< Psalms 142 >
1 Maschil. Of David. A prayer when he was in the hole of the rock. The sound of my cry went up to the Lord; with my voice I made my prayer for grace to the Lord.
Maskil ne ta Dawuda. Sa’ad da yake cikin kogo. Addu’a ce. Na yi kuka mai ƙarfi ga Ubangiji; na tā da muryata ga Ubangiji neman jinƙai.
2 I put all my sorrows before him; and made clear to him all my trouble.
Na kawo gunagunina a gabansa; a gabansa na faɗa wahalata.
3 When my spirit is overcome, your eyes are on my goings; nets have been secretly placed in the way in which I go.
Sa’ad da ƙarfina ya kāre a cikina, kai ne wanda ya san hanyata. A hanyar da nake tafiya mutane sun kafa mini tarko.
4 Looking to my right side, I saw no man who was my friend: I had no safe place; no one had any care for my soul.
Duba ta damata ka gani; babu wanda ya kula da ni. Ba ni da mafaka; babu wanda ya kula da raina.
5 I have made my cry to you, O Lord; I have said, You are my safe place, and my heritage in the land of the living.
Na yi kuka gare ka, ya Ubangiji; Na ce, “Kai ne mafakata, rabona a ƙasar masu rai.”
6 Give ear to my cry, for I am made very low: take me out of the hands of my haters, for they are stronger than I.
Ka saurari kukata, gama ina cikin matsananciyar bukata; ka cece ni daga waɗanda suke fafarata, gama sun fi ni ƙarfi sosai.
7 Take my soul out of prison, so that I may give praise to your name: the upright will give praise because of me; for you have given me a full reward.
Ka’yantar da ni daga kurkuku, don in yabi sunanka. Ta haka masu adalci za su taru kewaye da ni saboda alherinka gare ni.