< Jezekiel 35 >
1 And the word of the Lord came to me, saying,
Maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
2 Son of man, set your face against mount Seir, and prophesy against it,
“Ɗan mutum, ka fuskanci Dutsen Seyir; ka yi annabci a kansa
3 and say to it, Thus says the Lord God; Behold, I am against you, O mount Seir, and I will stretch out my hand against you, and will make you a waste, and you shall be made desolate.
ka ce, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa ina gāba da kai, Dutsen Seyir, zan kuma miƙa hannuna gāba da kai in mai da kai kango.
4 And I will cause desolation in your cities, and you shall be desolate, and you shall know that I am the Lord.
Zan mai da garuruwanka kufai za ka kuma zama kango. Sa’an nan za ka san cewa ni ne Ubangiji.
5 Because you have been a perpetual enemy, and have laid wait craftily for the house of Israel, with the hand of enemies with a sword, in the time of injustice, at the last:
“‘Domin ka riƙe ƙiyayya ta tun dā, ka kuma ba da mutanen Isra’ila domin a kashe su da takobi a lokacin masifarsu, lokacin da adadin horonsu ya cika,
6 Therefore, as I live, says the Lord God, verily you have sinned even to blood, therefore blood shall pursue you.
saboda haka muddin ina raye, in ji Ubangiji Mai Iko Duka, zan sa a zub da jininka zan kuwa fafare ka. Da yake ba ka ƙi zub da jini ba, zub da jini zai fafare ka.
7 And I will make mount Seir a waste, and desolate, and I will destroy from off it men and cattle:
Zan mai da Dutsen Seyir kango in kuma yanke dukan waɗanda suke shiga da fita a cikinka.
8 and I will fill your hills and your valleys with slain men, and in all your plains there shall fall in you men slain with the sword.
Zan cika duwatsunka da matattu; waɗanda aka kashe da takobi za su fāɗi a kan tuddanka, da cikin kwarurukanka, da cikin dukan kwazazzabanka.
9 I will make you a perpetual desolation, and your cities shall not be inhabited any more: and you shall know that I am the Lord.
Zan mai da kai kango har abada; ba za a zauna a cikin garuruwanka ba. Sa’an nan za ka san cewa ni ne Ubangiji.
10 Because you said, The two nations and the two countries shall be mine, and I shall inherit them; whereas the Lord is there:
“‘Domin kun ce, “Waɗannan al’ummai biyu da ƙasashe za su zama namu za mu kuma mallake su,” ko da yake Ni Ubangiji ina a can,
11 therefore, [as] I live, says the Lord, I will even deal with you according to your enmity, and I will be made known to you when I shall judge you:
saboda haka muddin ina raye, in ji Ubangiji Mai Iko Duka, zan sāka maka gwargwadon fushi da kuma kishin da ka nuna a ƙiyayyarsu da ka yi zan kuma sanar da kaina a cikinsu sa’ad da na hukunta ka.
12 and you shall know that I am the Lord. I have heard the voice of your blasphemies, whereas you have said, The desert mountains of Israel are given to us for food;
Sa’an nan za ka san cewa Ni Ubangiji na ji duk abubuwan banzan da ka faɗa a kan duwatsun Isra’ila. Ka ce, “An mai da su kango an kuma ba mu su mu cinye.”
13 and you have spoken swelling words against me with your mouth: I have heard [them].
Ka yi fariya a kaina, ka kuma yi magana a kaina ba gaggautawa, na ji shi sarai.
14 Thus says the Lord; When all the earth is rejoicing, I will make you desert.
Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa yayinda dukan duniya take farin ciki, zan mai da kai kango.
15 You shall be desert, O mount Seir, and all Idumea; and it shall be utterly consumed: and you shall know that I am the Lord their God.
Domin ka yi farin ciki sa’ad da gādon gidan Isra’ila ya zama kufai, haka zan yi da kai, ya Dutsen Seyir, kai da dukan Edom. Sa’an nan za ka san cewa ni ne Ubangiji.’”