< 1 Corinthians 1 >

1 Paul, called as an Apostle of Jesus Christ by the will of God; and Sosthenes, a brother:
Bulus, wanda aka kira domin yă zama manzon Kiristi Yesu, bisa ga nufin Allah, da kuma ɗan’uwanmu Sostenes,
2 to the Church of God which is at Corinth, to those sanctified in Christ Jesus, called to be saints with all who are invoking the name of our Lord Jesus Christ in every place of theirs and of ours.
Zuwa ga ikkilisiyar Allah da take a Korint, da waɗanda aka tsarkake cikin Kiristi Yesu, aka kuma kira domin su zama masu tsarki, tare da dukan waɗanda suke ko’ina da suke kiran sunan Ubangijinmu Yesu Kiristi, Ubangijinsu da kuma namu.
3 Grace and peace to you from God our Father and from the Lord Jesus Christ.
Alheri da salama daga Allah Ubanmu, da Ubangiji Yesu Kiristi, su kasance tare da ku.
4 I give thanks to my God continuously for you because of the grace of God that has been given to you in Christ Jesus.
Ina gode wa Allah kullum dominku, saboda alherinsa da aka ba ku a cikin Kiristi Yesu.
5 By that grace, in all things, you have become wealthy in him, in every word and in all knowledge.
Gama a cikinsa kuka sami wadata ta kowace hanya, a cikin dukan maganarku, da kuma cikin dukan saninku
6 And so, the testimony of Christ has been strengthened in you.
gama shaidarmu game da Kiristi ta tabbata a cikinku.
7 In this way, nothing is lacking to you in any grace, as you await the revelation of our Lord Jesus Christ.
Saboda haka, ba ku rasa kowace baiwa ta ruhaniya ba, yayinda kuke jira da marmari, saboda bayyanuwar Ubangijinmu Yesu Kiristi.
8 And he, too, will strengthen you, even until the end, without guilt, until the day of the advent of our Lord Jesus Christ.
Zai ƙarfafa ku har zuwa ƙarshe, domin ku zama marasa aibi a ranar Ubangijinmu Yesu Kiristi.
9 God is faithful. Through him, you have been called into the fellowship of his Son, Jesus Christ our Lord.
Allah, wanda ya kira ku zuwa ga zumunci tare da Ɗansa Yesu Kiristi Ubangijinmu, shi mai aminci ne.
10 And so, I beg you, brothers, by the name of our Lord Jesus Christ, that every one of you speak in the same way, and that there be no schisms among you. So may you become perfect, with the same mind and with the same judgment.
Ina roƙonku’yan’uwa, a cikin sunan Ubangijinmu Yesu Kiristi, dukanku ku yarda da juna, domin kada a sami tsattsaguwa a cikinku, domin kuma ku zama ɗaya, cikakku a cikin halinku da tunaninku.
11 For it has been indicated to me, about you, my brothers, by those who are with Chloes, that there are contentions among you.
’Yan’uwana, waɗansu daga iyalin gidan Kulos sun gaya mini cewa, akwai faɗa a cikinku.
12 Now I say this because each of you is saying: “Certainly, I am of Paul;” “But I am of Apollo;” “Truly, I am of Cephas;” as well as: “I am of Christ.”
Abin da nake nufi shi ne, ɗaya daga cikinku na cewa, “Ni ina bin Bulus,” wani na cewa, “Ni ina bin Afollos,” wani kuma, “Ni ina bin Kefas,” har wa yau wani kuma, “Ni ina bin Kiristi.”
13 Has Christ been divided? Was Paul crucified for you? Or were you baptized in the name of Paul?
Kiristi a rabe ne? Bulus ne aka gicciye dominku? An yi muku baftisma a cikin sunan Bulus ne?
14 I give thanks to God that I have baptized none of you, except Crispus and Gaius,
Ina godiya domin ban yi wa wani baftisma a cikinku ba, sai dai Kirisbus da Gayus kaɗai.
15 lest anyone say that you have been baptized in my name.
Don haka, ba wanda na iya cewa an yi muku baftisma a cikin sunana.
16 And I also baptized the household of Stephanus. Other than these, I do not recall if I baptized any others.
(I, na kuma yi wa iyalin gidan Istifanas baftisma, ban da wannan, ban tuna da wani da na yi masa baftisma ba.)
17 For Christ did not send me to baptize, but to evangelize: not through the wisdom of words, lest the cross of Christ become empty.
Gama Kiristi bai aike ni yin baftisma ba, sai dai wa’azin bishara ba da kalmomin hikimar mutum ba, domin kada gicciyen Kiristi ya rasa ikonsa.
18 For the Word of the Cross is certainly foolishness to those who are perishing. But to those who have been saved, that is, to us, it is the power of God.
Gama saƙon gicciye wauta ne ga waɗanda suke hallaka, amma a gare mu, mu da ake ceto, ikon Allah ne.
19 For it has been written: “I will perish the wisdom of the wise, and I will reject the discernment of the prudent.”
Gama a rubuce yake cewa, “Zan rushe hikimar mai hikima, basirar mai azanci kuma zan rikita shi.”
20 Where are the wise? Where are the scribes? Where are the truth-seekers of this age? Has not God made the wisdom of this world into foolishness? (aiōn g165)
Ina mai hikima? Ina mai zurfin bincike? Ina masana na wannan zamani? Ashe, Allah bai wofinta hikimar duniya ba? (aiōn g165)
21 For the world did not know God through wisdom, and so, in the wisdom of God, it pleased God to accomplish the salvation of believers, through the foolishness of our preaching.
Gama tun da a cikin hikimar Allah, duniya a cikin hikimarta ba tă san shi ba, Allah ya ji daɗin ceton waɗanda suka ba da gaskiya ta wurin wautar wa’azin bishara.
22 For the Jews ask for signs, and the Greeks seek wisdom.
Yahudawa suna so su ga alama, Hellenawa kuma suna neman hikima,
23 But we are preaching Christ crucified. Certainly, to the Jews, this is a scandal, and to the Gentiles, this is foolishness.
amma mu, muna wa’azin Kiristi wanda aka gicciye ne, wanda ya zama dutsen tuntuɓe ga Yahudawa, wauta kuma ga Al’ummai,
24 But to those who have been called, Jews as well as Greeks, the Christ is the virtue of God and the wisdom of God.
amma ga su waɗanda Allah ya kira, Yahudawa da Hellenawa, Kiristi ikon Allah ne, da kuma hikimar Allah.
25 For what is foolishness to God is considered wise by men, and that which is weakness to God is considered strong by men.
Gama wautar Allah ta fi hikimar mutum, kuma rashin ƙarfin Allah ya fi ƙarfin mutum.
26 So take care of your vocation, brothers. For not many are wise according to the flesh, not many are powerful, not many are noble.
’Yan’uwa, ku tuna yadda kuke sa’ad da aka kira ku. Babu masu hikima da yawa a cikinku, bisa ga ganin mutum; babu masu iko da yawa, babu masu martaba da yawa bisa ga haihuwa.
27 But God has chosen the foolish of the world, so that he may confound the wise. And God has chosen the weak of the world, so that he may confound the strong.
Amma Allah ya zaɓi abubuwa masu wautata duniya, don yă kunyata masu hikima. Allah ya zaɓi abubuwa marasa ƙarfi na duniya, domin ya ba wa masu ƙarfi kunya.
28 And God has chosen the ignoble and contemptible of the world, those who are nothing, so that he may reduce to nothing those who are something.
Ya zaɓi abubuwa marasa martaba na wannan duniya da kuma abubuwan da aka rena da abubuwan da ba a ɗauka a bakin kome ba, domin a wofinta abubuwan da ake ganinsu da daraja,
29 So then, nothing that is of the flesh should glory in his sight.
domin kada wani ya yi taƙama a gabansa.
30 But you are of him in Christ Jesus, who was made by God to be our wisdom and justice and sanctification and redemption.
Saboda Allah ne kuke cikin Kiristi Yesu, shi wanda ya zama hikima a gare mu daga Allah. Kiristi shi ne adalcinmu, da tsarkinmu, da kuma fansarmu.
31 And so, in the same way, it was written: “Whoever glories, should glory in the Lord.”
Saboda haka, kamar yadda yake a rubuce cewa, “Duk wanda yake taƙama, ya yi taƙama a cikin Ubangiji.”

< 1 Corinthians 1 >