< Psalms 40 >
1 For the end, a Psalm of David. I waited patiently for the Lord; and he attended to me, and hearkened to my supplication.
Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Ta Dawuda. Zabura ce. Na jira da haƙuri ga Ubangiji; ya juya wurina ya kuma ji kukata.
2 And he brought me up out of a pit of misery, and from miry clay: and he set my feet on a rock, and ordered my goings aright.
Ya ɗaga ni daga rami marar fāɗi, daga laka da taɓo; ya sa ƙafafuna a kan dutse ya kuma ba ni tsayayyen wuri don in tsaya.
3 And he put a new song into my mouth, [even] a hymn to our God: many shall see [it], and fear, and shall hope in the Lord.
Ya sa sabuwar waƙa a bakina, waƙar yabo ga Allahna. Da yawa za su gani su tsorata su kuma dogara ga Ubangiji.
4 Blessed [is] the man whose hope is in the name of the Lord, and [who] has not regarded vanities and false frenzies.
Mai albarka ne mutumin da ya mai da Ubangiji abin dogararsa, wanda ba ya kula da masu girman kai, waɗanda suka juya ga allolin ƙarya.
5 O Lord my God, thou hast multiplied thy wonderful works, and in thy thoughts there is none who shall be likened to thee: I declared and spoke [of them]: they exceeded number.
Da yawa ne, ya Ubangiji Allahna, abubuwan banmamakin da ka aikata. Abubuwan da ka shirya mana. Ba wanda zai iya faɗa maka su; a ce zan yi magana in faɗe su, za su wuce gaban misali a furta.
6 Sacrifice and offering thou wouldest not; but a body hast thou prepared me: whole-burnt-offering and [sacrifice] for sin thou didst not require.
Hadaya da sadaka ba ka sha’awa, amma kunnuwana ka huda; hadayun ƙonawa da hadayun zunubi ba ka bukata.
7 Then I said, Behold, I come: in the volume of the book it is written concerning me,
Sa’an nan na ce, “Ga ni, na zo, kamar yadda yake a rubuce game da ni cikin littafi.
8 I desired to do thy will, O my God, and thy law in the midst of mine heart.
Ina sha’awar aikata nufinka, ya Allahna; dokar tana cikin zuciyata.”
9 I have preached righteousness in the great congregation; lo! I will not refrain my lips; O Lord, thou knowest my righteousness.
Na yi shelar adalcinka cikin babban taro; ba na rufe leɓunana, kamar yadda ka sani, ya Ubangiji.
10 I have not hid thy truth within my heart, and I have declared thy salvation; I have not hid thy mercy and thy truth from the great congregation.
Ba na ɓoye adalcinka cikin zuciyata; ina maganar amincinka da cetonka. Ban ɓoye ƙaunarka da gaskiyarka a gaban taron jama’arka mai girma ba.
11 But thou, Lord, remove not thy compassion far from me; thy mercy and thy truth have helped me continually.
Kada ka hana mini jinƙanka, ya Ubangiji; bari ƙaunarka da gaskiyarka kullum su kāre ni.
12 For innumerable evils have encompassed me; my transgressions have taken hold of me, and I could not see; they are multiplied more than the hairs of my head; and my heart has failed me.
Gama damuwoyin da suka wuce misali sun kewaye ni; zunubaina sun mamaye ni, kuma ba na iya gani. Sun fi gashin kaina yawa, har ma na fid da zuciya.
13 Be pleased, O Lord, to deliver me; O Lord, draw nigh to help me.
Ka ji daɗin cetona, ya Ubangiji; Ya Ubangiji, ka zo da sauri ka taimake ni.
14 Let those that seek my soul, to destroy it, be ashamed and confounded together; let those that wish me evil be turned backward and put to shame.
Bari masu neman raina su sha kunya su kuma rikice; bari dukan waɗanda suke neman lalacewata su koma baya da kunya.
15 Let those that say to me, Aha, aha, quickly receive shame for their reward.
Bari masu ce mini, “Allah yă ƙara!” Su sha mamaki saboda kunyar da za su sha.
16 Let all those that seek thee, O Lord, exult and rejoice in thee; and let them that love thy salvation say continually, The Lord be magnified.
Amma bari dukan masu nemanka su yi farin ciki su kuma yi murna a cikinka; bari waɗanda suke ƙaunar cetonka kullum su ce, “Ubangiji mai girma ne!”
17 But I am poor and needy; the Lord will take care of me; thou art my helper, and my defender, O my God, delay not.
Ni dai matalauci ne da mai bukata; bari Ubangiji yă tuna da ni. Kai ne taimakona da mai cetona; Ya Allahna, kada ka jinkirta.