was not able to build a house to the name of the Lord his God, because of the wars that were imminent all around him, until the Lord set them under the steps of his feet.
“Ka san cewa saboda yaƙe-yaƙen da abokan gāba suka yi da mahaifina a kowane gefe, ya sa bai iya gina haikali domin Sunan Ubangiji Allahnsa ba, sai da Ubangiji ya sa abokan gābansa a ƙarƙashin ƙafafunsa.
4 But now the Lord my God has given rest to me on all sides. And there is no adversary, nor occurrence of evil.
Amma yanzu Ubangiji Allahna ya ba ni hutu a kowane gefe, babu kuma gāba ko masifa.
5 For this reason, I intend to build a temple to the name of the Lord my God, just as the Lord spoke to my father David, saying: ‘Your son, whom I will set in your place, upon your throne, he himself shall build a house to my name.’
Ina niyya in gina haikali domin Sunan Ubangiji Allahna, yadda Ubangiji ya faɗa wa mahaifina Dawuda, sa’ad da ya ce, ‘Ɗanka wanda zai gāje ka, shi zai gina haikali domin Sunana.’
6 Therefore, order that your servants may cut down for me cedars from Lebanon. And let my servants be with your servants. Then I will give to you, for the wages of your servants, whatever you will ask. For you know that there is not a man among my people who knows how to cut wood as well as the Sidonians.”
“Don haka, ka ba da umarni a yanka mini itatuwan al’ul na ƙasar Lebanon. Ma’aikatana za su haɗa hannu da ma’aikatanka, ni kuwa zan biya ka albashin ma’aikatanka kamar yadda ka faɗa. Gama ka san cewa babu wani a cikinmu da ya iya yanka itacen katako kamar Sidoniyawa.”
7 Therefore, when Hiram had heard the words of Solomon, he rejoiced greatly, and he said, “Blessed be the Lord God this day, who gave to David a very wise son over this numerous people!”
Da Hiram ya ji saƙon Solomon, sai ya ji daɗi ƙwarai, ya kuma ce, “Yabo ga Ubangiji a yau, gama ya ba wa Dawuda ɗa mai hikima yă yi mulki a bisa wannan al’umma mai girma.”
8 And Hiram sent to Solomon, saying: “I have heard the things that you would entrust to me. And I will do your whole will concerning the cedar trees and spruce trees.
Sai Hiram ya aike wa Solomon da kalmomin nan, “Na sami saƙon da ka aika mini, zan kuma yi duk abin da kake so ta wurin tanada katakan al’ul da na fir.
9 My servants shall bring them down from Lebanon to the sea. And I will arrange them together as rafts on the sea, as far as the place that you will indicate to me. And I will land them there, and you will take them. And you shall offer to me what is necessary to give food to my house.”
Ma’aikatana za su gangara da su daga Lebanon zuwa bakin teku. Zan sa a ɗaɗɗaura su su bi ruwan teku daga Lebanon zuwa bakin Bahar Rum da za ka nuna mini. A can zan kunce maka su, sa’an nan ka kwashe. Kai kuma za ka biya bukatata ta wurin tanadin abinci wa gidana.”
10 And so, Hiram gave to Solomon cedar trees and spruce trees, in accord with his whole will.
A haka Hiram ya ci gaba da aika wa Solomon al’ul da kuma fir da yake bukata.
11 Then Solomon offered to Hiram twenty thousand cor of wheat, as food for his house, and twenty cor of the purest oil. These things Solomon gave as a tribute to Hiram every year.
Solomon kuma ya ba wa Hiram mudu gari dubu ashirin na alkama a matsayin abinci domin gidansa, ya ƙara da garwa dubu ashirin na tataccen man zaitun. Solomon ya ci gaba da yin haka ga Hiram, shekara-shekara.
12 And the Lord gave wisdom to Solomon, just as he said to him. And there was peace between Hiram and Solomon, and the two struck a pact.
Ubangiji ya ba wa Solomon hikima, kamar yadda ya yi masa alkawari. Dangantakar zaman lafiya ta kasance tsakanin Hiram da Solomon, su biyun suka yi yarjejjeniya.
13 And king Solomon chose workers from all of Israel, and the conscription was of thirty thousand men.
Sarki Solomon ya ɗebi ma’aikata daga dukan Isra’ila, su dubu talatin.
14 And he sent them into Lebanon, ten thousand each month, in turns, so that for two months they were in their own houses. And Adoniram was over this type of conscription.
Ya riƙa aika su dubu goma-goma zuwa Lebanon kowane wata, saboda su yi wata ɗaya a Lebanon, watanni biyu kuma a gida. Adoniram ne ya lura da aikin gandun.
15 And Solomon had seventy thousand of those who were carrying burdens, and eighty thousand of those who cut stones from the mountain,
Solomon ya kasance da’yan ɗauko guda dubu saba’in da masu yankan duwatsu guda dubu tamanin a cikin tuddai,
16 aside from the commanders who were over each work, in number three thousand and three hundred, who gave orders to the people and to those who were doing the work.
ya kuma kasance da shugabanni dubu uku da ɗari uku waɗanda suke lura da aikin, su ne kuma suke bi da ma’aikatan.
17 And the king ordered them to bring great stones, precious stones, for the foundation of the temple, and to square them.
Bisa ga umarnin sarki sai suka cire manyan duwatsu masu kyau don a tanada tushen duwatsun da aka gyara domin haikalin daga wurin haƙar duwatsun.
18 And these were shaped by the stoneworkers of Solomon and the stoneworkers of Hiram. And the men of Gebal also prepared the wood and the stones in order to build the house.
Gwanayen Solomon da na Hiram da kuma mutanen Gebal, su suka yanka, suka kuma shirya katako da dutse don ginin haikali.

< 1 Kings 5 >