< Psalms 90 >
1 A Prayer of Moses, the man of God. Lord, you have been our resting-place in all generations.
Addu’ar Musa Mutumin Allah. Ubangiji kai ne mazauninmu cikin dukan zamanai.
2 Before the mountains were made, before you had given birth to the earth and the world, before time was, and for ever, you are God.
Kafin a haifi duwatsu ko a fid da ƙasa da duniya, daga madawwami zuwa madawwami kai Allah ne.
3 You send man back to his dust; and say, Go back, you children of men.
Ka komar da mutane zuwa ƙura, kana cewa, “Ku koma ƙura, ya ku’ya’yan mutane.”
4 For to you a thousand years are no more than yesterday when it is past, and like a watch in the night.
Gama shekaru dubu a gabanka kamar kwana ɗaya ne da ya wuce, ko sa’a guda na dare.
Ka share mutane cikin barcin mutuwa; suna kama da sabuwa ciyawar safiya,
6 In the morning it is green; in the evening it is cut down, and becomes dry.
ko da yake da safe takan yi sabuwar huda da yamma sai ta bushe ta kuma yanƙwane.
7 We are burned up by the heat of your passion, and troubled by your wrath.
An cinye mu ta wurin fushinka mun kuma razana ta wurin hasalarka.
8 You have put our evil doings before you, our secret sins in the light of your face.
Ka ajiye laifinmu a gabanka, asirin zunubanmu a hasken kasancewarka.
9 For all our days have gone by in your wrath; our years come to an end like a breath.
Dukan kwanakinmu sun wuce ƙarƙashin fushinka; mun gama shekarunmu da nishi.
10 The measure of our life is seventy years; and if through strength it may be eighty years, its pride is only trouble and sorrow, for it comes to an end and we are quickly gone.
Tsawon kwanakinmu shekaru saba’in ne, ko tamanin, in muna da ƙarfi; duk da haka tsawonsu wahaloli ne kawai da ɓacin rai, gama da sauri suke wucewa, ta mu kuma ta ƙare.
11 Who has knowledge of the power of your wrath, or who takes note of the weight of your passion?
Wa ya san ƙarfin fushinka? Gama hasalarka tana da girma kamar tsoron da ya dace da kai.
12 So give us knowledge of the number of our days, that we may get a heart of wisdom.
Ka koya mana yawan kwanakinmu daidai, don mu sami zuciyar hikima.
13 Come back, O Lord; how long? let your purpose for your servants be changed.
Ka ji mu, ya Ubangiji! Har yaushe zai ci gaba? Ka ji tausayin bayinka.
14 In the morning give us your mercy in full measure; so that we may have joy and delight all our days.
Ka ƙosar da mu da safe da ƙaunarka marar ƙarewa, don mu rera don yabo, mu kuma yi murna dukan kwanakinmu.
15 Make us glad in reward for the days of our sorrow, and for the years in which we have seen evil.
Faranta mana zuciya kamar yawan kwanakin da muka sha azaba, kamar yawan shekarun da muka ga wahala.
16 Make your work clear to your servants, and your glory to their children.
Bari a nuna ayyukanka ga bayinka, darajarka ga’ya’yansu.
17 Let the pleasure of the Lord our God be on us: O Lord, give strength to the work of our hands.
Bari alherin shugabanmu Allah yă kasance a kanmu; ka albarkaci mana aikin hannuwanmu, I, ka albarkaci aikin hannuwanmu.