< Job 14 >

1 For a mortal born of a woman [is] short lived, and full of wrath.
“Mutum haihuwar mace kwanakinsa kaɗan ne, kuma cike da wahala.
2 Or he falls like a flower that has bloomed; and he departs like a shadow, and can’t continue.
Yana tasowa kamar fure yana kuma shuɗewa; kamar inuwa, ba ya daɗewa.
3 Hast you not taken account even of him, and caused him to enter into judgement before you?
Za ka zura ido a kan irin wannan ne? Za ka kawo shi gaba don ka yi masa shari’a?
4 For who shall be pure from uncleanness? not even one;
Wane ne zai iya kawo abin da yake da tsarki daga cikin abu marar tsarki? Babu!
5 if even his life should be [but] one day upon the earth: and his months are numbered by him: you have appointed [him] for a time, and he shall by no means exceed [it].
An lissafta kwanakin mutum; ka riga ka ɗibar masa watanni, ka yi masa iyaka, ba zai iya wuce iyakar ba.
6 Depart from him, that he may be quiet, and take pleasure in his life, [though] as a hireling.
Saboda haka ka kawar da kanka daga gare shi, ka rabu da shi har sai ya cika lokacinsa kamar mutumin da aka ɗauki hayarsa.
7 For there is hope for a tree, even if it should be cut down, [that] it shall blossom again, and its branch shall not fail.
“Aƙalla itace yana da bege. In an sare shi, zai sāke tsira, zai tohu da kyau.
8 For though its root should grow old in the earth, and its stem die in the rock;
Ko da jijiyoyin itacen sun tsufa a cikin ƙasa kuma kututturensa ya mutu a cikin ƙasa.
9 it will blossom from the scent of water, and will produce a crop, as one newly planted.
Daga ya ji ƙanshin ruwa zai tohu yă yi tsiro kamar shuka.
10 But a man that has died is utterly gone; and when a mortal has fallen, he is no more.
Amma mutum yana mutuwa a bizne shi; daga ya ja numfashinsa na ƙarshe, shi ke nan.
11 For the sea wastes in [length of] time, and a river fails and is dried up.
Kamar yadda ruwa yake bushewa a teku ko a gaɓar rafi sai wurin yă bushe,
12 And man that has lain down [in death] shall certainly not rise again till the heaven be dissolved, and they shall not awake from their sleep.
haka mutum zai kwanta ba zai tashi ba; har sai duniya ta shuɗe mutane ba za su farka ba, ba za su tashi daga barcinsu ba.
13 For oh that you had kept me in the grave, and had hidden me until your wrath should cease, and you should set me a time in which you would remember me! (Sheol h7585)
“Da ma za ka ɓoye ni a cikin kabari ka ɓoye ni har sai fushinka ya wuce! In da za ka keɓe mini lokaci sa’an nan ka tuna da ni! (Sheol h7585)
14 For if a man should die, shall he live [again], having accomplished the days of his life? I will wait till I exist again?
In mutum ya mutu, ko zai sāke rayuwa? In haka ne zan daure kwanakin da nake shan wahala har su wuce.
15 Then shall you call, and I will listen to you: but do not you reject the work of your hands.
Za ka kira zan kuwa amsa maka; za ka yi marmarin abin da hannunka ya halitta.
16 But you have numbered my devices: and not one of my sins shall escape you?
Ba shakka a lokacin ne za ka lura da matakaina amma ba za ka kula da zunubaina ba.
17 An you have sealed up my transgressions in a bag, and marked if I have been guilty of any transgression unawares.
Za a daure laifofina a cikin jaka; za ka rufe zunubaina.
18 And verily a mountain falling will utterly be destroyed, and a rock shall be worn out of its place.
“Amma kamar yadda manyan duwatsu suke fāɗuwa su farfashe su kuma gusa daga wurarensu,
19 The waters wear the stones, and waters falling headlong [overflow] a heap of the earth: and you destroy the hope of man.
yadda ruwa yakan zaizaye duwatsu ruwa mai ƙarfi kuma yă kwashe turɓayar ƙasa, haka kake barin mutum ba bege.
20 You drive him to an end, and he is gone: you set your face against him, and send him away;
Ka sha ƙarfinsa gaba ɗaya, sai ya ɓace, ka sauya yanayinsa ka kuma kore shi.
21 and though his children be multiplied, he knows [it] not; and if they be few, he is not aware.
Ko an martaba’ya’yansa maza, ba zai sani ba; Ko an wulaƙanta su, ba zai gani ba.
22 But his flesh is in pain, and his soul mourns.
Zafin jikinsa kaɗai yake ji yana kuka wa kansa ne kaɗai.”

< Job 14 >