< Psalms 2 >
1 Wherefore did the heathen rage, and the nations imagine vain things?
Me ya sa ƙasashe suke haɗa baki mutane kuma suke ƙulla shawarwarin banza?
2 The kings of the earth stood up, and the rulers gathered themselves together, against the Lord, and against his Christ;
Sarakunan duniya sun ɗauki matsayi masu mulki sun taru gaba ɗaya suna gāba da Ubangiji da kuma Shafaffensa.
3 [saying], Let us break through their bonds, and cast away their yoke from us.
Suna cewa, “Bari mu tsittsinke sarƙoƙinsu, mu kuma’yantar da kamammu daga kangin bautar Allah.”
4 He that dwells in the heavens shall laugh them to scorn, and the Lord shall mock them.
Mai zama a kursiyi a sama yana dariya; Ubangiji yana musu ba’a.
5 Then shall he speak to them in his anger, and trouble them in his fury.
Sa’an nan ya tsawata musu cikin fushinsa ya kuma razanar da su cikin hasalarsa, yana cewa,
6 But I have been made king by him on Sion his holy mountain,
“Na kafa Sarkina a kan kursiyi a kan Sihiyona, dutsena mai tsarki.”
7 declaring the ordinance of the Lord: the Lord said to me, Thou art my Son, to-day have I begotten thee.
Sarki ya yi shelar umarnin Ubangiji. Ubangiji ya ce mini, “Kai Ɗana ne; yau na zama Mahaifinka.
8 Ask of me, and I will give thee the heathen [for] thine inheritance, and the ends of the earth [for] thy possession.
Ka tambaye ni zan kuwa sa al’ummai su zama gādonka, iyakokin duniya su zama mallakarka.
9 Thou shalt rule them with a rod of iron; thou shalt dash them in pieces as a potter's vessel.
Za ka yi mulkinsu da sandan ƙarfe; za ka farfashe su kucu-kucu kamar tukunyar laka.”
10 Now therefore understand, ye kings: be instructed, all ye that judge the earth.
Saboda haka, ku sarakuna, ku yi wayo; ku shiga hankalinku, ku masu mulkin duniya.
11 Serve the Lord with fear, and rejoice in him with trembling.
Ku bauta wa Ubangiji da tsoro ku kuma yi farin ciki kuna rawar jiki.
12 Accept correction, lest at any time the Lord be angry, and ye should perish from the righteous way: whensoever his wrath shall be suddenly kindled, blessed are all they that trust in him.
Ku sumbaci Ɗan, don kada yă yi fushi ku hallaka a abubuwan da kuke yi, gama fushinsa zai iya kuna farat ɗaya. Masu farin ciki ne dukan waɗanda suke neman mafaka daga gare shi.