< Ruth 4 >
1 And Boaz went up to the public place of the town, and took his seat there: and the near relation of whom he had been talking came by; and Boaz, crying out to him by name, said, Come and be seated here. And he came and was seated.
Ana cikin haka Bowaz ya haura zuwa ƙofar gari ya tafi ya zauna a can. Sa’ad da dangi mai fansan da ya yi zance ya iso, Bowaz ya ce, “Zo nan abokina ka zauna.” Saboda haka ya ratso ya zauna.
2 Then he got ten of the responsible men of the town, and said, Be seated here. And they took their seats.
Bowaz kuwa ya kira dattawa guda goma na garin ya ce, “Ku zauna a nan,” suka kuwa zauna.
3 Then he said to the near relation, Naomi, who has come back from the country of Moab, is offering for a price that bit of land which was our brother Elimelech's:
Sa’an nan ya ce wa dangin nan mai fansa, “Na’omi, wadda ta dawo daga Mowab, tana so ta sayar da filin da yake na ɗan’uwanmu Elimelek.
4 And it was in my mind to give you the chance of taking it, with the approval of those seated here and of the responsible men of my people. If you are ready to do what it is right for a relation to do, then do it: but if you will not do it, say so to me now; for there is no one who has the right to do it but you, and after you myself. And he said, I will do it.
Na ga ya kamata in jawo hankalinka ga batun in kuma ba da shawara ka saye shi a gaban waɗannan da suke zazzaune a nan da kuma a gaban dattawan jama’a. In kana so ka fanshe shi, to, sai ka yi. Amma in ba za ka yi ba, sai ka faɗa mini, don in sani. Gama babu wani mai izinin yin haka sai kai, ni ne kuwa na biye.” Sai ya ce, “Zan fansa.”
5 Then Boaz said, On the day when you take this field, you will have to take with it Ruth, the Moabitess, the wife of the dead, so that you may keep the name of the dead living in his heritage.
Sa’an nan Bowaz ya ce, “A ranar da ka saya filin daga Na’omi da kuma daga Rut mutuniyar Mowab, ka sayi gwauruwar marigayin nan, domin ka riƙe sunan marigayin da kuma kayansa.”
6 And the near relation said, I am not able to do the relation's part, for fear of damaging the heritage I have: you may do it in my place, for I am not able to do it myself.
Da jin haka, sai dangin nan mai fansa ya ce, “To, ba zan iya fanshe shi ba don kada in yi wa nawa mallakar rauni. Za ka iya fanshe shi wa kanka. Ni dai ba zan iya ba.”
7 Now, in earlier times this was the way in Israel when property was taken over by a near relation, or when there was a change of owner. To make the exchange certain one man took off his shoe and gave it to the other; and this was a witness in Israel.
(To, a kwanakin can a Isra’ila, domin a tabbatar da fansa da kuma musayar da mallaka, mutum zai cire takalminsa ya ba wa ɗayan. Wannan ita ce hanyar tabbatar da al’amarin a hukumance a cikin Isra’ila.)
8 So the near relation said to Boaz, Take it for yourself. And he took off his shoe.
Saboda haka dangin nan mai fansa ya ce wa Bowaz, “Saye shi wa kanka.” Sai ya cire takalminsa.
9 Then Boaz said to the responsible men and to all the people, You are witnesses today that I have taken at a price from Naomi all the property which was Elimelech's, and everything which was Chilion's and Mahlon's.
Sa’an nan Bowaz ya yi shela wa dattawa da kuma dukan mutane, “A yau ku ne shaidu cewa na saya daga Na’omi dukan mallakar Elimelek, Kiliyon da kuma Malon.
10 And, further, I have taken Ruth, the Moabitess, who was the wife of Mahlon, to be my wife, to keep the name of the dead man living in his heritage, so that his name may not be cut off from among his countrymen, and from the memory of his town: you are witnesses this day.
Na kuma ɗauki Rut mutuniyar Mowab, gwauruwar Malon a matsayin matata domin sunan mamaci da kuma mallakarsa yă ci gaba, domin kada sunansa yă ɓace daga cikin iyali ko daga tarihin gari. A yau ku ne shaidu!”
11 And all the people who were in the public place, and the responsible men, said, We are witnesses. May the Lord make this woman, who is about to come into your house, like Rachel and Leah, which two were the builders of the house of Israel: and may you have wealth in Ephrathah, and be great in Beth-lehem;
Sai dattawan da kuma dukan waɗanda suke a ƙofar suka ce, “Mu shaidu ne. Bari Ubangiji yă sa macen da take zuwa cikin gidanka ta zama kamar Rahila da Liyatu, waɗanda tare suka gina gidan Isra’ila. Bari ka sami martaba a cikin Efrata ka kuma zama sananne cikin Betlehem.
12 May your family be like the family of Perez, the son whom Tamar gave to Judah, from the offspring which the Lord may give you by this young woman.
Ta wurin’ya’yan da Ubangiji zai ba ka ta wurin wannan mace, bari iyalinka yă zama kamar na Ferez, wanda Tamar ta haifa wa Yahuda.”
13 So Boaz took Ruth and she became his wife; and he went in to her, and the Lord made her with child and she gave birth to a son.
Sai Bowaz ya ɗauki Rut ta kuwa zama matarsa. Sa’an nan ya kwana da ita, Ubangiji kuma ya sa ta yi ciki, ta haifi ɗa.
14 And the women said to Naomi, A blessing on the Lord, who has not let you be this day without a near relation, and may his name be great in Israel.
Mata suka ce wa Na’omi, “Yabo ya tabbata ga Ubangiji, wanda a wannan rana bai bar ki ba tare da dangi mai fansa ba. Allah yă sa yă zama sananne a dukan Isra’ila!
15 He will be a giver of new life to you, and your comforter when you are old, for your daughter-in-law, who, in her love for you, is better than seven sons, has given birth to him.
Zai sabunta rayuwarki yă adana ki a tsufanki. Gama surukarki wadda take ƙaunarki wadda kuma take mafi kyau gare ki fiye da’ya’ya maza bakwai, ta haife shi.”
16 And Naomi took the child and put her arms round it, and she took care of it.
Sai Na’omi ta ɗauki yaron, ta kwantar da shi a cinyarta ta kuma kula da shi.
17 And the women who were her neighbours gave it a name, saying, Naomi has a child; and they gave him the name of Obed: he is the father of Jesse, the father of David.
Matan da suke zama a wurin suka ce, “Na’omi ta sami yaro.” Suka kuwa ba shi suna Obed. Shi ne ya haifi Yesse, mahaifin Dawuda.
18 Now these are the generations of Perez: Perez became the father of Hezron;
Ga asalin zuriyar Ferez. Ferez shi ne mahaifin Hezron,
19 And Hezron became the father of Ram, and Ram became the father of Amminadab;
Hezron ya haifi Ram, Ram ya haifi Amminadab,
20 And Amminadab became the father of Nahshon, and Nahshon became the father of Salmon;
Amminadab ya haifi Nashon, Nashon ya haifi Salmon,
21 And Salmon became the father of Boaz, and Boaz became the father of Obed;
Salmon ya haifi Bowaz, Bowaz ya haifi Obed,
22 And Obed became the father of Jesse, and Jesse became the father of David.
Obed ya haifi Yesse, Yesse kuwa ya haifi Dawuda.