< Psalms 122 >
1 A Song of the going up. Of David. I was glad because they said to me, We will go into the house of the Lord.
Waƙar haurawa. Ta Dawuda. Na yi farin ciki tare da waɗanda suka ce da ni, “Bari mu tafi gidan Ubangiji.”
2 At last our feet were inside your doors, O Jerusalem.
Ƙafafunmu suna tsaye a ƙofofinki, ya Urushalima.
3 O Jerusalem, you are like a town which is well joined together;
An gina Urushalima kamar birnin da aka yi a harhaɗe wuri guda.
4 To which the tribes went up, even the tribes of the Lord, for a witness to Israel, to give praise to the name of the Lord.
A can ne kabilu suke haurawa, kabilan Ubangiji, don su yabi sunan Ubangiji bisa ga farillan da aka ba wa Isra’ila.
5 For there seats for the judges were placed, even the rulers' seats of the line of David.
A can kursiyoyin shari’a yake tsaye, kursiyoyin gidan Dawuda.
6 O make prayers for the peace of Jerusalem; may they whose love is given to you do well.
Ku yi addu’a don salamar Urushalima, “Bari waɗanda suke ƙaunarki su zauna lafiya.
7 May peace be inside your walls, and wealth in your noble houses.
Bari salama ta kasance a katangarki zaman lafiya kuma a fadodinki.”
8 Because of my brothers and friends, I will now say, Let peace be with you.
Saboda’yan’uwana da kuma abokaina, zan ce, “Salama tă kasance tare da ke.”
9 Because of the house of the Lord our God, I will be working for your good.
Saboda gidan Ubangiji Allahnmu, zan nemi wadatarki.