< Romans 3 >
1 How then is the Jew better off? or what profit is there in circumcision?
To ina fifikon da bayahude yake dashi? Kuma ina ribar kaciya?
2 Much in every way: first of all because the words of God were given to them.
Akwai muhimmancinsu ta kowacce hanya. Tun farko dai, yahudawa ne aka dankawa wahayi daga Allah.
3 And if some have no faith, will that make the faith of God without effect?
Idan wasu yahudawa basu bada gaskiya ba fa? Rashin bangaskiyarsu zai hana amincin Allah aiki?
4 In no way: but let God be true, though every man is seen to be untrue; as it is said in the Writings, That your words may be seen to be true, and you may be seen to be right when you are judged.
Bazai taba zama haka ba. Maimakon haka, bari Allah ya zama mai gaskiya, ko da kowanne mutum makaryaci ne. Kamar yadda aka rubuta, “Domin a nuna kai mai adalci cikin maganganunka, kuma kayi nasara a lokacin da aka kawo ka gaban shari'a.”
5 But if the righteousness of God is supported by our wrongdoing what is to be said? is it wrong for God to be angry (as men may say)?
Amma idan rashin adalcinmu ya nuna adalcin Allah, to me zamu ce? Allah ba marar adalci ba ne, wanda ke aiwatar da fushinsa, ko kuwa? Ina magana bisa ga tunanin mutuntaka.
6 In no way: because if it is so, how is God able to be the judge of all the world?
Bazai taba zama haka ba. Domin idan haka ne ta yaya Allah zai shar'anta duniya?
7 But if, because I am untrue, God being seen to be true gets more glory, why am I to be judged as a sinner?
Amma idan gaskiyar Allah ta wurin karyata ta habaka yabonsa, To me yasa ake shar'anta ni a matsayin mai zunubi?
8 Let us not do evil so that good may come (a statement which we are falsely said by some to have made), because such behaviour will have its right punishment.
To me zai hana ace kamar yadda ake fadin zancen karya a kanmu, wasu kuma sun dauka cewa mun fadi hakan, “Bari muyi mugunta, domin nagarta tazo?” Hukuncin su halal ne.
9 What then? are we worse off than they? In no way: because we have before made it clear that Jews as well as Greeks are all under the power of sin;
To me kenan? Zamu ba kanmu hujja ne? ko kadan. Domin mun riga munyi zargin yahudawa da hellinawa, da cewar dukkansu, suna karkashin zunubi.
10 As it is said in the holy Writings, There is not one who does righteousness;
Kamar yadda aka rubuta, babu wani mai adalci, babu ko daya.
11 Not one who has the knowledge of what is right, not one who is a searcher after God;
Babu wani mai fahimta. Babu wani mai neman Allah.
12 They have all gone out of the way, there is no profit in any of them; there is not one who does good, not so much as one:
Dukansu sun kauce hanya, dukansu gaba daya sun zama marasa amfani. Babu mai aikin nagarta, a'a, babu ko da guda daya.
13 Their throat is like an open place of death; with their tongues they have said what is not true: the poison of snakes is under their lips:
Makogwaronsu a bude yake kamar kabari. Harsunansu na dauke da cuta. Dafin macizai na karkashin lebunansu.
14 Whose mouth is full of curses and bitter words:
Bakunansu cike suke da la'ana da daci.
15 Their feet are quick in running after blood;
Sawayensu na saurin zuwa zubar da jini.
16 Destruction and trouble are in their ways;
Tafarkinsu wahala ce da lalacewa.
17 And of the way of peace they have no knowledge:
Wadannan mutane basu san hanyar salama ba.
18 There is no fear of God before their eyes.
Babu tsoron Allah a idanunsu.”
19 Now, we have knowledge that what the law says is for those who are under the law, so that every mouth may be stopped, and all men may be judged by God:
To mun san dai duk abin da shari'a tace, shari'a na magana ne da wadanda ke karkashinta, domin a rufe kowanne baki, domin dukan duniya ta bada amsa a gaban Allah.
20 Because by the works of the law no man is able to have righteousness in his eyes, for through the law comes the knowledge of sin.
Domin a gabansa babu wanda zai barata ta wurin ayukan shari'a. Domin ta wurin shari'a ne sanin zunubi yazo.
21 But now without the law there is a revelation of the righteousness of God, to which witness is given by the law and the prophets;
Amma yanzu ba tare da shari'a ba an bayyana sanin adalcin Allah, wanda shari'a da annabawa suke shaidawa.
22 That is, the righteousness of God through faith in Jesus Christ, to all those who have faith; and one man is not different from another,
Wato, adalcin Allah ta wurin bangaskiya cikin Yesu Almasihu ga dukkan wadanda ke bada gaskiya. Domin babu bambanci:
23 For all have done wrong and are far from the glory of God;
Domin duk sun yi zunubi sun kuma kasa kaiwa ga darajar Allah,
24 And they may have righteousness put to their credit, freely, by his grace, through the salvation which is in Christ Jesus:
Da alherinsa an baratar da mu ta wurin fansar dake cikin Yesu Almasihu.
25 Whom God has put forward as the sign of his mercy, through faith, by his blood, to make clear his righteousness when, in his pity, God let the sins of earlier times go without punishment;
Amma Allah ya bayar da Yesu Almasihu wanda yake hadayar fansa ta wurin bangaskiya cikin jininsa. Ya mika Almasihu a matsayin tabbacin hukuncinsa, sabo da kuma ketarewar zunubanmu na baya
26 And to make clear his righteousness now, so that he might himself be upright, and give righteousness to him who has faith in Jesus.
cikin hakurinsa. Duk wannan ya faru ne domin a bayyana adalcinsa cikin wannan zamani, domin ya tabbatar da kansa mai hukunci, kuma ya nuna shine mai baratar da kowa saboda bangaskiya cikin Yesu.
27 What reason, then, is there for pride? It is shut out. By what sort of law? of works? No, but by a law of faith.
To ina fahariya? An fitar da ita. A kan wane dalilin? Don ayyuka? A'a, amma ta dalilin bangaskiya.
28 For this reason, then, a man may get righteousness by faith without the works of the law.
Domin wannan muka kammala cewar ana baratar da mutum ta wurin bangaskiya ba tare da ayyukan shari'a ba.
29 Or is God the God of Jews only? is he not in the same way the God of Gentiles? Yes, of Gentiles:
Ko kuwa Allah Allahn yahudawa ne kadai? Shi ba Allahn al'ummai bane? I, na al'ummai ne kuma.
30 If God is one; and he will give righteousness because of faith to those who have circumcision, and through faith to those who have not circumcision.
Idan dai lallai Allah daya ne, zai baratar da mai kaciya ta wurin bangaskiya, da marar kaciya kuma ta wurin bangaskiya.
31 Do we, then, through faith make the law of no effect? in no way: but we make it clear that the law is important.
Mun kawar da shari'a kenan ta wurin bangaskiya? ba zai taba kasancewa haka ba. Maimako ma, muna inganta shari'a kenan.