< Ruth 3 >

1 And Naomi, her mother-in-law, said to her, My daughter, am I not to get you a resting-place where you may be in comfort?
Wata rana Na’omi surukar Rut ta ce mata, “’Yata, bai kamata in nema miki gida, inda za a tanada miki da kyau?
2 And now, is there not Boaz, our relation, with whose young women you were? See, tonight he is separating the grain from the waste in his grain-floor.
Bowaz wanda kike aiki da bayinsa’yan mata ba danginmu ne na kusa ba? Da daren yau zai sussuka sha’ir nasa a masussuka.
3 So take a bath, and, after rubbing your body with sweet oil, put on your best robe, and go down to the grain-floor; but do not let him see you till he has come to the end of his meal.
Ki yi wanka ki fesa turare, ki kuma sa tufafinki mafi kyau. Sa’an nan ki gangara zuwa masussuka, amma kada ki bari yă san cewa kina a can sai ya gama ci da sha.
4 But see to it, when he goes to rest, that you take note of the place where he is sleeping, and go in there, and, uncovering his feet, take your place by him; and he will say what you are to do.
Sa’ad da ya kwanta, ki lura da inda yake kwance. Sa’an nan ki tafi ki buɗe ƙafafunsa ki kwanta. Zai faɗa miki abin da za ki yi.”
5 And she said, I will do all you say.
Rut ta amsa ta ce “Zan yi abin da kika faɗa.”
6 So she went down to the grain-floor and did all her mother-in-law had said to her.
Saboda haka ta gangara zuwa masussuka ta kuma yi dukan abin da surukarta ta ce ta yi.
7 Now when Boaz had taken meat and drink, and his heart was glad, he went to take his rest at the end of the mass of grain; then she came softly and, uncovering his feet, went to rest.
Sa’ad da Bowaz ya gama ci da sha yana kuma cikin farin ciki, sai ya tafi ya kwanta a ƙarshen tarin hatsi. Rut kuwa ta sulalle ta je ta buɗe ƙafafunsa ta kwanta.
8 Now in the middle of the night, the man awaking from his sleep in fear, and lifting himself up, saw a woman stretched at his feet.
Da tsakar dare sai wani abu ya firgitar da mutumin, ya kuwa juya sai ya tarar da mace kwance a ƙafafunsa.
9 And he said, Who are you? And she answering said, I am your servant Ruth: take your servant as wife, for you are a near relation.
Sai ya yi tambaya ya ce, “Ke wace ce?” Ta amsa ta ce, “Ni ce baranyarka Rut, ka rufe ni ta mayafinka da yake kai dangi, mai fansa ne na kusa.”
10 And he said, May the Lord give you his blessing, my daughter: even better than what you did at the first is this last kind act you have done, in not going after young men, with or without wealth.
Sai ya amsa ya ce, “Ubangiji yă albarkace ki’yata. Wannan alheri ya fi wannan da kika nuna da farko. Ba ki gudu kin bi saurayi, mai arziki ko matalauci ba.
11 And now, my daughter, have no fear; I will do for you whatever you say: for it is clear to all my townspeople that you are a woman of virtue.
Yanzu kuwa’yata kada ki ji tsoro. Zan yi miki dukan abin da kika roƙa. Dukan’yan’uwana na gari sun san cewa ke mace ce mai halin kirki.
12 Now it is true that I am a near relation: but there is a relation nearer than I.
Ko da yake gaskiya ne ni dangi ne na kusa, amma akwai dangi mai fansa mafi kusa fiye da ni.
13 Take your rest here tonight; and in the morning, if he will do for you what it is right for a relation to do, very well, let him do so: but if he will not, then by the living Lord I myself will do so.
Ki kwana a nan, da safe kuwa in yana so yă fansa, to, da kyau, sai yă fansa. Amma in ba ya niyya, tabbatacce, na rantse da Ubangiji mai rai zan yi. Ki kwanta a nan sai da safe.”
14 And she took her rest at his feet till the morning: and she got up before it was light enough for one to see another. And he said, Let it not come to anyone's knowledge that the woman came to the grain-floor.
Saboda haka ta kwanta a ƙafafunsa sai da safe, amma ta tashi kafin a gane wani, sai ya ce, “Kada ki bar wani yă san cewa mace ta zo masussuka.”
15 And he said, Take your robe, stretching it out in your hands: and she did so, and he took six measures of grain and put them into it, and gave it her to take: and she went back to the town.
Ya kuma ce, “Ki kawo gyalenki da kika yafa ki shimfiɗa shi a nan.” Sa’ad da ta yi haka, sai ya zuba mudu shida na sha’ir ya sa mata a kai. Sa’an nan ya koma gari.
16 And when she came back her mother-in-law said to her, How did it go with you, my daughter? And she gave her an account of all the man had done to her.
Sa’ad da Rut ta koma wurin surukarta Na’omi ta tambaye ta “Yaya aka yi’yata?” Sai ta faɗa mata dukan abin da Bowaz ya yi mata
17 And she said, He gave me these six measures of grain, saying, Do not go back to your mother-in-law with nothing in your hands.
ta kuma ƙara da cewa, “Ya ba ni waɗannan mudu shida na sha’ir, yana cewa, ‘Kada ki koma wurin surukarki hannu wofi.’”
18 Then she said, Do nothing now, my daughter, till you see what will come of this; for the man will take no rest till he has put this thing through.
Sai Na’omi ta ce, “Ki jira,’yata, sai kin ga abin da zai faru. Gama mutumin ba zai huta ba sai an warware batun a yau.”

< Ruth 3 >