< Proverbs 31 >
1 My words have been spoken by God—the oracular answer of a king, whom his mother instructed.
Maganganun Sarki Lemuwel, magana ce horarriya mahaifiyarsa ta koya masa,
2 What will you keep, my son, what? the words of God. My firstborn son, I speak to you: what? son of my womb? what? son of my vows?
“Ka saurara, ya ɗana! Ka saurara, ɗan cikina! Ka saurara, ya ɗan amshin addu’ata!
3 Give not your wealth to women, nor your mind and living to remorse. Do all things with counsel: drink wine with counsel.
Kada ka ba da ƙarfinka a kan mata, ƙarfinka ga waɗanda suka hallaka sarakuna.
4 Princes are prone to anger: let them then not drink wine:
“Ba na sarakuna ba ne, ya Lemuwel, ba na sarakuna ba ne su sha ruwan inabi, ba na masu mulki ba ne su yi marmarin barasa,
5 lest they drink, and forget wisdom, and be not able to judge the poor rightly.
don kada su sha su manta da abin da doka ta umarta, su hana wa waɗanda aka danne hakkinsu.
6 Give strong drink to those that are in sorrow, and the wine to drink to those in pain:
A ba da barasa ga waɗanda suke cikin halin ƙaƙa naka yi, ruwan inabi ga waɗanda suke cikin wahala;
7 that they may forget their poverty, and may not remember their troubles any more.
bari su sha su manta da talaucinsu kada kuma su ƙara tunawa da ɓacin ransu.
8 Open your mouth with the word of God, and judge all fairly.
“Yi magana domin bebaye, domin hakkin dukan waɗanda suke naƙasassu.
9 Open your mouth and judge justly, and plead the cause of the poor and weak.
Yi magana a kuma yi shari’ar adalci; a tsare hakkin talakawa da masu bukata.”
10 Who shall find a virtuous woman? for such a one is more valuable than precious stones.
Wa yake iya samun mace mai halin kirki? Darajarta ta fi ta lu’ulu’ai.
11 The heart of her husband trusts in her: such a one shall stand in no need of fine spoils.
Mijinta yana da cikakken amincewa da ita kuma ba ya rasa wani abu mai daraja.
12 For she employs all her living for her husband's good.
Takan yi masa alheri ba mugunta ba, dukan kwanakin ranta.
13 Gathering wool and flax, she makes it serviceable with her hands.
Takan zaɓi ulu da lilin ta yi ta saƙa da hannuwanta da farin ciki.
14 She is like a ship trading from a distance: so she procures her livelihood.
Ita kamar jirgin’yan kasuwa ne tana kawo abincinta daga nesa.
15 And she rises by night, and gives food to her household, and [appointed] tasks to her maidens.
Takan farka tun da sauran duhu; ta tanada wa iyalinta abinci ta kuma shirya wa’yan matan gidanta ayyukan da za su yi.
16 She views a farm, and buys it: and with the fruit of her hands she plants and a possession.
Takan lura da gona sosai ta kuma saye ta; daga abin da take samu na kuɗin shiga take shuka gonar inabi.
17 She strongly girds her loins, and strengthens her arms for work.
Takan himmantu tă yi aikinta tuƙuru; hannuwanta suna da ƙarfi domin ayyukanta.
18 And she finds by experience that working is good; and her candle goes not out all night.
Takan tabbata akwai riba a kasuwancinta, kuma fitilarta ba ya mutuwa da dare.
19 She reaches forth her arms to needful [works], and applies her hands to the spindle.
Da hannunta take riƙe abin kaɗi ta kuma kama abin saƙa da yatsotsinta.
20 And she opens her hands to the needy, and reaches out fruit to the poor.
Takan marabci talakawa takan kuma taimaki masu bukata.
21 Her husband is not anxious about those at home when he tarries anywhere abroad: for all her household are clothed.
Sa’ad da ƙanƙara ta fāɗi, ba ta jin tsoro saboda gidanta; gama dukansu suna da tufafi masu kauri.
22 She makes for her husband clothes of double texture, and garments for herself of fine linen and scarlet.
Takan yi wa gadonta kayan shimfiɗa; tufafinta kuma na lilin ne mai laushi na shunayya.
23 And her husband becomes a distinguished [person] in the gates, when he sits in council with the old inhabitants of the land.
Ana girmama mijinta a ƙofar shiga birni inda yakan zauna a cikin dattawan gari.
24 She makes fine linens, and sells girdles to the Chananites: she opens her mouth heedfully and with propriety, and controls her tongue.
Takan yi riguna na lilin ta sayar; takan kuma sayar wa’yan kasuwa da ɗamara.
25 She puts on strength and honour; and rejoices in the last days.
Ƙarfi da mutunci su ne suturarta; za tă iya yin dariyar kwanaki masu zuwa.
26 But she opens her mouth wisely, and according to law.
Tana magana da hikima, kuma umarnai mai aminci yana a harshenta.
27 The ways of her household are careful, and she eats not the bread of idleness.
Tana lura da sha’anin gidanta kuma ba ta cin abincin ƙyuya.
28 And [her] kindness to them sets up her children for them, and they grow rich, and her husband praises her.
’Ya’yanta sukan tashi su ce da ita mai albarka; haka mijinta ma, yakan kuma yabe ta yana cewa,
29 Many daughters have obtained wealth, many have wrought valiantly; but you have exceeded, you have surpassed all.
“Mata da yawa suna yin abubuwan yabo, amma ke kin fi su duka.”
30 Charms are false, and woman's beauty is vain: for it is a wise woman that is blessed, and let her praise the fear the Lord.
Kayan tsari yana ruɗu, kyau kuma kan shuɗe; amma mace mai tsoron Ubangiji abar yabo ce.
31 Give her of the fruit of her lips; and let her husband be praised in the gates.
Ka ba ta ladar da ya dace tă samo wa kanta, bari kuma ayyukanta su kawo mata yabo a ƙofar shiga birni.