< Psalms 35 >
1 Of David. O Lord, be on my side against those who are judging me; be at war with those who make war against me.
Ta Dawuda. Yi hamayya, ya Ubangiji, da waɗanda suke hamayya da ni; yi faɗa da waɗanda suke faɗa da ni.
2 Be a breastplate to me, and give me your help.
Ka ɗauki garkuwa da kuma makami; ka tashi ka taimake ni.
3 Take up your spear and keep back my attackers; say to my soul, I am your salvation.
Ka ɗaga māshi da kuma abin da ake jefa a kan waɗanda suke fafarata. Ka ce wa raina, “Ni ne cetonka.”
4 Let them be overcome and put to shame who make attempts to take my soul; let those who would do me damage be turned back and made foolish.
Bari waɗanda suke neman raina su sha kunya a kuma kunyatar da su; bari waɗanda suke shirya lalacewata su juya da baya su ruɗe.
5 Let them be like dust from the grain before the wind; let the angel of the Lord send them in flight.
Bari su zama kamar yayi a gaban iska, mala’ikan Ubangiji kuma yana korarsu;
6 Let their way be dark and full of danger; let them be troubled by the angel of the Lord.
bari hanyarsu tă yi duhu ta kuma yi santsi, mala’ikan Ubangiji kuma yana fafararsu.
7 For without cause they have put a net ready for me secretly, in which to take my soul.
Da yake sun ɓoye tarko domina ba dalili kuma babu dalili suka haƙa mini rami,
8 Let destruction come on them without their knowledge; let them be taken themselves in their secret nets, falling into the same destruction.
bari lalaci yă kama su ba zato, bari tarkon da suka ɓoye yă kama su, bari su fāɗa cikin ramin, yă kai ga lalacinsu.
9 And my soul will have joy in the Lord; it will be glad in his salvation.
Sa’an nan raina zai cika da farin ciki a cikin Ubangiji in yi kuma murna a cikin cetonsa.
10 All my bones will say, Lord, who is like you? The saviour of the poor man from the hands of the strong, of him who is poor and in need from him who takes his goods.
Dukan raina zai ce, “Wane ne kamar ka, ya Ubangiji? Ka kuɓutar da matalauta daga waɗanda suka fi ƙarfinsu, matalauta da masu bukata daga waɗanda suke musu fashi.”
11 False witnesses got up: they put questions to me about crimes of which I had no knowledge.
Shaidu marasa imani sun fito; suna mini tambaya a kan abubuwan da ban san kome a kai ba.
12 They gave me back evil for good, troubling my soul.
Suna sāka alherin da na yi musu da mugunta suka bar raina da nadama.
13 But as for me, when they were ill I put on the clothing of sorrow: I went without food and was sad, and my prayer came back again to my heart.
Duk da haka sa’ad da suke ciwo, na sanya rigar makoki na ƙasƙantar da kaina da azumi. Sa’ad da aka mayar mini da addu’o’i babu amsa,
14 My behaviour was as if it had been my friend or my brother: I was bent low in grief like one whose mother is dead.
nakan yi ta yawo ina makoki sai ka ce yadda nake yi wa abokina ko ɗan’uwana. Nakan sunkuyar da kaina cikin baƙin ciki sai ka ce ina kuka domin mahaifiyata.
15 But they took pleasure in my trouble, and came together, yes, low persons came together against me without my knowledge; they never came to an end of wounding me.
Amma sa’ad da na yi tuntuɓe, sukan taru suna murna; masu kai hari sun taru a kaina sa’ad da ban sani ba. Suna ɓata mini suna ba tsagaitawa.
16 Like men of deceit they put me to shame; the voice of their wrath was loud against me.
Kamar marasa sani Allah suna mini riyar ba’a; Suna hararata da ƙiyayya.
17 Lord, how long will you be looking on? take my soul from their destruction, my life from the lions.
Ya Ubangiji, har yaushe za ka ci gaba da zuba ido kawai? Ka kuɓutar da raina daga farmakinsu, raina mai daraja daga waɗannan zakoki.
18 I will give you praise in the great meeting; I will give you honour among a strong people.
Zan yi godiya cikin taro mai girma; cikin ɗumbun mutane zan yabe ka.
19 Do not let my haters be glad over me falsely; let not those who are against me without cause make sport of me.
Kada ka bar maƙaryatan nan, su yi farin ciki a kaina; kada ka bar waɗanda suke ƙina ba dalili, su ji daɗin baƙin cikina.
20 For they do not say words of peace; in their deceit they are designing evil things against the quiet ones in the land.
Ba sa maganar salama sukan ƙirƙiro zage-zagen ƙarya a kan waɗanda suka zama shiru a ƙasar.
21 Their mouths were open wide against me, and they said, Aha, aha, our eyes have seen it.
Sukan wage mini bakinsu suna cewa, “Allah yă ƙara! Da idanunmu mun gani.”
22 You have seen this, O Lord; be not unmoved: O Lord, be not far from me.
Ya Ubangiji, ka ga wannan; kada ka yi shiru. Kada ka yi nisa da ni, ya Ubangiji.
23 Be awake, O Lord, be moved to take up my cause, my God and my Lord.
Ka farka, ka kuma tashi ka kāre ni! Ka yi mini faɗa, ya Allahna da shugabana.
24 Be my judge, O Lord my God, in your righteousness; do not let them be glad over me.
Ka nuna ni marar laifi ne ciki adalcinka, Ya Ubangiji Allahna; kada ka bari su yi farin ciki a kaina.
25 Let them not say in their hearts, So we will have it: let them not say, We have put an end to him.
Kada ka bari su ce wa kansu, “Allah yă ƙara, dā ma abin da mun so ke nan!” Ko su ce, “Mun haɗiye shi.”
26 Let all those who take pleasure in my troubles be shamed and come to nothing: let those who are lifted up against me be covered with shame and have no honour.
Bari dukan waɗanda suke farin ciki a kaina a wahalata su sha kunya su kuma ruɗe; bari dukan waɗanda suke ɗaukar kansu sun fi ni su sha kunya da wulaƙanci.
27 Let those who are on my side give cries of joy; let them ever say, The Lord be praised, for he has pleasure in the peace of his servant.
Bari waɗanda suke murna saboda nasarata su yi sowa don farin ciki da murna; bari kullum su riƙa cewa, “A ɗaukaka Ubangiji, wanda yake farin ciki da zaman lafiyar bawansa.”
28 And my tongue will be talking of your righteousness and of your praise all the day.
Harshena zai yi zancen adalcinka da kuma yabonka dukan yini.