< Psalms 119 >

1 ALEPH Happy are they who are without sin in their ways, walking in the law of the Lord.
Albarka ta tabbata ga waɗanda rayuwarsu ba ta da abin zargi, waɗanda suke tafiya bisa ga dokar Ubangiji.
2 Happy are they who keep his unchanging word, searching after him with all their heart.
Albarka ta tabbata ga waɗanda suke kiyaye ƙa’idodinsa suke kuma nemansa da dukan zuciyarsu.
3 They do no evil; they go in his ways.
Ba sa yin wani abin da ba daidai ba; suna tafiya a hanyoyinsa.
4 You have put your orders into our hearts, so that we might keep them with care.
Ka shimfiɗa farillan da dole a yi biyayya da su.
5 If only my ways were ordered so that I might keep your rules!
Kash, da a ce hanyoyina tsayayyu ne a yin biyayya da ƙa’idodinka mana!
6 Then I would not be put to shame, as long as I have respect for all your teaching.
Da ba zan sha kunya ba sa’ad da na lura da dukan umarnanka.
7 I will give you praise with an upright heart in learning your right decisions.
Zan yabe ka da zuciya ta gaskiya yayinda nake koyon dokokinka masu adalci.
8 I will keep your rules: O give me not up completely.
Zan yi biyayya da ƙa’idodinka; kada ka yashe ni ɗungum.
9 BETH How may a young man make his way clean? by guiding it after your word.
Yaya matashi zai kiyaye hanyarsa da tsabta? Sai ta yin rayuwa bisa ga maganarka.
10 I have made search for you with all my heart: O let me not go wandering far from your teaching.
Na neme ka da dukan zuciyata; kada ka bar ni in kauce daga umarnanka.
11 I have kept your sayings secretly in my heart, so that I might do no sin against you.
Na ɓoye maganarka a cikin zuciyata don kada in yi maka zunubi.
12 Praise be to you, O Lord: give me knowledge of your rules.
Yabo ya tabbata gare ka, ya Ubangiji; ka koya mini ƙa’idodinka.
13 With my lips have I made clear all the decisions of your mouth.
Da leɓunana na ba da labarin dukan dokokin da suka fito bakinka.
14 I have taken as much delight in the way of your unchanging word, as in all wealth.
Na yi farin ciki da bin farillanka yadda mutum yakan yi farin ciki da arziki mai yawa.
15 I will give thought to your orders, and have respect for your ways.
Na yi tunani a kan farillanka na kuma lura da hanyoyinka.
16 I will have delight in your rules; I will not let your word go out of my mind.
Na yi murna a cikin ƙa’idodinka; ba zan ƙyale maganarka ba.
17 GIMEL Give me, your servant, the reward of life, so that I may keep your word;
Ka yi alheri ga bawanka, zan kuwa rayu; zan yi biyayya da maganarka.
18 Let my eyes be open to see the wonders of your law.
Ka buɗe idanuna don in iya gani abubuwan banmamaki a cikin dokarka.
19 I am living in a strange land: do not let your teachings be kept secret from me.
Ni baƙo ne a duniya; kada ka ɓoye mini umarnanka.
20 My soul is broken with desire for your decisions at all times.
Zuciyata ta ƙosa saboda marmari don dokokinka koyaushe.
21 Your hand has been against the men of pride, a curse is on those who go wandering out of your way.
Ka tsawata wa masu fariya, waɗanda suke la’anta waɗanda kuma suka kauce daga umarnanka.
22 Take away from me shame and bitter words; for I have kept your unchanging word in my heart.
Ka cire mini ba’a da reni, gama ina kiyaye farillanka.
23 Rulers make evil designs against me; but your servant gives thought to your rules.
Ko da yake masu mulki sun zauna tare suna ɓata mini suna, bawanka zai yi tunani a kan ƙa’idodinka.
24 Your unchanging word is my delight, and the guide of my footsteps.
Farillanka ne abin farin cikina; su ne mashawartana.
25 DALETH My soul is joined to the dust: O give me life, in keeping with your word.
An kwantar da ni ƙasa cikin ƙura; ka kiyaye raina bisa ga maganarka.
26 I put the record of my ways before you, and you gave me an answer: O give me knowledge of your rules.
Na ba da labari hanyoyina ka kuma amsa mini; ka koya mini ƙa’idodinka.
27 Make the way of your orders clear to me; then my thoughts will be ever on your wonders.
Bari in gane koyarwar farillanka; sa’an nan zan yi tunani a kan abubuwan banmamakinka.
28 My soul is wasted with sorrow; give me strength again in keeping with your word
Raina ya gaji da baƙin ciki; ka ƙarfafa ni bisa ga maganarka.
29 Take from me every false way; and in mercy give me your law.
Ka kiyaye ni daga hanyoyin ruɗu; ka yi mini alheri ta wurin dokokinka.
30 I have taken the way of faith: I have kept your decisions before me.
Na zaɓi hanyar gaskiya; na sa zuciyata a kan dokokinka.
31 I have been true to your unchanging word; O Lord, do not put me to shame.
Na riƙe farillanka kankan, ya Ubangiji; kada ka sa in sha kunya.
32 I will go quickly in the way of your teaching, because you have given me a free heart.
Ina gudu a kan hanyar umarnanka, gama ka’yantar da zuciyata.
33 HE O Lord, let me see the way of your rules, and I will keep it to the end.
Ka koya mini Ya Ubangiji, don in bi ƙa’idodinka; sa’an nan zan kiyaye su har ƙarshe.
34 Give me wisdom, so that I may keep your law; going after it with all my heart.
Ka ba ni ganewa, zan kuwa kiyaye dokarka in kuma yi biyayya da ita da dukan zuciyata.
35 Make me go in the way of your teachings; for they are my delight.
Ka bi da ni a hanyar umarnanka, gama a can zan sami farin ciki.
36 Let my heart be turned to your unchanging word, and not to evil desire.
Ka juye zuciyata wajen farillanka ba wajen riba ta sonkai ba.
37 Let my eyes be turned away from what is false; give me life in your ways.
Ka juye idanuna daga abubuwa marasa amfani; ka kiyaye raina bisa ga maganarka.
38 Give effect to your word to your servant, in whose heart is the fear of you.
Ka cika alkawarinka ga bawanka, saboda a ji tsoronka.
39 Take away the shame which is my fear; for your decisions are good.
Ka kawar da shan kunyar da nake tsoro, gama dokokinka nagari ne.
40 See how great is my desire for your orders: give me life in your righteousness.
Ina marmarin farillanka ƙwarai! Ka kiyaye raina cikin adalcinka.
41 VAU Let your mercies come to me, O Lord, even your salvation, as you have said.
Bari ƙaunarka marar ƙarewa ta zo gare ni, ya Ubangiji, cetonka bisa ga alkawarinka;
42 So that I may have an answer for the man who would put me to shame; for I have faith in your word.
sa’an nan zan amsa wa masu cin mutuncina, gama na dogara ga maganarka.
43 Take not your true word quite out of my mouth; for I have put my hope in your decisions.
Kada ka ƙwace maganarka daga bakina, gama na sa zuciyata a dokokinka.
44 So that I may keep your law for ever and ever;
Kullayaumi zan yi biyayya da dokokinka, har abada abadin.
45 So that my way may be in a wide place: because my search has been for your orders.
Zan yi ta yawo a sake gama na nemi farillanka.
46 So that I may give knowledge of your unchanging word before kings, and not be put to shame.
Zan yi maganar farillanka a gaban sarakuna ba kuwa za a kunyata ni ba,
47 And so that I may take delight in your teachings, to which I have given my love.
gama ina farin ciki da umarnanka saboda ina ƙaunarsu.
48 And so that my hands may be stretched out to you; and I will give thought to your rules.
Na ɗaga hannuwana ga umarnanka, waɗanda nake ƙauna, ina kuma tunani a kan ƙa’idodinka.
49 ZAIN Keep in mind your word to your servant, for on it has my hope been fixed.
Tuna da maganarka ga bawanka, gama ka ba ni bege.
50 This is my comfort in my trouble; that your sayings have given me life.
Ta’aziyyata cikin wahalata ita ce alkawarinka yana kiyaye raina.
51 The men of pride have made great sport of me; but I have not been turned from your law.
Masu fariya suna yi mini ba’a ba tare da an hana su ba, amma ban rabu da dokar ba.
52 I have kept the memory of your decisions from times past, O Lord; and they have been my comfort.
Na tuna da dokokinka na tun dā, ya Ubangiji, na kuwa sami ta’aziyya a cikinsu.
53 I am burning with wrath, because of the sinners who have given up your law.
Fushi ya kama ni saboda mugaye, waɗanda suka keta dokokinka.
54 Your rules have been melodies to me, while I have been living in strange lands.
Ƙa’idodinka su ne kan waƙata a duk inda na sauka.
55 I have given thought to your name in the night, O Lord, and have kept your law.
Da dare na tuna da sunanka, ya Ubangiji, zan kuwa kiyaye dokarka.
56 This has been true of me, that I have kept your orders in my heart.
Wannan shi ne na saba yi, ina yin biyayya da farillanka.
57 CHETH The Lord is my heritage: I have said that I would be ruled by your words.
Kai ne rabona, ya Ubangiji; na yi alkawarin in kiyaye maganarka.
58 I have given my mind to do your pleasure with all my heart; have mercy on me, as you have said.
Na nemi fuskarka da dukan zuciyata; ka yi mini alheri bisa ga alkawarinka.
59 I gave thought to my steps, and my feet were turned into the way of your unchanging word.
Na lura da hanyoyina na kuma mayar da matakaina ga farillanka.
60 I was quick to do your orders, and let no time be wasted.
Zan gaggauta ba zan ɓata lokaci ba in yi biyayya da umarnanka.
61 The cords of evil-doers are round me; but I have kept in mind your law.
Ko da yake mugaye sun ɗaura ni da igiyoyi, ba zan manta da dokokinka ba.
62 In the middle of the night I will get up to give you praise, because of all your right decisions.
Da tsakar dare nakan tashi in gode maka saboda dokokinka masu adalci.
63 I keep company with all your worshippers, and those who have your orders in their memory.
Ni aboki ne ga duk mai tsoronka, ga duk wanda yake bin farillanka.
64 The earth, O Lord, is full of your mercy: give me knowledge of your rules.
Duniya ta cika da ƙaunarka, ya Ubangiji; ka koya mini ƙa’idodinka.
65 TETH You have done good to your servant, O Lord, in keeping with your word.
Ka yi wa bawanka alheri bisa ga maganarka, ya Ubangiji.
66 Give me knowledge and good sense; for I have put my faith in your teachings.
Ka koya mini sani da kuma hukunci mai kyau, gama na gaskata a umarnanka.
67 Before I was in trouble I went out of the way; but now I keep your word.
Kafin in sha wahala na kauce, amma yanzu ina biyayya da maganarka.
68 You are good, and your works are good; give me knowledge of your rules.
Kai nagari ne, kuma abin da kake yi yana da kyau; ka koya mini ƙa’idodinka.
69 The men of pride have said false things about me; but I will keep your orders in my heart.
Ko da yake masu fariya sun shafe ni da ƙarairayi, na kiyaye farillanka da dukan zuciyata.
70 Their hearts are shut up with fat; but my delight is in your law.
Zukatansu sun yi tauri da kuma marasa tausayi amma ina farin ciki a dokarka.
71 It is good for me to have been through trouble; so that I might come to the knowledge of your rules.
Ya yi kyau da na sha wahala don in koyi ƙa’idodinka.
72 The law of your mouth is better to me than thousands of gold and silver.
Doka daga bakinka ya fi mini daraja fiye da azurfa da zinariya guda dubu.
73 JOD Your hands have made me, and given me form: give me wisdom, so that I may have knowledge of your teaching.
Hannuwanka ne suka yi suka kuma siffanta ni; ka ba ni ganewa don in koyi umarnanka.
74 Your worshippers will see me and be glad; because my hope has been in your word.
Bari waɗanda suke tsoronka su yi farin ciki sa’ad da suke gan ni, gama na sa zuciyata a maganarka.
75 I have seen, O Lord, that your decisions are right, and that in unchanging faith you have sent trouble on me.
Ya Ubangiji na sani, cewa dokokinka masu adalci ne, kuma cikin aminci ka hore ni.
76 Let your mercy now be my comfort, as you have said to your servant.
Bari ƙaunarka marar ƙarewa tă yi mini ta’aziyya, bisa ga alkawarinka ga bawanka.
77 Let your gentle mercies come to me, so that I may have life; for your law is my delight.
Bari tausayinka yă zo mini don in rayu, gama dokarka ce farin cikina.
78 Let the men of pride be shamed; because they have falsely given decision against me; but I will give thought to your orders.
Bari masu girman kai su sha kunya saboda abubuwa marasa kyau da suke yi mini ba dalili; amma zan yi tunani a kan farillanka.
79 Let your worshippers be turned to me, and those who have knowledge of your words.
Bari waɗanda suke tsoronka su juya gare ni, waɗanda suka gane da farillanka.
80 Let all my heart be given to your orders, so that I may not be put to shame.
Bari zuciyata ta kasance marar abin zargi wajen ƙa’idodinka, don kada in sha kunya.
81 CAPH My soul is wasted with desire for your salvation: but I have hope in your word.
Raina ya tafke da marmari don cetonka, amma na sa zuciyata a maganarka.
82 My eyes are full of weariness with searching for your word, saying, When will you give me comfort?
Idanuna sun gaji, suna jiran alkawarinka; Na ce, “Yaushe za ka ta’azantar da ni?”
83 For I have become like a wine-skin black with smoke; but I still keep the memory of your rules.
Ko da yake ni kamar salkar ruwan inabi ne a cikin hayaƙi, ban manta da ƙa’idodinka ba.
84 How short is the life of your servant! when will you give your decision against those who are attacking me?
Har yaushe bawanka zai yi ta jira? Yaushe za ka hukunta masu tsananta mini?
85 The men of pride, who are turned away from your law, have put nets for me.
Masu girman kai sun haƙa mini rami, sun ƙetare dokarka.
86 All your teachings are certain; they go after me with evil design; give me your help.
Dukan umarnanka abin dogara ne; ka taimake ni, gama mutane suna tsananta mini ba dalili.
87 They had almost put an end to me on earth; but I did not give up your orders.
Sun kusa gama da ni a duniya, amma ban bar bin farillanka ba.
88 Give me life in your mercy; so that I may be ruled by the unchanging word of your mouth.
Ka kiyaye raina bisa ga ƙaunarka, zan kuwa yi biyayya da farillan bakinka.
89 LAMED For ever, O Lord, your word is fixed in heaven.
Maganarka, ya Ubangiji madawwamiya ce; tana nan daram a cikin sammai.
90 Your faith is unchanging from generation to generation: you have put the earth in its place, and it is not moved.
Amincinka yana cin gaba cikin dukan zamanai; ka kafa duniya ta kuma dawwama.
91 They are ruled this day by your decisions; for all things are your servants.
Dokokinka sun dawwama har yă zuwa yau, gama dukan abubuwa suna maka hidima.
92 If your law had not been my delight, my troubles would have put an end to me.
Da ba don dokarka ce farin cikina ba, da na hallaka a cikin azabana.
93 I will ever keep your orders in mind; for in them I have life.
Ba zan taɓa manta da farillanka ba, gama ta wurinsu ne ka kiyaye raina.
94 I am yours, O be my saviour; for my desire has been for your rules.
Ka cece ni, gama ni naka ne; na yi ƙoƙarin neman farillanka.
95 The sinners have been waiting for me to give me up to destruction; but I will give all my mind to your unchanging ward.
Mugaye suna jira su hallaka ni, amma zan yi ta tunani a kan farillanka.
96 I have seen that nothing on earth is complete; but your teaching is very wide.
Ga duk cikakke na ga kāsawa; amma umarnanka ba su da iyaka.
97 MEM O what love I have for your law! I give thought to it all the day.
Kash, ga yadda nake ƙaunar dokarka! Ina tunani a kanta dukan yini.
98 Your teaching has made me wiser than my haters: for it is mine for ever.
Umarnanka suna sa in zama mai hikima fiye da abokan gābana, gama kullum suna tare da ni.
99 I have more knowledge than all my teachers, because I give thought to your unchanging word.
Ina da ganewa sosai fiye da dukan malamaina, gama ina tunani a kan farillanka.
100 I have more wisdom than the old, because I have kept your orders.
Ina da ganewa fiye da dattawa, gama ina biyayya da farillanka.
101 I have kept back my feet from all evil ways, so that I might be true to your word.
Na kiyaye ƙafafuna daga kowace muguwar hanya domin in yi biyayya da maganarka.
102 My heart has not been turned away from your decisions; for you have been my teacher.
Ban rabu da dokokinka ba, gama kai da kanka ne ka koya mini.
103 How sweet are your sayings to my taste! truly, they are sweeter than honey in my mouth!
Ɗanɗanon maganarka akwai zaki, sun ma fi zuma zaki a bakina!
104 Through your orders I get wisdom; for this reason I am a hater of every false way.
Na sami ganewa daga farillanka; saboda haka ina ƙin kowace hanyar da ba daidai ba.
105 NUN Your word is a light for my feet, ever shining on my way.
Maganarka fitila ce ga ƙafafuna haske kuma a kan hanyata.
106 I have made an oath and kept it, to be guided by your upright decisions.
Na yi rantsuwa na kuma tabbatar da shi, cewa zan bi dokokinka masu adalci.
107 I am greatly troubled, O Lord, give me life in keeping with your word.
Na sha wahala sosai; ka kiyaye raina, ya Ubangiji, bisa ga maganarka.
108 Take, O Lord, the free offerings of my mouth, and give me knowledge of your decisions.
Ka karɓi yabon bakina da nake yi da yardar rai, ya Ubangiji, ka kuwa koya mini dokokinka.
109 My soul is ever in danger; but I still keep the memory of your law.
Ko da yake kullum ina riƙe da raina a hannuwana, ba zan manta da dokarka ba.
110 Sinners have put a net to take me; but I was true to your orders.
Mugaye sun kafa mini tarko, amma ban kauce daga farillanka ba.
111 I have taken your unchanging word as an eternal heritage; for it is the joy of my heart.
Farillanka su ne gādona har abada; su ne farin cikin zuciyata.
112 My heart is ever ready to keep your rules, even to the end.
Zuciyata ta shirya a kan kiyaye ƙa’idodinka har ƙarshe.
113 SAMECH I am a hater of men of doubting mind; but I am a lover of your law.
Na ƙi mutane masu baki biyu, amma ina ƙauna dokarka.
114 You are my secret place and my breastplate against danger; my hope is in your word.
Kai ne mafakata da garkuwata; na sa zuciyata a maganarka.
115 Go far from me, you evil-doers; so that I may keep the teachings of my God.
Ku rabu da ni, ku masu aikata mugunta, don in kiyaye umarnan Allahna!
116 Be my support as you have said, and give me life; let not my hope be turned to shame.
Ka raya ni bisa ga alkawarinka, zan kuwa rayu; kada ka bari a gwale sa zuciyata.
117 Let me not be moved, and I will be safe, and ever take delight in your rules.
Ka riƙe ni za a kuma cece ni; kullayaumi zan ɗauka ƙa’idodinka da muhimmanci.
118 You have overcome all those who are wandering from your rules; for all their thoughts are false.
Ka ki dukan waɗanda suka kauce daga ƙa’idodinka, gama yaudararsu banza ne.
119 All the sinners of the earth are like waste metal in your eyes; and for this cause I give my love to your unchanging word.
Dukan mugayen duniya ka zubar kamar datti; saboda haka nake ƙaunar farillanka.
120 My flesh is moved for fear of you; I give honour to your decisions.
Naman jikina na rawan jiki don tsoronka; na cika da tsoron dokokinka.
121 AIN I have done what is good and right: you will not give me into the hands of those who are working against me.
Na aikata abin da yake mai adalci da kuma daidai; kada ka ni a hannun masu danne ni.
122 Take your servant's interests into your keeping; let me not be crushed by the men of pride.
Ka tabbatar da lafiyar bawanka; kada ka bar masu girman kai su danne ni.
123 My eyes are wasted with desire for your salvation, and for the word of your righteousness.
Idanuna sun gaji, da jiran cetonka, da jiran alkawarinka mai adalci.
124 Be good to your servant in your mercy, and give me teaching in your rules.
Ka yi da bawanka bisa ga ƙaunarka ka kuma koya mini ƙa’idodinka.
125 I am your servant; give me wisdom, so that I may have knowledge of your unchanging word.
Ni bawanka ne, ka ba ni fahimi don in gane farillanka.
126 It is time, O Lord, for you to let your work be seen; for they have made your law without effect.
Lokaci ya yi da za ka yi wani abu, ya Ubangiji; ana karya dokarka.
127 For this reason I have greater love far your teachings than for gold, even for shining gold.
Saboda ina ƙaunar umarnanka fiye da zinariya, kai, fiye da zinariya zalla,
128 Because of it I keep straight in all things by your orders; and I am a hater of every false way.
saboda kuma ina lura da dukan farillanka da kyau, na ƙi kowace hanyar da ba daidai ba.
129 PE Your unchanging word is full of wonder; for this reason my soul keeps it.
Farillanka masu banmamaki ne; saboda haka nake yin biyayya da su.
130 The opening of your words gives light; it gives good sense to the simple.
Fassarar maganganunka sukan ba da haske; sukan ba da ganewa ga marar ilimi.
131 My mouth was open wide, waiting with great desire for your teachings.
Ina hakkin da bakina a buɗe, ina marmarin umarnanka.
132 Let your eyes be turned to me, and have mercy on me, as it is right for you to do to those who are lovers of your name.
Ka juye wurina ka kuma yi mini jinƙai, yadda kullum ka yi wa waɗanda suke ƙaunar sunanka.
133 Let my steps be guided by your word; and let not sin have control over me.
Ka bi da sawuna bisa ga maganarka; kada ka bar zunubi yă mallake ni.
134 Make me free from the cruel rule of man; then I will keep your orders.
Ka fanshe ni daga mutane masu danniya, don in yi biyayya da farillanka.
135 Let your servant see the shining of your face; give me knowledge of your rules.
Ka sa fuskarka ta haskaka a kan bawanka ka kuma koya mini ƙa’idodinka.
136 Rivers of water are flowing from my eyes, because men do not keep your law.
Hawaye suna malalowa daga idanuna kamar rafi, gama ba a biyayya da dokarka.
137 TZADE O Lord, great is your righteousness, and upright are your decisions.
Mai adalci ne kai, ya Ubangiji, dokokinka kuma daidai ne.
138 You have given your unchanging word in righteousness, and it is for ever.
Farillan da ka shimfiɗa masu adalci ne; su kuma abin dogara ne ƙwarai.
139 My passion has overcome me; because my haters are turned away from your words.
Kishina ya cinye ni ɗungum, gama abokan gābana sun yi biris da maganganunka.
140 Your word is of tested value; and it is dear to your servant.
An gwada alkawuranka sarai, bawanka kuwa yana ƙaunarsu.
141 I am small and of no account; but I keep your orders in mind.
Ko da yake ni ba kome ba ne an kuwa rena ni, ba na manta da farillanka.
142 Your righteousness is an unchanging righteousness, and your law is certain.
Adalcinka dawwammame ne dokar kuma gaskiya ce.
143 Pain and trouble have overcome me: but your teachings are my delight.
Wahala da damuwa suna a kaina, amma umarnanka su ne farin cikina.
144 The righteousness of your unchanging word is eternal; give me wisdom so that I may have life.
Farillanka daidai ne har abada; ka ba ni ganewa don in rayu.
145 KOPH I have made my prayer with all my heart; give answer to me, O Lord: I will keep your rules.
Na yi kira da dukan zuciyata; ka amsa mini, ya Ubangiji, zan kuwa yi biyayya da ƙa’idodinka.
146 My cry has gone up to you; take me out of trouble, and I will be guided by your unchanging word.
Na yi kira gare ka; ka cece ni zan kuwa kiyaye farillanka.
147 Before the sun is up, my cry for help comes to your ear; my hope is in your words.
Na tashi kafin fitowar rana na kuma yi kukan neman taimako; na sa zuciyata a maganarka.
148 In the night watches I am awake, so that I may give thought to your saying.
Ban rufe idanuna ba dukan dare, don in yi tunani a kan alkawuranka.
149 Let my voice come to you, in your mercy; O Lord, by your decisions give me life.
Ka ji muryata bisa ga ƙaunarka; ka kiyaye raina, ya Ubangiji, bisa ga dokokinka.
150 Those who have evil designs against me come near; they are far from your law.
Waɗanda suke ƙirƙiro mugayen dabaru suna nan kusa, amma suna nesa da dokarka.
151 You are near, O Lord; and all your teachings are true.
Duk da haka kana kusa, ya Ubangiji, kuma dukan umarnanka gaskiya ne.
152 I have long had knowledge that your unchanging word is for ever.
Tun tuni na koyi daga farillanka cewa ka kafa su su kasance har abada.
153 RESH O see my trouble, and be my saviour; for I keep your law in my mind,
Ka dubi wahalata ka cece ni, gama ban manta da dokarka ba.
154 Undertake my cause, and come to my help, give me life, as you have said.
Ka kāre manufata ka kuma fanshe ni, ka cece rai na kamar yadda ka alkawarta!
155 Salvation is far from evil-doers; for they have made no search for your rules.
Ceto yana nesa da mugaye, gama ba sa neman ƙa’idodinka.
156 Great is the number of your mercies, O Lord; give me life in keeping with your decisions.
Tausayinka da girma yake, ya Ubangiji; ka kiyaye raina bisa ga dokokinka.
157 Great is the number of those who are against me; but I have not been turned away from your unchanging word.
Maƙiya masu yawa ne suke tsananta mini, amma ban rabu da farillanka ba.
158 I saw with hate those who were untrue to you; for they did not keep your saying.
Na dubi marasa aminci da ƙyama, gama ba sa yin biyayya da maganarka.
159 See how great is my love for your orders: give me life, O Lord, in keeping with your mercy.
Dubi yadda nake ƙaunar farillanka; ka kiyaye raina, ya Ubangiji, bisa ga ƙaunarka.
160 Your word is true from the first; and your upright decision is unchanging for ever.
Dukan maganganunka gaskiya ne; dukan dokokinka masu adalci madawwami ne.
161 SHIN Rulers have been cruel to me without cause; but I have the fear of your word in my heart.
Masu mulki suna tsananta mini ba dalili, amma zuciyata na rawan jiki game da maganarka.
162 I am delighted by your saying, like a man who makes discovery of great wealth.
Ina farin ciki da alkawarinka kamar yadda wani kan sami ganima mai girma.
163 I am full of hate and disgust for false words; but I am a lover of your law.
Na ƙi ina kuma ƙyamar ƙarya amma ina ƙaunar dokarka.
164 Seven times a day do I give you praise, because of your upright decisions.
Sau bakwai a rana ina yabonka saboda dokokinka masu adalci.
165 Great peace have lovers of your law; they have no cause for falling.
Waɗanda suke ƙaunar dokarka suna da babban salama, kuma babu abin da zai sa su yi tuntuɓe.
166 Lord, my hope has been in your salvation; and I have kept your teachings.
Ina jiran cetonka, ya Ubangiji, ina kuma bin umarnanka.
167 My soul has kept your unchanging word; great is my love for it.
Ina biyayya da farillanka, gama ina ƙaunarsu ƙwarai.
168 I have been ruled by your orders; for all my ways are before you.
Ina biyayya da farillanka da kuma koyarwarka, gama dukan hanyoyina sanannu ne gare ka.
169 TAU Let my cry come before you, O Lord; give me wisdom in keeping with your word.
Bari kukata ta zo gare ka, ya Ubangiji; ka ba ni ganewa bisa ga maganarka.
170 Let my prayer come before you; take me out of trouble, as you have said.
Bari roƙona yă zo gabanka; ka cece ni bisa ga alkawarinka.
171 Let my lips be flowing with praise, because you have given me knowledge of your rules.
Bari leɓunana su cika da yabonka, gama ka koya mini ƙa’idodinka.
172 Let my tongue make songs in praise of your word; for all your teachings are righteousness.
Bari harshena yă rera game da maganarka, gama dukan umarnanka masu adalci ne.
173 Let your hand be near for my help; for I have given my heart to your orders.
Bari hannunka yă kasance a shirye don yă taimake ni, gama na zaɓi farillanka.
174 All my desire has been for your salvation, O Lord; and your law is my delight.
Ina marmarin cetonka, ya Ubangiji, dokarka kuwa ita ce farin cikina.
175 Give life to my soul so that it may give you praise; and let your decisions be my support.
Bari in rayu don in yabe ka, bari kuma dokokinka su raya ni.
176 I have gone out of the way like a wandering sheep; make search for your servant; for I keep your teachings ever in mind.
Na kauce kamar ɓatacciyar tunkiya. Ka nemi bawanka, gama ban manta da umarnanka ba.

< Psalms 119 >