< Psalms 46 >

1 To the chief music-maker. Of the sons of Korah; put to Alamoth. A Song. God is our harbour and our strength, a very present help in trouble.
Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Ta’Ya’yan Kora maza. Bisa ga alamot Waƙa ce. Allah ne mafakarmu da ƙarfinmu, kullum yana a shirye yă taimaka a lokacin wahala.
2 For this cause we will have no fear, even though the earth is changed, and though the mountains are moved in the heart of the sea;
Saboda haka ba za mu ji tsoro ba, ko da ƙasa ta girgiza duwatsu kuma suka fāɗi cikin zurfin teku,
3 Though its waters are sounding and troubled, and though the mountains are shaking with their violent motion. (Selah)
ko da ruwansa suna ruri suna kumfa duwatsu kuma suna girgiza da tumbatsansu. (Sela)
4 There is a river whose streams make glad the resting-place of God, the holy place of the tents of the Most High.
Akwai kogi mai rafuffukan da suke sa birnin Allah murna, tsattsarkan wuri inda Mafi Ɗaukaka ke zama.
5 God has taken his place in her; she will not be moved: he will come to her help at the dawn of morning.
Allah yana cikinta, ba za tă fāɗi ba; Allah zai taimake ta da safe.
6 The nations were angry, the kingdoms were moved; at the sound of his voice the earth became like wax.
Al’ummai suna hayaniya, mulkoki sun fāɗi; ya ɗaga muryarsa, duniya ta narke.
7 The Lord of armies is with us; the God of Jacob is our high tower. (Selah)
Ubangiji Maɗaukaki yana tare da mu; Allah na Yaƙub ne kagararmu. (Sela)
8 Come, see the works of the Lord, the destruction which he has made in the earth.
Zo ku ga ayyukan Ubangiji, kangon da ya kawo a kan duniya.
9 He puts an end to wars over all the earth; by him the bow is broken, and the spear cut in two, and the carriage burned in the fire.
Ya sa yaƙoƙi suka yi tsit ko’ina a duniya. Ya kakkarya bakkuna ya kuma ragargaza māsu, ya ƙone garkuwoyi da wuta.
10 Be at peace in the knowledge that I am God: I will be lifted up among the nations, I will be honoured through all the earth.
“Ku natsu ku kuma san cewa ni ne Allah; za a ɗaukaka ni a cikin al’ummai, za a ɗaukaka ni cikin duniya.”
11 The Lord of armies is with us; the God of Jacob is our high tower. (Selah)
Ubangiji Maɗaukaki yana tare da mu; Allah na Yaƙub ne kagararmu. (Sela)

< Psalms 46 >