< Psalms 54 >
1 To the chief music-maker; on Neginoth. Maschil. Of David. When the Ziphites came and said to Saul, Is not David keeping himself secret among us? Let your name be my salvation, O God; let my cause be judged by your strength.
Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Da kayan kiɗi masu tsirkiya. Wani maskil ta Dawuda. Sa’ad da Zifawa suka tafi wurin Shawulu suka ce, “Ba Dawuda ba ne yake ɓuya a cikinmu?” Ka cece ni, ya Allah ta wurin sunanka; ka nuna ni marar laifi ne ta wurin ƙarfinka.
2 Let my prayer come before you, O God; give ear to the words of my mouth.
Ka ji addu’ata, ya Allah; ka saurari maganar bakina.
3 For men who are going after me have come out against me, violent men are purposing to take my soul; they have not put God before their eyes. (Selah)
Baƙi suna kawo mini hari; mutane marasa imani suna neman raina, mutanen da ba sa tsoron Allah. (Sela)
4 See, God is my helper: the Lord is the great supporter of my soul.
Tabbatacce Allah ne mai taimakona, Ubangiji shi ne wanda yake riƙe ni.
5 Let the evil works of my haters come back on them again; let them be cut off by your good faith.
Bari mugunta ta shaƙe masu magana marar kyau a kaina; cikin amincinka ka hallaka su.
6 Freely will I make my offerings to you; I will give praise to your name, O Lord, for it is good.
Zan miƙa hadaya ta yardar rai gare ka; zan yabe sunanka, ya Ubangiji, gama yana da kyau.
7 Because it has been my saviour from all my trouble; and my eyes have seen the punishment of my haters.
Gama ya cece ni daga dukan wahalolina, idanuna kuma sun ga an yi nasara a kan maƙiyana.