< Psalms 44 >
1 To the chief music-maker. Of the sons of Korah Maschil. It has come to our ears, O God, our fathers have given us the story, of the works which you did in their days, in the old times,
Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Ta’ya’yan Kora maza. Maskil ne. Mun ji da kunnuwanmu, ya Allah; kakanninmu sun faɗa mana abin da ka aikata a kwanakinsu, tun dā can.
2 Uprooting the nations with your hand, and planting our fathers in their place; cutting down the nations, but increasing the growth of your people.
Da hannunka ka kori al’ummai ka kuma dasa kakanninmu; ka ragargaza mutanen ka kuma sa kakanninmu suka haɓaka.
3 For they did not make the land theirs by their swords, and it was not their arms which kept them safe; but your right hand, and your arm, and the light of your face, because you had pleasure in them.
Ba da takobinsu ba ne suka ci ƙasar, ba kuwa ƙarfin hannunsu ne ya ba su nasara ba; hannun damanka ne, ƙarfin hannunka, da kuma hasken fuskarka, gama ka ƙaunace su.
4 You are my King and my God; ordering salvation for Jacob.
Kai ne Sarkina da kuma Allahna, wanda ya ba da nasarori wa Yaƙub.
5 Through you will we overcome our haters; by your name will they be crushed under our feet who are violent against us.
Ta wurinka mun tura abokan gābanmu baya; ta wurin sunanka muka tattake maƙiyanmu.
6 I will not put faith in my bow, my sword will not be my salvation.
Ba na dogara ga bakana, takobina ba ya kawo nasara;
7 But it is you who have been our saviour from those who were against us, and have put to shame those who had hate for us.
amma kana ba mu nasara a kan abokan gābanmu, ka sa abokan gābanmu suka sha kunya.
8 Our pride is in God at all times, to his name we give praise for ever. (Selah)
A cikin Allah muke fariyarmu dukan yini, kuma za mu yabi sunanka har abada. (Sela)
9 But now you have sent us away from you, and put us to shame; you do not go out with our armies.
Amma yanzu ka ƙi mu ka kuma ƙasƙantar da mu; ba ka ƙara fita tare da mayaƙanmu.
10 Because of this we are turned back by the attacker: those who have hate for us take our goods for themselves.
Ka sa muka gudu a gaban abokin gāba, kuma abokan gābanmu suka washe mu.
11 You have made us like sheep which are taken for meat; we are put to flight among the nations.
Ka ba da mu a cinye kamar tumaki ka kuma watsar da mu a cikin al’ummai.
12 You let your people go for nothing; your wealth is not increased by their price.
Ka sayar da mutanenka a kuɗin da bai taka ƙara ya karye ba babu wata riba daga sayar da su da ka yi.
13 You have made us to be looked down on by our neighbours, we are laughed at and shamed by those who are round about us.
Ka mai da mu abin dariya ga maƙwabtanmu, abin dariya da reni ga waɗanda suke kewaye da mu.
14 Our name is a word of shame among the nations, a sign for the shaking of heads among the peoples.
Ka sa muka zama abin ba’a a cikin al’ummai; mutanen suna kaɗa mana kai.
15 My downfall is ever before me, and I am covered with the shame of my face;
Dukan yini ina cikin wulaƙanci, fuskata kuma ta rufu da kunya
16 Because of the voice of him who says sharp and bitter words; because of the hater and him who is the instrument of punishment.
saboda ba’ar waɗanda suke zagi suke kuma ƙina, saboda abokan gābana, waɗanda suka sha alwashi sai sun yi ramuwa.
17 All this has come on us, but still we have kept you in our memory; and we have not been false to your word.
Dukan wannan ya faru da mu, ko da yake ba mu manta da kai ba ko mu kasance masu ƙarya ga alkawarinka.
18 Our hearts have not gone back, and our steps have not been turned out of your way;
Zukatanmu ba su juya baya; ƙafafunmu ba su kauce daga hanyarka ba.
19 Though you have let us be crushed in the place of jackals, though we are covered with darkest shade.
Amma ka ragargaza mu ka kuma maishe mu abin farautar karnukan jeji ka kuma rufe mu cikin duhu baƙi ƙirin.
20 If the name of our God has gone out of our minds, or if our hands have been stretched out to a strange god,
Da a ce mun manta da sunan Allahnmu ko mun miƙa hannuwanmu ga baƙin alloli,
21 Will not God make search for it? for he sees the secrets of the heart.
da Allah bai gane ba, da yake ya san asiran zuciya?
22 Truly, because of you we are put to death every day; we are numbered like sheep for destruction.
Duk da haka saboda kai mun fuskanci mutuwa dukan yini; aka ɗauke mu kamar tumakin da za a yanka.
23 Why are you sleeping, O Lord? awake! and come to our help, do not give us up for ever.
Ka farka, ya Ubangiji! Don me kake barci? Ta da kanka! Kada ka ƙi mu har abada.
24 Why is your face covered, and why do you give no thought to our trouble and our cruel fate?
Me ya sa ka ɓoye fuskarka ka manta da azabanmu da kuma danniyar da ake mana?
25 For our souls are crushed down to the dust: our bodies are stretched out on the earth.
An kai mu ƙasa zuwa ƙura; jikunanmu sun manne da ƙasa.
26 Up! and come to our help, and give us salvation because of your mercy.
Ka tashi ka taimake mu; ka cece mu saboda ƙaunarka marar ƙarewa.